< Mahukunta 16 >

1 Wata rana Samson ya tafi Gaza, inda ya ga wata karuwa. Ya shiga wurinta ya kwana.
Now Samson went to Gaza, and there he saw a loose woman and went in to her.
2 Aka gaya wa mutanen Gaza, “Ai, Samson yana a nan!” Saboda haka suka zo suka kewaye wurin suka yi kwanto dukan dare a bakin ƙofar birni. A daren nan ba su motsa nan da can ba, suna cewa, “Gari yana wayewa za mu kashe shi.”
And it was said to the Gazites, Samson is here. So they went round, watching for him all day at the doorway of the town, but at night they kept quiet, saying, When daylight comes we will put him to death.
3 Amma Samson ya yi kwanciyarsa har tsakiyar dare. Sa’an nan ya tashi ya kama ƙofofin birnin, tare da madogarai biyunsu, ya tumɓuke, ya aza su a kafaɗarsa, ya kai su kan dutsen da yake a fuskantar Hebron.
And Samson was there till the middle of the night; then he got up, and took a grip on the doors of the town, pulling them up, together with their two supports and their locks, and put them on his back and took them up to the top of the hill in front of Hebron.
4 Bayan ɗan lokaci, sai ya shiga ƙaunar wata mace, mai suna Delila a Kwarin Sorek.
Now after this, he was in love with a woman in the valley of Sorek, named Delilah.
5 Sai shugabannin Filistiyawa suka tafi wurinta suka ce, “Ki yi ƙoƙari ki ga ko za ki rarrashe shi yă nuna miki asirin ƙarfinsa da yadda za mu iya shan ƙarfinsa don mu ɗaura shi mu yi nasara a kansa. Kowannenmu zai ba ki shekel dubu ɗari ɗaya na azurfa.”
And the chiefs of the Philistines came up to her, and said to her, Make use of your power over him and see what is the secret of his great strength, and how we may get the better of him, and put bands on him, so that we may make him feeble; and every one of us will give you eleven hundred shekels of silver.
6 Saboda haka Delila ta ce wa Samson, “Ka faɗa miki asirin ƙarfinka da yadda za a ɗaura ka a yi nasara a kanka.”
So Delilah said to Samson, Make clear to me now what is the secret of your great strength, and how you may be put in bands and made feeble.
7 Samson ya ce mata, “In wani ya ɗaura ni da sababbin igiyoyin da ba su bushe ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
And Samson said to her, If seven new bow-cords which have never been made dry are knotted round me, I will become feeble and will be like any other man.
8 Sa’an nan shugabannin Filistiyawa suka kawo mata sababbin igiyoyi guda bakwai da ba su bushe ba, sai ta daure shi da su.
So the chiefs of the Philistines gave her seven new bow-cords which had never been made dry, and she had them tightly knotted round him.
9 Da mutane a ɓoye a cikin ɗaki tare da ita, sai ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Da jin haka sai ya tsintsinke igiyoyin kamar zaren da ya yi kusa da harshen wuta. Saboda haka asirin ƙarfinsa bai tonu ba.
Now she had men waiting secretly in the inner room; and she said to him, The Philistines are on you, Samson. And the cords were broken by him as a twist of thread is broken when touched by a flame. So the secret of his strength did not come to light.
10 Sa’an nan Delila ta ce wa Samson, “Ka mai da ni wawiya; ka ruɗe ni. Yanzu, ka gaya mini yadda za a daure ka.”
Then Delilah said to Samson, See, you have been making sport of me with false words; now, say truly how may you be put in bands?
11 Ya ce, “In wani ya ɗaura ni sosai da sababbin igiyoyin da ba a taɓa amfani da su ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
And he said to her, If they only put round me new thick cords which have never been used, then I will become feeble and will be like any other man.
12 Saboda haka Delila ta ɗauki sababbin igiyoyi ta ɗaura shi da su. Sa’an nan, tare da mutane a ɓoye a ɗakin, ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Amma sai ya tsintsinke su kamar zare.
