< Mahukunta 16 >

1 Wata rana Samson ya tafi Gaza, inda ya ga wata karuwa. Ya shiga wurinta ya kwana.
Şimşon bir gün Gazze'ye gitti. Orada gördüğü bir fahişenin evine girdi.
2 Aka gaya wa mutanen Gaza, “Ai, Samson yana a nan!” Saboda haka suka zo suka kewaye wurin suka yi kwanto dukan dare a bakin ƙofar birni. A daren nan ba su motsa nan da can ba, suna cewa, “Gari yana wayewa za mu kashe shi.”
Gazzeliler'e, “Şimşon buraya geldi” diye haber verilince çevreyi kuşattılar. Bütün gece kentin kapısında pusuya yattılar. “Gün ağarınca onu öldürürüz” diyerek gece boyunca yerlerinden kımıldamadılar.
3 Amma Samson ya yi kwanciyarsa har tsakiyar dare. Sa’an nan ya tashi ya kama ƙofofin birnin, tare da madogarai biyunsu, ya tumɓuke, ya aza su a kafaɗarsa, ya kai su kan dutsen da yake a fuskantar Hebron.
Şimşon gece yarısına dek yattı. Gece yarısı kalktı, kent kapısının iki kanadıyla iki direğini tutup sürgüyle birlikte yerlerinden söktü. Hepsini omuzlayıp Hevron'un karşısındaki tepeye çıkardı.
4 Bayan ɗan lokaci, sai ya shiga ƙaunar wata mace, mai suna Delila a Kwarin Sorek.
Bir süre sonra Şimşon Sorek Vadisi'nde yaşayan Delila adında bir kadına aşık oldu.
5 Sai shugabannin Filistiyawa suka tafi wurinta suka ce, “Ki yi ƙoƙari ki ga ko za ki rarrashe shi yă nuna miki asirin ƙarfinsa da yadda za mu iya shan ƙarfinsa don mu ɗaura shi mu yi nasara a kansa. Kowannenmu zai ba ki shekel dubu ɗari ɗaya na azurfa.”
Filist beyleri kadına gelip, “Şimşon'un üstün gücünün kaynağı nedir, onu kandırıp öğrenmeye bak” dediler, “Böylece belki onu bağlar, etkisiz hale getirip yenebiliriz. Her birimiz sana bin yüzer parça gümüş vereceğiz.”
6 Saboda haka Delila ta ce wa Samson, “Ka faɗa miki asirin ƙarfinka da yadda za a ɗaura ka a yi nasara a kanka.”
Bunun üzerine Delila Şimşon'a, “Lütfen, söyle bana, bu üstün gücü nereden alıyorsun?” diye sordu, “Seni bağlayıp yenmek olası mı?”
7 Samson ya ce mata, “In wani ya ɗaura ni da sababbin igiyoyin da ba su bushe ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
Şimşon, “Beni kurumamış yedi taze sırımla bağlarlarsa sıradan bir adam gibi güçsüz olurum” dedi.
8 Sa’an nan shugabannin Filistiyawa suka kawo mata sababbin igiyoyi guda bakwai da ba su bushe ba, sai ta daure shi da su.
Bunun üzerine Filist beyleri Delila'ya kurumamış yedi taze sırım getirdiler. Delila bunlarla Şimşon'u bağladı.
9 Da mutane a ɓoye a cikin ɗaki tare da ita, sai ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Da jin haka sai ya tsintsinke igiyoyin kamar zaren da ya yi kusa da harshen wuta. Saboda haka asirin ƙarfinsa bai tonu ba.
Adamları bitişik odada pusuya yatmıştı. Delila, “Şimşon, Filistliler geldi!” dedi. Şimşon sırımları ateş değdiğinde dağılıveren kendir lifleri gibi koparıp attı. Gücünün sırrını vermemişti.
10 Sa’an nan Delila ta ce wa Samson, “Ka mai da ni wawiya; ka ruɗe ni. Yanzu, ka gaya mini yadda za a daure ka.”
Delila, “Beni kandırdın, bana yalan söyledin” dedi, “Lütfen söyle bana, seni neyle bağlamalı?”
11 Ya ce, “In wani ya ɗaura ni sosai da sababbin igiyoyin da ba a taɓa amfani da su ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
Şimşon, “Beni hiç kullanılmamış yeni urganla sımsıkı bağlarlarsa sıradan bir adam gibi güçsüz olurum” dedi.
12 Saboda haka Delila ta ɗauki sababbin igiyoyi ta ɗaura shi da su. Sa’an nan, tare da mutane a ɓoye a ɗakin, ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Amma sai ya tsintsinke su kamar zare.
