< Mahukunta 16 >

1 Wata rana Samson ya tafi Gaza, inda ya ga wata karuwa. Ya shiga wurinta ya kwana.
Engang drog Samson til Gasa; der fikk han se en skjøge og gikk inn til henne.
2 Aka gaya wa mutanen Gaza, “Ai, Samson yana a nan!” Saboda haka suka zo suka kewaye wurin suka yi kwanto dukan dare a bakin ƙofar birni. A daren nan ba su motsa nan da can ba, suna cewa, “Gari yana wayewa za mu kashe shi.”
Da folkene i Gasa fikk høre at Samson var kommet dit, omringet de ham og lurte på ham hele natten ved byporten, men holdt sig ellers rolig hele natten og sa: Når det lysner mot dag, vil vi slå ham ihjel.
3 Amma Samson ya yi kwanciyarsa har tsakiyar dare. Sa’an nan ya tashi ya kama ƙofofin birnin, tare da madogarai biyunsu, ya tumɓuke, ya aza su a kafaɗarsa, ya kai su kan dutsen da yake a fuskantar Hebron.
Samson blev liggende til midnatt. Ved midnattstid stod han op; han grep fatt i byportens dører og i begge portstolpene og rykket dem op sammen med bommen, la dem på sine skuldrer og bar dem op på toppen av det fjell som ligger midt imot Hebron.
4 Bayan ɗan lokaci, sai ya shiga ƙaunar wata mace, mai suna Delila a Kwarin Sorek.
Siden fattet han kjærlighet til en kvinne i Sorek-dalen, som hette Dalila.
5 Sai shugabannin Filistiyawa suka tafi wurinta suka ce, “Ki yi ƙoƙari ki ga ko za ki rarrashe shi yă nuna miki asirin ƙarfinsa da yadda za mu iya shan ƙarfinsa don mu ɗaura shi mu yi nasara a kansa. Kowannenmu zai ba ki shekel dubu ɗari ɗaya na azurfa.”
Da kom filistrenes høvdinger op til henne og sa til henne: Lokk ham til å si dig hvori hans store styrke ligger, og hvorledes vi kan rå med ham og binde ham, så vi får bukt med ham! Så vil vi gi dig hver elleve hundre sekel sølv.
6 Saboda haka Delila ta ce wa Samson, “Ka faɗa miki asirin ƙarfinka da yadda za a ɗaura ka a yi nasara a kanka.”
Så sa Dalila til Samson: Kjære, la mig få vite hvori din store styrke ligger, og hvorledes du kan bindes, så en får bukt med dig!
7 Samson ya ce mata, “In wani ya ɗaura ni da sababbin igiyoyin da ba su bushe ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
Samson svarte: Dersom en binder mig med syv friske strenger som ikke er blitt tørre, så blir jeg svak og er som et annet menneske.
8 Sa’an nan shugabannin Filistiyawa suka kawo mata sababbin igiyoyi guda bakwai da ba su bushe ba, sai ta daure shi da su.
Da kom filistrenes høvdinger op til henne med syv friske strenger som ikke var blitt tørre; dem bandt hun ham med,
9 Da mutane a ɓoye a cikin ɗaki tare da ita, sai ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Da jin haka sai ya tsintsinke igiyoyin kamar zaren da ya yi kusa da harshen wuta. Saboda haka asirin ƙarfinsa bai tonu ba.
og i kammeret hadde hun folk sittende og lure. Så sa hun til ham: Filistrene er over dig, Samson! Da sønderrev han strengene som en tråd av stry brister når den kommer ilden for nær, og ingen fikk vite hvorledes det hadde sig med hans styrke.
10 Sa’an nan Delila ta ce wa Samson, “Ka mai da ni wawiya; ka ruɗe ni. Yanzu, ka gaya mini yadda za a daure ka.”
Da sa Dalila til Samson: Du har narret mig og løiet for mig! Kjære, la mig nu få vite hvorledes du kan bindes!
11 Ya ce, “In wani ya ɗaura ni sosai da sababbin igiyoyin da ba a taɓa amfani da su ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
Han svarte: Dersom en binder mig med nye rep som aldri har vært brukt til noget, så blir jeg svak og er som et annet menneske.
12 Saboda haka Delila ta ɗauki sababbin igiyoyi ta ɗaura shi da su. Sa’an nan, tare da mutane a ɓoye a ɗakin, ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Amma sai ya tsintsinke su kamar zare.
