< Mahukunta 17 >

1 To, wani mutum mai suna Mika daga ƙasar tudu ta Efraim
There was at that time a man of mount Ephraim whose name was Michas,
2 ya ce wa mahaifiyarsa, “Shekel dubu ɗaya da ɗari ɗaya na azurfa da aka ɗauka daga gare ki wanda kuma ji kin furta la’ana a kai, azurfan yana wurina; ni ne na ɗauka.” Sa’an nan mahaifiyarsa ta ce, “Ubangiji yă albarkace ka ɗana!”
Who said to his mother: The eleven hundred pieces of silver, which thou hadst put aside for thyself, and concerning which thou didst swear in my hearing, behold I have, and they are with me. And she said to him: Blessed be my son by the Lord.
3 Sa’ad da ya mayar da azurfa dubu ɗaya da ɗari ɗaya na shekel wa mahaifiyarsa, sai ta ce, “Na ba da azurfata ga Ubangiji don ɗana yă sassaƙa sura yă kuma yi zubin gunki. Zan mayar maka.”
So he restored them to his mother, who said to him: I have consecrated and vowed this silver to the Lord, that my son may receive it at my hand, and make a graven and a molten god, so now I deliver it to thee.
4 Saboda haka ya mayar da azurfan wa mahaifiyarsa, ita kuwa ta ɗauki azurfa ɗari biyu na shekel ta ba wa maƙeri, wanda ya mai da su sura da kuma gunki. Aka kuwa sa su a gidan Mika.
And he restored them to his mother: and she took two hundred pieces of silver and gave them to the silversmith, to make of them a graven and a molten god, which was in the house of Michas.
5 To, wannan mutum Mika yana da ɗakin gumaka, ya yi efod da waɗansu gumaka, ya kuma naɗa ɗaya daga cikin’ya’yansa firist nasa.
And he separated also therein a little temple for the god, and made an ephod, and theraphim, that is to say, a priestly garment, and idols: and he filled the hand of one of his sons, and he became his priest.
6 A kwanakin Isra’ila ba ta da sarki; kowa yana yin abin da ya ga dama.
In those days there was no king in Israel, but every one did that which seemed right to himself.
7 Wani saurayi Balawe daga Betlehem a Yahuda, wanda yake zama cikin zuriyar Yahuda,
There was also another young man of Bethlehem Juda, of the kindred thereof: and he was a Levite, and dwelt there.
8 ya bar garin ya tafi neman inda zai zauna. A hanyarsa ya zo gidan Mika a ƙasar tudu ta Efraim.
Now he went out from the city of Bethlehem, and desired to sojourn wheresoever he should find it convenient for him. And when he was come to mount Ephraim, as he was on his journey, and had turned aside a little into the house of Michas,
9 Mika ya ce masa, “Daga ina kake?” Ya ce, “Ni Balawe ne daga Betlehem a Yahuda, ina kuwa neman wurin zauna ne.”
He was asked by him whence he came. And he answered: I am a Levite of Bethlehem Juda, and I am going to dwell where I can, and where I shall find a place to my advantage.
10 Sa’an nan Mika ya ce masa, “Ka zauna tare da ni ka zama mini mahaifi da firist, zan kuwa ba ka azurfa goma na shekel a shekara, tufafinka da kuma abincinka.” Sai Balawen ya tafi.
And Michas said: Stay with me, and be unto me a father and a priest, and I will give thee every year ten pieces of silver, and a double suit of apparel, and thy victuals.
11 Saboda haka Balawen ya yarda ya zauna tare da shi, ɗan saurayin kuwa ya zama kamar ɗaya daga cikin’ya’yansa.
He was content, and abode with the man, and was unto him as one of his sons.
12 Sa’an nan Mika ya naɗa Balawen, saurayin kuwa ya zama masa firist ya kuma zauna a gidansa.
And Michas filled his hand, and had the young man with him, for his priest, saying:
13 Mika ya ce, “Yanzu na san cewa Ubangiji zai yi mini alheri, da yake Balawen nan ya zama firist nawa.”
Now I know God will do me good, since I have a priest of the race of the Levites.

< Mahukunta 17 >