Böylece Delila yeni urgan alıp Şimşon'u bağladı. Sonra, “Şimşon, Filistliler geldi!” dedi. Adamlar hâlâ bitişik odada pusu kurmuş bekliyorlardı. Şimşon urganları iplik koparır gibi koparıp kollarından sıyırdı.
13 Sa’an nan Delila ta ce, “Har yanzu, ka mai da shashasha, kana mai da ni wawiya kana kuma yin mini ƙarya. Ka gaya mini yadda za a daure ka mana.” Ya ce mata, “In kin yi kitson gashin kaina guda bakwai kika ɗaura su da zare kika buga su da akwasha, zan rasa ƙarfi in zama kamar kowa.” Saboda haka yayinda yake barci, sai Delila ta yi kitson gashin kansa guda bakwai ta ɗinka su da zare,
Delila ona, “Şimdiye kadar beni hep kandırdın, bana yalan söyledin” dedi, “Söyle bana, seni neyle bağlamalı?” Şimşon, “Başımdaki yedi örgüyü dokuma tezgahındaki kumaşla birlikte dokuyup kazıkla burarsan sıradan bir adam gibi güçsüz olurum” dedi.
14 ta kuma ɗaura su da akwasha. Ta sāke yin ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka.” Ya tashi daga barcinsa ya tumɓuke akwashan tare da zaren da aka ɗaura gashin kansa da su.
Şimşon uyurken Delila onun başındaki yedi örgüyü dokuma tezgahındaki kumaşla birlikte dokuyup kazıkla burdu. Sonra, “Şimşon, Filistliler geldi!” dedi. Şimşon uykusundan uyandı, saçını tezgah kazığından ve kumaştan çekip kurtardı.
15 Sa’an nan ta ce masa, “Yaya kake cewa kana sona alhali ba ka yarda da ni ba? Wannan shi ne sau na uku kana mai da ni wawiya kuma ba ka nuna mini asirin ƙarfinka ba.”
Delila, “Bana güvenmiyorsan nasıl olur da, ‘Seni seviyorum’ diyorsun?” dedi, “Üç kezdir beni kandırıyorsun, üstün gücünün nereden geldiğini söylemiyorsun.”
16 Da irin wannan fitina ta tsokane shi kwana da kwanaki har sai da ya gaji kamar zai mutu.
Bu sözlerle Şimşon'u sıkıştırıp günlerce başını ağrıttı. Sonunda Şimşon dayanamayıp
17 Saboda haka sai ya faɗa mata kome ya ce, “Ba a taɓa sa reza a kaina ba, domin ni Naziri ne keɓaɓɓe ga Allah tun haihuwa. In kuwa an aske kaina, ƙarfina zai rabu da ni, sai in zama kamar kowa.”
yüreğini kadına tümüyle açtı. “Başıma hiç ustura değmedi” dedi, “Çünkü ben ana rahmindeyken Tanrı'ya adanmışım. Tıraş olursam gücümü yitiririm. Sıradan bir adam gibi güçsüz olurum.”
18 Da Delila ta gane ya gaya mata kome yanzu, sai ta aika saƙo zuwa ga shugabannin Filistiyawa ta ce, “Ku ƙara zuwa sau ɗayan nan, ai, ya gaya mini kome.” Saboda haka shugabannin Filistiyawa suka dawo tare da azurfa a hannuwansu.
Delila Şimşon'un gerçeği söylediğini anlayınca haber gönderip Filist beylerini çağırttı. “Bir kez daha gelin” dedi, “Şimşon bana gerçeği söyledi.” Kadının yanına gelen Filist beyleri gümüşü de birlikte getirdiler.
19 Bayan ta sa shi ya yi barci a cinyarta, sai ta kira wani ya zo ya aske kitso guda bakwai nan a kansa, aka fara rinjayensa. Ƙarfinsa kuwa ya rabu da shi.
Delila Şimşon'u dizleri üzerinde uyuttuktan sonra adamlardan birini çağırtıp başındaki yedi örgüyü kestirdi. Sonra alay ederek onu dürtüklemeye başladı. Çünkü Şimşon gücünü yitirmişti.
20 Sa’an nan ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Sai ya farka daga barci yana tsammani cewa, “Zan fita kamar dā in miƙe jikina.” Amma bai san cewa Ubangiji ya rabu da shi ba.
Delila, “Şimşon, Filistliler geldi!” dedi. Şimşon uyandı ve, “Her zamanki gibi kalkıp silkinirim” diye düşündü. RAB'bin kendisinden ayrıldığını bilmiyordu.