Da tok Dalila nye rep og bandt ham med dem og sa til ham: Filistrene er over dig, Samson! Og i kammeret satt der folk og lurte. Men han rev repene av sine armer som tråder.
13 Sa’an nan Delila ta ce, “Har yanzu, ka mai da shashasha, kana mai da ni wawiya kana kuma yin mini ƙarya. Ka gaya mini yadda za a daure ka mana.” Ya ce mata, “In kin yi kitson gashin kaina guda bakwai kika ɗaura su da zare kika buga su da akwasha, zan rasa ƙarfi in zama kamar kowa.” Saboda haka yayinda yake barci, sai Delila ta yi kitson gashin kansa guda bakwai ta ɗinka su da zare,
Da sa Dalila til Samson: Hittil har du narret mig og løiet for mig! La mig nu få vite hvorledes du kan bindes! Han svarte henne: Når du vever de syv fletter på mitt hode sammen med renningen i veven.
14 ta kuma ɗaura su da akwasha. Ta sāke yin ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka.” Ya tashi daga barcinsa ya tumɓuke akwashan tare da zaren da aka ɗaura gashin kansa da su.
Så slo hun dem fast med naglen og sa til ham: Filistrene er over dig, Samson! Og han våknet av sin søvn og rev ut både vevnaglen og renningen.
15 Sa’an nan ta ce masa, “Yaya kake cewa kana sona alhali ba ka yarda da ni ba? Wannan shi ne sau na uku kana mai da ni wawiya kuma ba ka nuna mini asirin ƙarfinka ba.”
Da sa hun til ham: Hvorledes kan du si at du elsker mig når du ikke har nogen tiltro til mig? Nu har du narret mig tre ganger og ikke sagt mig hvori din store styrke ligger.
16 Da irin wannan fitina ta tsokane shi kwana da kwanaki har sai da ya gaji kamar zai mutu.
Da hun nu hver dag plaget ham med sine ord og trengte sterkt inn på ham, blev han så lei av sig at han næsten kunde dø,
17 Saboda haka sai ya faɗa mata kome ya ce, “Ba a taɓa sa reza a kaina ba, domin ni Naziri ne keɓaɓɓe ga Allah tun haihuwa. In kuwa an aske kaina, ƙarfina zai rabu da ni, sai in zama kamar kowa.”
og så åpnet han hele sitt hjerte for henne og sa til henne: Det er ikke kommet rakekniv på mitt hode, for jeg har vært en Guds nasireer fra mors liv; dersom jeg blir raket, viker min styrke fra mig; jeg blir svak og er som alle andre mennesker.
18 Da Delila ta gane ya gaya mata kome yanzu, sai ta aika saƙo zuwa ga shugabannin Filistiyawa ta ce, “Ku ƙara zuwa sau ɗayan nan, ai, ya gaya mini kome.” Saboda haka shugabannin Filistiyawa suka dawo tare da azurfa a hannuwansu.
Da skjønte Dalila at han hadde åpnet hele sitt hjerte for henne; hun sendte bud efter filistrenes høvdinger og lot si: Kom nu op, for han har åpnet hele sitt hjerte for mig. Da kom filistrenes høvdinger op til henne og hadde pengene med sig.
19 Bayan ta sa shi ya yi barci a cinyarta, sai ta kira wani ya zo ya aske kitso guda bakwai nan a kansa, aka fara rinjayensa. Ƙarfinsa kuwa ya rabu da shi.
Så lot hun ham sove inn på sine knær og kalte på en mann og lot de syv fletter på hans hode rake av; og hun begynte å plage ham, og hans styrke vek fra ham.
20 Sa’an nan ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Sai ya farka daga barci yana tsammani cewa, “Zan fita kamar dā in miƙe jikina.” Amma bai san cewa Ubangiji ya rabu da shi ba.
Og hun sa: Filistrene er over dig, Samson! Da våknet han op av sin søvn og sa: Jeg skal nok gjøre mig fri denne gang som før og slite mig løs. Men han visste ikke at Herren var veket fra ham.
21 Sa’an nan Filistiyawa suka fizge shi, suka ƙwaƙule idanunsa suka gangara da shi zuwa Gaza. Da suka daure shi da sarƙoƙin tagulla, sai aka sa shi yana niƙa a kurkuku.