So Delilah took new thick cords, knotting them tightly round him, and said to him, The Philistines are on you, Samson. And men were waiting secretly in the inner room. And the cords were broken off his arms like threads.
13 Sa’an nan Delila ta ce, “Har yanzu, ka mai da shashasha, kana mai da ni wawiya kana kuma yin mini ƙarya. Ka gaya mini yadda za a daure ka mana.” Ya ce mata, “In kin yi kitson gashin kaina guda bakwai kika ɗaura su da zare kika buga su da akwasha, zan rasa ƙarfi in zama kamar kowa.” Saboda haka yayinda yake barci, sai Delila ta yi kitson gashin kansa guda bakwai ta ɗinka su da zare,
Then Delilah said to Samson, Up to now you have made sport of me with false words; now say truly, how may you be put in bands? And he said to her, If you get the seven twists of my hair worked into the cloth you are making and fixed with the pin, I will become feeble and will be like any other man.
14 ta kuma ɗaura su da akwasha. Ta sāke yin ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka.” Ya tashi daga barcinsa ya tumɓuke akwashan tare da zaren da aka ɗaura gashin kansa da su.
So while he was sleeping she got the seven twists of his hair worked into her cloth and fixed with the pin, and said to him, The Philistines are on you, Samson. Then awaking from his sleep, he got up quickly, pulling up cloth and machine together.
15 Sa’an nan ta ce masa, “Yaya kake cewa kana sona alhali ba ka yarda da ni ba? Wannan shi ne sau na uku kana mai da ni wawiya kuma ba ka nuna mini asirin ƙarfinka ba.”
And she said to him, Why do you say you are my lover when your heart is not mine? Three times you have made sport of me, and have not made clear to me the secret of your great strength.
16 Da irin wannan fitina ta tsokane shi kwana da kwanaki har sai da ya gaji kamar zai mutu.
So day after day she gave him no peace, for ever questioning him till his soul was troubled to death.
17 Saboda haka sai ya faɗa mata kome ya ce, “Ba a taɓa sa reza a kaina ba, domin ni Naziri ne keɓaɓɓe ga Allah tun haihuwa. In kuwa an aske kaina, ƙarfina zai rabu da ni, sai in zama kamar kowa.”
And opening all his heart to her, he said to her, My head has never been touched by a blade, for I have been separate to God from the day of my birth: if my hair is cut off, then my strength will go from me and I will become feeble, and will be like any other man.
18 Da Delila ta gane ya gaya mata kome yanzu, sai ta aika saƙo zuwa ga shugabannin Filistiyawa ta ce, “Ku ƙara zuwa sau ɗayan nan, ai, ya gaya mini kome.” Saboda haka shugabannin Filistiyawa suka dawo tare da azurfa a hannuwansu.
And when Delilah saw that he had let her see into his heart, she sent word to the chiefs of the Philistines saying, Come up this time, for he has let out all his heart to me. Then the chiefs of the Philistines came to her, with the money in their hands.
19 Bayan ta sa shi ya yi barci a cinyarta, sai ta kira wani ya zo ya aske kitso guda bakwai nan a kansa, aka fara rinjayensa. Ƙarfinsa kuwa ya rabu da shi.
And she made him go to sleep on her knees; and she sent for a man and had his seven twists of hair cut off; and while it was being done he became feeble and his strength went from him.
20 Sa’an nan ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Sai ya farka daga barci yana tsammani cewa, “Zan fita kamar dā in miƙe jikina.” Amma bai san cewa Ubangiji ya rabu da shi ba.
Then she said, The Philistines are on you, Samson. And awaking from his sleep, he said, I will go out as at other times, shaking myself free. But he was not conscious that the Lord had gone from him.
21 Sa’an nan Filistiyawa suka fizge shi, suka ƙwaƙule idanunsa suka gangara da shi zuwa Gaza. Da suka daure shi da sarƙoƙin tagulla, sai aka sa shi yana niƙa a kurkuku.