21 Sa’an nan Filistiyawa suka fizge shi, suka ƙwaƙule idanunsa suka gangara da shi zuwa Gaza. Da suka daure shi da sarƙoƙin tagulla, sai aka sa shi yana niƙa a kurkuku.
Filistliler onu yakalayıp gözlerini oydular. Gazze'ye götürüp tunç zincirlerle bağladılar, cezaevinde değirmen taşına koştular.
22 Amma gashi kansa ya fara tohuwa kuma bayan an aske shi.
Bu arada Şimşon'un kesilen saçları uzamaya başladı.
23 To, sai Filistiyawa suka taru don su miƙa hadaya ga Dagon allahnsu su kuma yi biki cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu Samson a hannuwanmu.”
Filist beyleri ilahları Dagon'un onuruna çok sayıda kurban kesip eğlenmek için toplandılar. “İlahımız, düşmanımız Şimşon'u elimize teslim etti” dediler.
24 Sa’ad da mutane suka gan shi, sai suka yabi allahnsu, suna cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu a hannunmu, wanda ya lalace ƙasarmu ya kuma raɓanya kisan mutanenmu.”
Halk Şimşon'u görünce kendi ilahlarını övmeye başladı. “İlahımız ülkemizi yakıp yıkan, Birçoğumuzu öldüren Düşmanımızı elimize teslim etti” diyorlardı.
25 Yayinda suke cikin farin ciki, sai suka yi ihu, suka ce, “Fito mana da Samson yă yi mana wasa.” Saboda haka aka zo da Samson daga kurkuku, shi kuwa ya yi wasa a gabansu. Sa’ad da suka tsai da shi a tsakanin ginshiƙai,
İyice coşunca, “Şimşon'u getirin, bizi eğlendirsin” dediler. Şimşon'u cezaevinden getirip oynatmaya başladılar, sonra sütunların arasında durdurdular.
26 sai Samson ya ce wa bawan da ya riƙe hannunsa, “Ka kai ni inda zan taɓa ginshiƙan da suke ɗauke da wannan haikali, don in jingina a kai.”
Şimşon, elinden tutan gence, “Beni tapınağın damını taşıyan sütunların yanına götür de onlara yaslanayım” dedi.
27 To, haikalin ya cika da mutane maza da mata; dukan shugabannin Filistiyawa kuwa suna a can, a bisan rufin kuwa akwai mutum wajen dubu uku maza da mata suna kallon Samson yana wasa.
Tapınak erkeklerle, kadınlarla doluydu. Bütün Filist beyleri de oradaydı. Üç bin kadar kadın erkek Şimşon'un oynayışını damdan seyrediyordu.
28 Sa’an nan Samson ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ya Allah ka tuna da ni, ka ƙarfafa ni sau ɗaya nan kaɗai, ka bar ni da bugu ɗaya kawai in ɗauki fansa a kan Filistiyawa domin idanuna.”
Şimşon RAB'be yakarmaya başladı: “Ey Egemen RAB, lütfen beni anımsa. Ey Tanrı, bir kez daha beni güçlendir; Filistliler'den bir vuruşta iki gözümün öcünü alayım.”
29 Sa’an nan Samson ya kai hannuwansa ga ginshiƙan waɗanda haikalin yake a kai, ya jingina jikinsa, hannunsa dama yana a ɗaya, hannun hagu kuma na ɗayan,
Sonra tapınağın damını taşıyan iki ana sütunun ortasında durup sağ eliyle birini, sol eliyle ötekini kavradı.
30 Samson ya ce, “Bari in mutu tare da Filistiyawa!” Sa’an nan da dukan ƙarfinsa ya tura haikali ya fāɗa a kan shugabanni da dukan mutanen da suke ciki. Ta haka ya kashe mutane da yawa fiye da yayinda yake da rai.
“Filistliler'le birlikte öleyim” diyerek bütün gücüyle sütunlara yüklendi. Tapınak Filist beylerinin ve bütün içindekilerin üzerine çöktü. Böylece Şimşon ölürken, yaşamı boyunca öldürdüğünden daha çok insan öldürdü.
31 Sa’an nan’yan’uwansa da dukan dangin mahaifinsa suka gangaro don su ɗauke shi. Suka kawo shi suka binne tsakanin Zora da Eshtawol a kabarin Manowa mahaifinsa. Ya yi mulkin Isra’ila shekara ashirin.
Şimşon'un kardeşleriyle babası Manoah'ın bütün ailesi onun ölüsünü almaya geldiler. Şimşon'u götürüp babasının Sora ile Eştaol arasındaki mezarına gömdüler. Şimşon İsrail'i yirmi yıl süreyle yönetmişti.

< Mahukunta 16 >