< Mahukunta 17 >

1 To, wani mutum mai suna Mika daga ƙasar tudu ta Efraim
And there was a man of the hill country of Ephraim, whose, name, was Micah.
2 ya ce wa mahaifiyarsa, “Shekel dubu ɗaya da ɗari ɗaya na azurfa da aka ɗauka daga gare ki wanda kuma ji kin furta la’ana a kai, azurfan yana wurina; ni ne na ɗauka.” Sa’an nan mahaifiyarsa ta ce, “Ubangiji yă albarkace ka ɗana!”
And he said unto his mother—The eleven hundred pieces of silver that were taken by thee, when, thou, didst utter a curse, and didst also say in my hearing, Lo! the silver, is with me! I took it. Then said his mother, Blessed, be my son by Yahweh.
3 Sa’ad da ya mayar da azurfa dubu ɗaya da ɗari ɗaya na shekel wa mahaifiyarsa, sai ta ce, “Na ba da azurfata ga Ubangiji don ɗana yă sassaƙa sura yă kuma yi zubin gunki. Zan mayar maka.”
And, when he had restored the eleven hundred shekels of silver to his mother, his mother said—I had, hallowed, the silver unto Yahweh out of mine own hand, for my son, to make a graved (molten) image, now, therefore, I will restore it unto thee.
4 Saboda haka ya mayar da azurfan wa mahaifiyarsa, ita kuwa ta ɗauki azurfa ɗari biyu na shekel ta ba wa maƙeri, wanda ya mai da su sura da kuma gunki. Aka kuwa sa su a gidan Mika.
But he restored the silver to his mother, —so his mother took two hundred pieces of silver, and gave it to the silversmith, who made thereof a graved (molten) image, and it was in the house of Micah.
5 To, wannan mutum Mika yana da ɗakin gumaka, ya yi efod da waɗansu gumaka, ya kuma naɗa ɗaya daga cikin’ya’yansa firist nasa.
Now, the man Micah, had a house of gods, —and he made an ephod, and teraphim, and installed one of his sons, who became his priest.
6 A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa yana yin abin da ya ga dama.
In those days, there was no king in Israel, —every man did, that which was right in his own eyes.
7 Wani saurayi Balawe daga Betlehem a Yahuda, wanda yake zama cikin zuriyar Yahuda,
And there was a young man out of Bethlehem-judah, of the family of Judah, —he, being a Levite, and, he, being a sojourner there.
8 ya bar garin ya tafi neman inda zai zauna. A hanyarsa ya zo gidan Mika a ƙasar tudu ta Efraim.
So the man took his journey out of the city, out of Bethlehem-judah, to sojourn, wheresoever he could find [a home], —and he came into the hill country of Ephraim, as far as the house of Micah, in pursuing his journey.
9 Mika ya ce masa, “Daga ina kake?” Ya ce, “Ni Balawe ne daga Betlehem a Yahuda, ina kuwa neman wurin zauna ne.”
And Micah said unto him, Whence comest thou? And he said unto him—A Levite, am I, from Bethlehem-judah, and, I, am taking my journey to sojourn, wheresoever I can find [a home].
10 Sa’an nan Mika ya ce masa, “Ka zauna tare da ni ka zama mini mahaifi da firist, zan kuwa ba ka azurfa goma na shekel a shekara, tufafinka da kuma abincinka.” Sai Balawen ya tafi.
And Micah said unto him—Dwell with me, and be to me a father and a priest, and, I, will give thee ten pieces of silver by the year, and a suit of apparel, and thy sustenance. So the Levite went.
11 Saboda haka Balawen ya yarda ya zauna tare da shi, ɗan saurayin kuwa ya zama kamar ɗaya daga cikin’ya’yansa.
And the Levite was content to dwell with the man, —and the young man became to him, as one of his sons.
12 Sa’an nan Mika ya naɗa Balawen, saurayin kuwa ya zama masa firist ya kuma zauna a gidansa.
And Micah installed the Levite, and the young man became his priest, —and remained in the house of Micah.
13 Mika ya ce, “Yanzu na san cewa Ubangiji zai yi mini alheri, da yake Balawen nan ya zama firist nawa.”
Then said Micah—Now, I know that Yahweh will do me good, —seeing I have a Levite as my priest.

< Mahukunta 17 >