< Mahukunta 16 >

1 Wata rana Samson ya tafi Gaza, inda ya ga wata karuwa. Ya shiga wurinta ya kwana.
And Samson went to Gaza, and saw there a harlot, and went in unto her.
2 Aka gaya wa mutanen Gaza, “Ai, Samson yana a nan!” Saboda haka suka zo suka kewaye wurin suka yi kwanto dukan dare a bakin ƙofar birni. A daren nan ba su motsa nan da can ba, suna cewa, “Gari yana wayewa za mu kashe shi.”
And it was told the Gazites, saying: 'Samson is come hither.' And they compassed him in, and lay in wait for him all night in the gate of the city, and were quiet all the night, saying: 'Let be till morning light, then we will kill him.'
3 Amma Samson ya yi kwanciyarsa har tsakiyar dare. Sa’an nan ya tashi ya kama ƙofofin birnin, tare da madogarai biyunsu, ya tumɓuke, ya aza su a kafaɗarsa, ya kai su kan dutsen da yake a fuskantar Hebron.
And Samson lay till midnight, and arose at midnight, and laid hold of the doors of the gate of the city, and the two posts, and plucked them up, bar and all, and put them upon his shoulders, and carried them up to the top of the mountain that is before Hebron.
4 Bayan ɗan lokaci, sai ya shiga ƙaunar wata mace, mai suna Delila a Kwarin Sorek.
And it came to pass afterward, that he loved a woman in the valley of Sorek, whose name was Delilah.
5 Sai shugabannin Filistiyawa suka tafi wurinta suka ce, “Ki yi ƙoƙari ki ga ko za ki rarrashe shi yă nuna miki asirin ƙarfinsa da yadda za mu iya shan ƙarfinsa don mu ɗaura shi mu yi nasara a kansa. Kowannenmu zai ba ki shekel dubu ɗari ɗaya na azurfa.”
And the lords of the Philistines came up unto her, and said unto her: 'Entice him, and see wherein his great strength lieth, and by what means we may prevail against him, that we may bind him to afflict him; and we will give thee every one of us eleven hundred pieces of silver.'
6 Saboda haka Delila ta ce wa Samson, “Ka faɗa miki asirin ƙarfinka da yadda za a ɗaura ka a yi nasara a kanka.”
And Delilah said to Samson: 'Tell me, I pray thee, wherein thy great strength lieth, and wherewith thou mightest be bound to afflict thee.'
7 Samson ya ce mata, “In wani ya ɗaura ni da sababbin igiyoyin da ba su bushe ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
And Samson said unto her: 'If they bind me with seven fresh bowstrings that were never dried, then shall I become weak, and be as any other man.'
8 Sa’an nan shugabannin Filistiyawa suka kawo mata sababbin igiyoyi guda bakwai da ba su bushe ba, sai ta daure shi da su.
Then the lords of the Philistines brought up to her seven fresh bowstrings which had not been dried, and she bound him with them.
9 Da mutane a ɓoye a cikin ɗaki tare da ita, sai ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Da jin haka sai ya tsintsinke igiyoyin kamar zaren da ya yi kusa da harshen wuta. Saboda haka asirin ƙarfinsa bai tonu ba.
Now she had liers-in-wait abiding in the inner chamber. And she said unto him: 'The Philistines are upon thee, Samson.' And he broke the bowstrings as a string of tow is broken when it toucheth the fire. So his strength was not known.
10 Sa’an nan Delila ta ce wa Samson, “Ka mai da ni wawiya; ka ruɗe ni. Yanzu, ka gaya mini yadda za a daure ka.”
And Delilah said unto Samson: 'Behold, thou hast mocked me, and told me lies; now tell me, I pray thee, wherewith thou mightest be bound.'
11 Ya ce, “In wani ya ɗaura ni sosai da sababbin igiyoyin da ba a taɓa amfani da su ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
And he said unto her: 'If they only bind me with new ropes wherewith no work hath been done, then shall I become weak, and be as any other man.'