So the Philistines took him and put out his eyes; then they took him down to Gaza, and, chaining him with bands of brass, put him to work crushing grain in the prison-house.
22 Amma gashi kansa ya fara tohuwa kuma bayan an aske shi.
But the growth of his hair was starting again after it had been cut off.
23 To, sai Filistiyawa suka taru don su miƙa hadaya ga Dagon allahnsu su kuma yi biki cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu Samson a hannuwanmu.”
And the chiefs of the Philistines came together to make a great offering to Dagon their god, and to be glad; for they said, Our god has given into our hands Samson our hater.
24 Sa’ad da mutane suka gan shi, sai suka yabi allahnsu, suna cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu a hannunmu, wanda ya lalace ƙasarmu ya kuma raɓanya kisan mutanenmu.”
And when the people saw him, they gave praise to their god; for they said, Our god has given into our hands the one who was fighting against us, who made our country waste, and who put great numbers of us to death.
25 Yayinda suke cikin farin ciki, sai suka yi ihu, suka ce, “Fito mana da Samson yă yi mana wasa.” Saboda haka aka zo da Samson daga kurkuku, shi kuwa ya yi wasa a gabansu. Sa’ad da suka tsai da shi a tsakanin ginshiƙai,
Now when their hearts were full of joy, they said, Send for Samson to make sport for us. And they sent for Samson out of the prison-house, and he made sport before them; and they put him between the pillars.
26 sai Samson ya ce wa bawan da ya riƙe hannunsa, “Ka kai ni inda zan taɓa ginshiƙan da suke ɗauke da wannan haikali, don in jingina a kai.”
And Samson said to the boy who took him by the hand, Let me put my hand on the pillars supporting the house, so that I may put my back against them.
27 To, haikalin ya cika da mutane maza da mata; dukan shugabannin Filistiyawa kuwa suna a can, a bisan rufin kuwa akwai mutum wajen dubu uku maza da mata suna kallon Samson yana wasa.
Now the house was full of men and women; and all the lords of the Philistines were there; and about three thousand men and women were on the roof, looking on while Samson made sport.
28 Sa’an nan Samson ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ya Allah ka tuna da ni, ka ƙarfafa ni sau ɗaya nan kaɗai, ka bar ni da bugu ɗaya kawai in ɗauki fansa a kan Filistiyawa domin idanuna.”
And Samson, crying out to the Lord, said, O Lord God, do have me now in mind, and do make me strong only this once, O God, so that I may take one last payment from the Philistines for my two eyes.
29 Sa’an nan Samson ya kai hannuwansa ga ginshiƙan waɗanda haikalin yake a kai, ya jingina jikinsa, hannunsa dama yana a ɗaya, hannun hagu kuma na ɗayan,
Then Samson put his arms round the two middle pillars supporting the house, putting his weight on them, on one with his right hand and on the other with his left.
30 Samson ya ce, “Bari in mutu tare da Filistiyawa!” Sa’an nan da dukan ƙarfinsa ya tura haikali ya fāɗa a kan shugabanni da dukan mutanen da suke ciki. Ta haka ya kashe mutane da yawa fiye da yayinda yake da rai.
And Samson said, Let death overtake me with the Philistines. And he put out all his strength, and the house came down on the chiefs and on all the people who were in it. So the dead whom he sent to destruction by his death were more than all those on whom he had sent destruction in his life.
31 Sa’an nan’yan’uwansa da dukan dangin mahaifinsa suka gangaro don su ɗauke shi. Suka kawo shi suka binne tsakanin Zora da Eshtawol a kabarin Manowa mahaifinsa. Ya yi mulkin Isra’ila shekara ashirin.
Then his brothers and his father's people came down and took him up and put his body to rest in the earth between Zorah and Eshtaol in the resting-place of Manoah his father. And he had been judge of Israel for twenty years.

< Mahukunta 16 >