< Mahukunta 17 >
1 To, wani mutum mai suna Mika daga ƙasar tudu ta Efraim
And there is a man of the hill-country of Ephraim, and his name [is] Micah,
2 ya ce wa mahaifiyarsa, “Shekel dubu ɗaya da ɗari ɗaya na azurfa da aka ɗauka daga gare ki wanda kuma ji kin furta la’ana a kai, azurfan yana wurina; ni ne na ɗauka.” Sa’an nan mahaifiyarsa ta ce, “Ubangiji yă albarkace ka ɗana!”
and he saith to his mother, 'The eleven hundred silverlings which have been taken of thine, and [of which] thou hast sworn, and also spoken in mine ears; lo, the silver [is] with me, I have taken it;' and his mother saith, 'Blessed [is] my son of Jehovah.'
3 Sa’ad da ya mayar da azurfa dubu ɗaya da ɗari ɗaya na shekel wa mahaifiyarsa, sai ta ce, “Na ba da azurfata ga Ubangiji don ɗana yă sassaƙa sura yă kuma yi zubin gunki. Zan mayar maka.”
And he giveth back the eleven hundred silverlings to his mother, and his mother saith, 'I had certainly sanctified the silver to Jehovah, from my hand, for my son, to make a graven image, and a molten image; and now, I give it back to thee.'
4 Saboda haka ya mayar da azurfan wa mahaifiyarsa, ita kuwa ta ɗauki azurfa ɗari biyu na shekel ta ba wa maƙeri, wanda ya mai da su sura da kuma gunki. Aka kuwa sa su a gidan Mika.
And he giveth back the money to his mother, and his mother taketh two hundred silverlings, and giveth them to a refiner, and he maketh them a graven image, and a molten image, and it is in the house of Micah.
5 To, wannan mutum Mika yana da ɗakin gumaka, ya yi efod da waɗansu gumaka, ya kuma naɗa ɗaya daga cikin’ya’yansa firist nasa.
As to the man Micah, he hath a house of gods, and he maketh an ephod, and teraphim, and consecrateth the hand of one of his sons, and he is to him for a priest;
6 A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa yana yin abin da ya ga dama.
in those days there is no king in Israel, each that which is right in his own eyes doth.
7 Wani saurayi Balawe daga Betlehem a Yahuda, wanda yake zama cikin zuriyar Yahuda,
And there is a young man of Beth-Lehem-Judah, of the family of Judah, and he [is] a Levite, and he [is] a sojourner there.
8 ya bar garin ya tafi neman inda zai zauna. A hanyarsa ya zo gidan Mika a ƙasar tudu ta Efraim.
And the man goeth out of the city, out of Beth-Lehem-Judah, to sojourn where he doth find, and cometh to the hill-country of Ephraim, unto the house of Micah, to work his way.
9 Mika ya ce masa, “Daga ina kake?” Ya ce, “Ni Balawe ne daga Betlehem a Yahuda, ina kuwa neman wurin zauna ne.”
And Micah saith to him, 'Whence comest thou?' and he saith unto him, 'A Levite [am] I, of Beth-Lehem-Judah, and I am going to sojourn where I do find.'
10 Sa’an nan Mika ya ce masa, “Ka zauna tare da ni ka zama mini mahaifi da firist, zan kuwa ba ka azurfa goma na shekel a shekara, tufafinka da kuma abincinka.” Sai Balawen ya tafi.
And Micah saith to him, 'Dwell with me, and be to me for a father and for a priest, and I give to thee ten silverlings for the days, and a suit of garments, and thy sustenance;' and the Levite goeth [in].
11 Saboda haka Balawen ya yarda ya zauna tare da shi, ɗan saurayin kuwa ya zama kamar ɗaya daga cikin’ya’yansa.
And the Levite is willing to dwell with the man, and the young man is to him as one of his sons.
12 Sa’an nan Mika ya naɗa Balawen, saurayin kuwa ya zama masa firist ya kuma zauna a gidansa.
And Micah consecrateth the hand of the Levite, and the young man is to him for a priest, and he is in the house of Micah,
13 Mika ya ce, “Yanzu na san cewa Ubangiji zai yi mini alheri, da yake Balawen nan ya zama firist nawa.”
and Micah saith, 'Now I have known that Jehovah doth good to me, for the Levite hath been to me for a priest.'