< Mahukunta 16 >
1 Wata rana Samson ya tafi Gaza, inda ya ga wata karuwa. Ya shiga wurinta ya kwana.
Un Simsons gāja uz Gazu un tur ieraudzīja vienu sievieti, kas bija mauka, un iegāja pie tās.
2 Aka gaya wa mutanen Gaza, “Ai, Samson yana a nan!” Saboda haka suka zo suka kewaye wurin suka yi kwanto dukan dare a bakin ƙofar birni. A daren nan ba su motsa nan da can ba, suna cewa, “Gari yana wayewa za mu kashe shi.”
Un Gaziešiem tapa sacīts: Simsons ir šurp atnācis. Un tie gāja apkārt un glūnēja uz viņu cauru nakti pilsētas vārtos un turējās klusu cauru nakti un sacīja: kad rīta gaisma aust, tad to nokausim. Bet Simsons gulēja līdz pusnaktij.
3 Amma Samson ya yi kwanciyarsa har tsakiyar dare. Sa’an nan ya tashi ya kama ƙofofin birnin, tare da madogarai biyunsu, ya tumɓuke, ya aza su a kafaɗarsa, ya kai su kan dutsen da yake a fuskantar Hebron.
Un nakts vidū viņš cēlās un sagrāba pilsētas vārtus ar tiem diviem stabiem un tos izcēla līdz ar aizšaujamo un tos lika uz saviem pleciem un tos uznesa uz tā kalna galu, kas ir pret Hebronu.
4 Bayan ɗan lokaci, sai ya shiga ƙaunar wata mace, mai suna Delila a Kwarin Sorek.
Un notikās pēc tam, ka viņš iemīļoja vienu sievieti pie Zoreka upes ar vārdu Delila.
5 Sai shugabannin Filistiyawa suka tafi wurinta suka ce, “Ki yi ƙoƙari ki ga ko za ki rarrashe shi yă nuna miki asirin ƙarfinsa da yadda za mu iya shan ƙarfinsa don mu ɗaura shi mu yi nasara a kansa. Kowannenmu zai ba ki shekel dubu ɗari ɗaya na azurfa.”
Tad Fīlistu lielkungi pie tās atnāca un uz to sacīja: pārrunā viņu un lūko, iekš kā viņa lielais spēks stāv, un ar ko viņu spējam pārvarēt, ka viņu saistām un savaldām, tad mēs tev dosim ikkatrs tūkstoš un simts sudraba (gabalus).
6 Saboda haka Delila ta ce wa Samson, “Ka faɗa miki asirin ƙarfinka da yadda za a ɗaura ka a yi nasara a kanka.”
Tad Delila sacīja uz Simsonu: saki man jel lūdzams, iekš kam stāv tavs lielais spēks, un ar ko tevi var saistīt un savaldīt?
7 Samson ya ce mata, “In wani ya ɗaura ni da sababbin igiyoyin da ba su bushe ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
Un Simsons uz to sacīja: ja mani saistītu ar septiņām zaļām lūku virvēm, kas vēl nav sakaltušas, tad es taptu nespēcīgs un būtu tā kā cits cilvēks.
8 Sa’an nan shugabannin Filistiyawa suka kawo mata sababbin igiyoyi guda bakwai da ba su bushe ba, sai ta daure shi da su.
Tad Fīlistu lielkungi pie tās atnesa septiņas zaļas lūku virves, kas nebija sakaltušas, un tā viņu ar tām saistīja.
9 Da mutane a ɓoye a cikin ɗaki tare da ita, sai ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Da jin haka sai ya tsintsinke igiyoyin kamar zaren da ya yi kusa da harshen wuta. Saboda haka asirin ƙarfinsa bai tonu ba.
Bet tie glūnētāji pie tās sēdēja kambarī. Un tā sacīja uz viņu: Fīlisti pār tevi, Simson! Tad viņš saraustīja tās virves tā kā pakulu pavedienu sarauta, kas pie uguns apsvilināts. Un viņa spēks netapa zināms.
10 Sa’an nan Delila ta ce wa Samson, “Ka mai da ni wawiya; ka ruɗe ni. Yanzu, ka gaya mini yadda za a daure ka.”
Tad Delila sacīja uz Simsonu: redzi, tu mani esi mānījis un man melus stāstījis. Nu tad saki man lūdzams, ar ko tevi var saistīt.
11 Ya ce, “In wani ya ɗaura ni sosai da sababbin igiyoyin da ba a taɓa amfani da su ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
Un viņš uz to sacīja: ja mani saistītu ar jaunām virvēm, ar ko nekāds darbs nav darīts, tad es taptu bezspēcīgs un būtu kā cits cilvēks.