12 Saboda haka Delila ta ɗauki sababbin igiyoyi ta ɗaura shi da su. Sa’an nan, tare da mutane a ɓoye a ɗakin, ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Amma sai ya tsintsinke su kamar zare.
So Delilah took new ropes, and bound him therewith, and said unto him: 'The Philistines are upon thee, Samson.' And the liers-in-wait were abiding in the inner chamber. And he broke them from off his arms like a thread.
13 Sa’an nan Delila ta ce, “Har yanzu, ka mai da shashasha, kana mai da ni wawiya kana kuma yin mini ƙarya. Ka gaya mini yadda za a daure ka mana.” Ya ce mata, “In kin yi kitson gashin kaina guda bakwai kika ɗaura su da zare kika buga su da akwasha, zan rasa ƙarfi in zama kamar kowa.” Saboda haka yayinda yake barci, sai Delila ta yi kitson gashin kansa guda bakwai ta ɗinka su da zare,
And Delilah said unto Samson: 'Hitherto thou hast mocked me, and told me lies; tell me wherewith thou mightest be bound.' And he said unto her: 'If thou weavest the seven locks of my head with the web.'
14 ta kuma ɗaura su da akwasha. Ta sāke yin ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka.” Ya tashi daga barcinsa ya tumɓuke akwashan tare da zaren da aka ɗaura gashin kansa da su.
And she fastened it with the pin, and said unto him: 'The Philistines are upon thee, Samson.' And he awoke out of his sleep, and plucked away the pin of the beam, and the web.
15 Sa’an nan ta ce masa, “Yaya kake cewa kana sona alhali ba ka yarda da ni ba? Wannan shi ne sau na uku kana mai da ni wawiya kuma ba ka nuna mini asirin ƙarfinka ba.”
And she said unto him: 'How canst thou say: I love thee, when thy heart is not with me? thou hast mocked me these three times, and hast not told me wherein thy great strength lieth.'
16 Da irin wannan fitina ta tsokane shi kwana da kwanaki har sai da ya gaji kamar zai mutu.
And it came to pass, when she pressed him daily with her words, and urged him, that his soul was vexed unto death.
17 Saboda haka sai ya faɗa mata kome ya ce, “Ba a taɓa sa reza a kaina ba, domin ni Naziri ne keɓaɓɓe ga Allah tun haihuwa. In kuwa an aske kaina, ƙarfina zai rabu da ni, sai in zama kamar kowa.”
And he told her all his heart, and said unto her: 'There hath not come a razor upon my head; for I have been a Nazirite unto God from my mother's womb; if I be shaven, then my strength will go from me, and I shall become weak, and be like any other man.'
18 Da Delila ta gane ya gaya mata kome yanzu, sai ta aika saƙo zuwa ga shugabannin Filistiyawa ta ce, “Ku ƙara zuwa sau ɗayan nan, ai, ya gaya mini kome.” Saboda haka shugabannin Filistiyawa suka dawo tare da azurfa a hannuwansu.
And when Delilah saw that he had told her all his heart, she sent and called for the lords of the Philistines, saying: 'Come up this once, for he hath told me all his heart.' Then the lords of the Philistines came up unto her, and brought the money in their hand.
19 Bayan ta sa shi ya yi barci a cinyarta, sai ta kira wani ya zo ya aske kitso guda bakwai nan a kansa, aka fara rinjayensa. Ƙarfinsa kuwa ya rabu da shi.
And she made him sleep upon her knees; and she called for a man, and had the seven locks of his head shaven off; and she began to afflict him, and his strength went from him.
20 Sa’an nan ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Sai ya farka daga barci yana tsammani cewa, “Zan fita kamar dā in miƙe jikina.” Amma bai san cewa Ubangiji ya rabu da shi ba.
And she said: 'The Philistines are upon thee, Samson.' And he awoke out of his sleep, and said: 'I will go out as at other times, and shake myself.' But he knew not that the LORD was departed from him.
21 Sa’an nan Filistiyawa suka fizge shi, suka ƙwaƙule idanunsa suka gangara da shi zuwa Gaza. Da suka daure shi da sarƙoƙin tagulla, sai aka sa shi yana niƙa a kurkuku.