Da grep filistrene ham og stakk hans øine ut; og de førte ham ned til Gasa og bandt ham med to kobberlenker, og han malte korn i fangehuset.
22 Amma gashi kansa ya fara tohuwa kuma bayan an aske shi.
Men med det samme han var raket, begynte håret på hans hode å vokse.
23 To, sai Filistiyawa suka taru don su miƙa hadaya ga Dagon allahnsu su kuma yi biki cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu Samson a hannuwanmu.”
Så samledes filistrenes høvdinger for å bære frem et stort slaktoffer for sin gud Dagon og for å holde fest; for de sa: Vår gud har gitt Samson, vår fiende, i vår hånd.
24 Sa’ad da mutane suka gan shi, sai suka yabi allahnsu, suna cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu a hannunmu, wanda ya lalace ƙasarmu ya kuma raɓanya kisan mutanenmu.”
Og da folket fikk se ham, lovet de sin gud og sa: Vår gud har gitt vår fiende i vår hånd, han som herjet vårt land og slo så mange av oss ihjel.
25 Yayinda suke cikin farin ciki, sai suka yi ihu, suka ce, “Fito mana da Samson yă yi mana wasa.” Saboda haka aka zo da Samson daga kurkuku, shi kuwa ya yi wasa a gabansu. Sa’ad da suka tsai da shi a tsakanin ginshiƙai,
Mens de nu var glade og vel til mote, sa de: Hent Samson hit forat han kan leke for oss! Da hentet de Samson ut av fangehuset, og han lekte for dem, og de stilte ham mellem stolpene.
26 sai Samson ya ce wa bawan da ya riƙe hannunsa, “Ka kai ni inda zan taɓa ginshiƙan da suke ɗauke da wannan haikali, don in jingina a kai.”
Da sa Samson til den gutt som holdt ham ved hånden: Slipp mig, og la mig få ta i stolpene som huset hviler på, og støtte mig til dem!
27 To, haikalin ya cika da mutane maza da mata; dukan shugabannin Filistiyawa kuwa suna a can, a bisan rufin kuwa akwai mutum wajen dubu uku maza da mata suna kallon Samson yana wasa.
Men huset var fullt av menn og kvinner, alle filistrenes høvdinger var der, og på taket var det omkring tre tusen menn og kvinner, som så på at Samson lekte.
28 Sa’an nan Samson ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ya Allah ka tuna da ni, ka ƙarfafa ni sau ɗaya nan kaɗai, ka bar ni da bugu ɗaya kawai in ɗauki fansa a kan Filistiyawa domin idanuna.”
Da ropte Samson til Herren og sa: Herre, Herre! Kom mig i hu og styrk mig bare denne ene gang, min Gud, så jeg kan få hevne mig på filistrene for ett av mine to øine!
29 Sa’an nan Samson ya kai hannuwansa ga ginshiƙan waɗanda haikalin yake a kai, ya jingina jikinsa, hannunsa dama yana a ɗaya, hannun hagu kuma na ɗayan,
Så grep Samson om de to mellemste stolper, som huset hvilte på, og trykte sig inn til dem; den ene grep han om med sin høire, og den andre med sin venstre hånd.
30 Samson ya ce, “Bari in mutu tare da Filistiyawa!” Sa’an nan da dukan ƙarfinsa ya tura haikali ya fāɗa a kan shugabanni da dukan mutanen da suke ciki. Ta haka ya kashe mutane da yawa fiye da yayinda yake da rai.
Og Samson sa: La mig dø sammen med filistrene! Så bøide han sig fremover av all sin makt; da falt huset sammen over høvdingene og over alt folket som var der inne, og de som han drepte i sin død, var flere enn de han hadde drept i sitt liv.
31 Sa’an nan’yan’uwansa da dukan dangin mahaifinsa suka gangaro don su ɗauke shi. Suka kawo shi suka binne tsakanin Zora da Eshtawol a kabarin Manowa mahaifinsa. Ya yi mulkin Isra’ila shekara ashirin.
Men hans brødre og hele hans fars hus drog ned og tok ham og førte ham hjem og la ham i Manoahs, hans fars grav mellem Sora og Estaol. Han hadde da vært dommer i Israel i tyve år.

< Mahukunta 16 >