12 Saboda haka Delila ta ɗauki sababbin igiyoyi ta ɗaura shi da su. Sa’an nan, tare da mutane a ɓoye a ɗakin, ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Amma sai ya tsintsinke su kamar zare.
Tad Delila ņēma jaunas virves un viņu ar tām saistīja un uz to sacīja: Fīlisti pār tevi, Simson! Un tie glūnētāji sēdēja kambarī. Bet viņš tās saraustīja no savām rokām tā kā pavedienu.
13 Sa’an nan Delila ta ce, “Har yanzu, ka mai da shashasha, kana mai da ni wawiya kana kuma yin mini ƙarya. Ka gaya mini yadda za a daure ka mana.” Ya ce mata, “In kin yi kitson gashin kaina guda bakwai kika ɗaura su da zare kika buga su da akwasha, zan rasa ƙarfi in zama kamar kowa.” Saboda haka yayinda yake barci, sai Delila ta yi kitson gashin kansa guda bakwai ta ɗinka su da zare,
Tad Delila sacīja uz Simsonu: līdz šim tu mani esi mānījis un man melus stāstījis; saki man jel, ar ko tevi var saistīt? Un viņš uz to sacīja: ja tu manas septiņas matu bizes aptītu ap riestavu.
14 ta kuma ɗaura su da akwasha. Ta sāke yin ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka.” Ya tashi daga barcinsa ya tumɓuke akwashan tare da zaren da aka ɗaura gashin kansa da su.
Un viņa tās piesita ar tapu un uz to sacīja: Fīlisti pār tevi, Simson! Un viņš uzmodās no sava miega un izrāva to aptīto tapu un to riestavu.
15 Sa’an nan ta ce masa, “Yaya kake cewa kana sona alhali ba ka yarda da ni ba? Wannan shi ne sau na uku kana mai da ni wawiya kuma ba ka nuna mini asirin ƙarfinka ba.”
Tad viņa uz to sacīja: kā tu vari sacīt: es tevi mīlēju, kad tomēr tava sirds nav ar mani? Tu nu trīs reiz mani esi mānījis un man neesi sacījis, iekš kam tavs lielais spēks stāv.
16 Da irin wannan fitina ta tsokane shi kwana da kwanaki har sai da ya gaji kamar zai mutu.
Un kad viņa to ikdienas ar savām runām māca un mocīja, tad viņa dvēsele apnika līdz pat nāvei.
17 Saboda haka sai ya faɗa mata kome ya ce, “Ba a taɓa sa reza a kaina ba, domin ni Naziri ne keɓaɓɓe ga Allah tun haihuwa. In kuwa an aske kaina, ƙarfina zai rabu da ni, sai in zama kamar kowa.”
Un tas viņai darīja zināmu visu savu sirdi un uz viņu sacīja: uz manu galvu dzenamais nazis nav nācis, jo es esmu Dievam svētīts no mātes miesām; kad (mani mati) taptu nodzīti, tad mans spēks no manis atstātos, un es taptu bezspēcīgs un būtu tā kā visi citi cilvēki.
18 Da Delila ta gane ya gaya mata kome yanzu, sai ta aika saƙo zuwa ga shugabannin Filistiyawa ta ce, “Ku ƙara zuwa sau ɗayan nan, ai, ya gaya mini kome.” Saboda haka shugabannin Filistiyawa suka dawo tare da azurfa a hannuwansu.
Kad nu Delila redzēja, ka tas viņai visu savu sirdi bija izsacījis, tad viņa nosūtīja un sasauca Fīlistu lielkungus sacīdama: atnāciet vēl šo reiz', jo viņš man izsacījis visu savu sirdi. Tad Fīlistu lielkungi pie viņas atnāca un atnesa to sudrabu savā rokā.
19 Bayan ta sa shi ya yi barci a cinyarta, sai ta kira wani ya zo ya aske kitso guda bakwai nan a kansa, aka fara rinjayensa. Ƙarfinsa kuwa ya rabu da shi.
Bet viņa tam lika aizmigt savā klēpī un aicināja vīru un lika nodzīt viņa galvas septiņas matu bizes un sāka viņu pārvarēt, un viņa spēks no viņa atstājās.
20 Sa’an nan ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Sai ya farka daga barci yana tsammani cewa, “Zan fita kamar dā in miƙe jikina.” Amma bai san cewa Ubangiji ya rabu da shi ba.
Un viņa sacīja: Fīlisti pār tevi, Simson! Un viņš uzmodās no sava miega un domāja: es iziešu šo reizi kā citām reizēm un izraušos; jo viņš nezināja, ka Tas Kungs no viņa bija atstājies.
21 Sa’an nan Filistiyawa suka fizge shi, suka ƙwaƙule idanunsa suka gangara da shi zuwa Gaza. Da suka daure shi da sarƙoƙin tagulla, sai aka sa shi yana niƙa a kurkuku.