And the Philistines laid hold on him, and put out his eyes; and they brought him down to Gaza, and bound him with fetters of brass; and he did grind in the prison-house.
22 Amma gashi kansa ya fara tohuwa kuma bayan an aske shi.
Howbeit the hair of his head began to grow again after he was shaven.
23 To, sai Filistiyawa suka taru don su miƙa hadaya ga Dagon allahnsu su kuma yi biki cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu Samson a hannuwanmu.”
And the lords of the Philistines gathered them together to offer a great sacrifice unto Dagon their god, and to rejoice; for they said: 'Our god hath delivered Samson our enemy into our hand.'
24 Sa’ad da mutane suka gan shi, sai suka yabi allahnsu, suna cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu a hannunmu, wanda ya lalace ƙasarmu ya kuma raɓanya kisan mutanenmu.”
And when the people saw him, they praised their god; for they said: 'Our god hath delivered into our hand our enemy, and the destroyer of our country, who hath slain many of us.'
25 Yayinda suke cikin farin ciki, sai suka yi ihu, suka ce, “Fito mana da Samson yă yi mana wasa.” Saboda haka aka zo da Samson daga kurkuku, shi kuwa ya yi wasa a gabansu. Sa’ad da suka tsai da shi a tsakanin ginshiƙai,
And it came to pass, when their hearts were merry, that they said: 'Call for Samson, that he may make us sport.' And they called for Samson out of the prison-house; and he made sport before them; and they set him between the pillars.
26 sai Samson ya ce wa bawan da ya riƙe hannunsa, “Ka kai ni inda zan taɓa ginshiƙan da suke ɗauke da wannan haikali, don in jingina a kai.”
And Samson said unto the lad that held him by the hand: 'Suffer me that I may feel the pillars whereupon the house resteth, that I may lean upon them.'
27 To, haikalin ya cika da mutane maza da mata; dukan shugabannin Filistiyawa kuwa suna a can, a bisan rufin kuwa akwai mutum wajen dubu uku maza da mata suna kallon Samson yana wasa.
Now the house was full of men and women; and all the lords of the Philistines were there; and there were upon the roof about three thousand men and women, that beheld while Samson made sport.
28 Sa’an nan Samson ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ya Allah ka tuna da ni, ka ƙarfafa ni sau ɗaya nan kaɗai, ka bar ni da bugu ɗaya kawai in ɗauki fansa a kan Filistiyawa domin idanuna.”
And Samson called unto the LORD, and said: 'O Lord GOD, remember me, I pray Thee, and strengthen me, I pray Thee, only this once, O God, that I may be this once avenged of the Philistines for my two eyes.'
29 Sa’an nan Samson ya kai hannuwansa ga ginshiƙan waɗanda haikalin yake a kai, ya jingina jikinsa, hannunsa dama yana a ɗaya, hannun hagu kuma na ɗayan,
And Samson took fast hold of the two middle pillars upon which the house rested, and leaned upon them, the one with his right hand, and the other with his left.
30 Samson ya ce, “Bari in mutu tare da Filistiyawa!” Sa’an nan da dukan ƙarfinsa ya tura haikali ya fāɗa a kan shugabanni da dukan mutanen da suke ciki. Ta haka ya kashe mutane da yawa fiye da yayinda yake da rai.
And Samson said: 'Let me die with the Philistines.' And he bent with all his might; and the house fell upon the lords, and upon all the people that were therein. So the dead that he slew at his death were more than they that he slew in his life.
31 Sa’an nan’yan’uwansa da dukan dangin mahaifinsa suka gangaro don su ɗauke shi. Suka kawo shi suka binne tsakanin Zora da Eshtawol a kabarin Manowa mahaifinsa. Ya yi mulkin Isra’ila shekara ashirin.
Then his brethren and all the house of his father came down, and took him, and brought him up, and buried him between Zorah and Eshtaol in the burying-place of Manoah his father. And he judged Israel twenty years.

< Mahukunta 16 >