Tad Fīlisti viņu sagrāba un izdūra viņam acis un to noveda uz Gazu un to sēja ar divām vara ķēdēm, un viņam tur cietumā bija jāmaļ.
22 Amma gashi kansa ya fara tohuwa kuma bayan an aske shi.
Bet viņa galvas mati sāka atkal ataugt, kad tie bija nodzīti.
23 To, sai Filistiyawa suka taru don su miƙa hadaya ga Dagon allahnsu su kuma yi biki cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu Samson a hannuwanmu.”
Tad Fīlistu lielkungi sapulcējās, savam dievam Dagonam lielu upuri upurēt un līksmoties, un tie sacīja: mūsu dievs mūsu ienaidnieku Simsonu nodevis mūsu rokā.
24 Sa’ad da mutane suka gan shi, sai suka yabi allahnsu, suna cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu a hannunmu, wanda ya lalace ƙasarmu ya kuma raɓanya kisan mutanenmu.”
Un kad tie ļaudis viņu redzēja, tad tie teica savu dievu, jo tie sacīja: mūsu dievs mūsu ienaidnieku mums ir rokā devis, kas mūsu zemi ir postījis un lielu pulku no mums nokāvis.
25 Yayinda suke cikin farin ciki, sai suka yi ihu, suka ce, “Fito mana da Samson yă yi mana wasa.” Saboda haka aka zo da Samson daga kurkuku, shi kuwa ya yi wasa a gabansu. Sa’ad da suka tsai da shi a tsakanin ginshiƙai,
Un kad viņu sirds līksmojās, tad tie sacīja: sauciet Simsonu, lai tas mūs pajautrina. Tad tie sauca Simsonu no cietuma nama, un viņš tiem bija par pajautrināšanu, un tie viņam lika stāvēt starp diviem stabiem.
26 sai Samson ya ce wa bawan da ya riƙe hannunsa, “Ka kai ni inda zan taɓa ginshiƙan da suke ɗauke da wannan haikali, don in jingina a kai.”
Tad Simsons sacīja uz to puisi, kas viņu pie rokas vadīja: laid mani vaļā un ļauj man tos stabus taustīt, uz kā tas nams stiprināts, un pie tiem atslieties.
27 To, haikalin ya cika da mutane maza da mata; dukan shugabannin Filistiyawa kuwa suna a can, a bisan rufin kuwa akwai mutum wajen dubu uku maza da mata suna kallon Samson yana wasa.
Bet tas nams bija pilns ar vīriem un sievām. Un tur bija visi Fīlistu lielkungi, un uz tā jumta bija kādi trīs tūkstoši vīri un sievas, kas lūkojās uz Simsona jautrināšanu.
28 Sa’an nan Samson ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ya Allah ka tuna da ni, ka ƙarfafa ni sau ɗaya nan kaɗai, ka bar ni da bugu ɗaya kawai in ɗauki fansa a kan Filistiyawa domin idanuna.”
Tad Simsons piesauca To Kungu un sacīja: Kungs, Dievs, piemini mani un stiprini lūdzams mani tikai šo reiz', ak Dievs, ka es par savām abējām acīm vienreiz varu atriebties.
29 Sa’an nan Samson ya kai hannuwansa ga ginshiƙan waɗanda haikalin yake a kai, ya jingina jikinsa, hannunsa dama yana a ɗaya, hannun hagu kuma na ɗayan,
Un Simsons apkampa tos divus vidējos stabus, uz kā tas nams bija stiprināts un uz kā tas turējās, vienu ar savu labo roku un vienu ar savu kreiso roku, un Simsons sacīja:
30 Samson ya ce, “Bari in mutu tare da Filistiyawa!” Sa’an nan da dukan ƙarfinsa ya tura haikali ya fāɗa a kan shugabanni da dukan mutanen da suke ciki. Ta haka ya kashe mutane da yawa fiye da yayinda yake da rai.
Lai mana dvēsele mirst ar tiem Fīlistiem! Un viņš locījās ar varu, - tad tas nams krita uz tiem lielkungiem un uz visiem ļaudīm, kas iekšā bija un vairāk bija miroņu, ko viņš mirdams nokāva, nekā ko viņš bija nokāvis, dzīvs būdams.
31 Sa’an nan’yan’uwansa da dukan dangin mahaifinsa suka gangaro don su ɗauke shi. Suka kawo shi suka binne tsakanin Zora da Eshtawol a kabarin Manowa mahaifinsa. Ya yi mulkin Isra’ila shekara ashirin.
Tad viņa brāļi un viss viņa tēva nams nonāca un to ņēma un to aiznesa un apraka starp Careū un Estaoli, Manoūs, viņa tēva, kapā. Un viņš Israēli bija tiesājis divdesmit gadus.