< Mahukunta 16 >

1 Wata rana Samson ya tafi Gaza, inda ya ga wata karuwa. Ya shiga wurinta ya kwana.
Samson drog så til Gaza. Der så han en Skøge og gik ind til hende.
2 Aka gaya wa mutanen Gaza, “Ai, Samson yana a nan!” Saboda haka suka zo suka kewaye wurin suka yi kwanto dukan dare a bakin ƙofar birni. A daren nan ba su motsa nan da can ba, suna cewa, “Gari yana wayewa za mu kashe shi.”
Da det spurgtes blandt Folkene i Gaza, at Samson var kommet derhen, gik de hen og lagde sig på Lur efter ham ved Byporten; men de holdt sig rolige Natten over, idet de sagde: "Vi vil vente, til det bliver lyst; så slår vi ham ihjel!"
3 Amma Samson ya yi kwanciyarsa har tsakiyar dare. Sa’an nan ya tashi ya kama ƙofofin birnin, tare da madogarai biyunsu, ya tumɓuke, ya aza su a kafaɗarsa, ya kai su kan dutsen da yake a fuskantar Hebron.
Samson blev liggende den halve Nat, men ved Midnatstide stod han op, greb fat i Byportens to Fløje og begge Portstolper, rykkede dem op tillige med Portslåen, tog dem på Skuldrene og bar dem op på Toppen af Bjerget over for Hebron.
4 Bayan ɗan lokaci, sai ya shiga ƙaunar wata mace, mai suna Delila a Kwarin Sorek.
Siden fik han Kærlighed til en Kvinde ved Navn Dalila i Sorekdalen.
5 Sai shugabannin Filistiyawa suka tafi wurinta suka ce, “Ki yi ƙoƙari ki ga ko za ki rarrashe shi yă nuna miki asirin ƙarfinsa da yadda za mu iya shan ƙarfinsa don mu ɗaura shi mu yi nasara a kansa. Kowannenmu zai ba ki shekel dubu ɗari ɗaya na azurfa.”
Da kom Filisternes Fyrster til hende og sagde til hende: "Se at lokke ud af ham, hvad det er, der giver ham hans vældige Kræfter, og hvorledes vi kan få Bugt med ham, så vi kan binde og kue ham, så vil vi hver give dig 1100 Sekel Sølv!"
6 Saboda haka Delila ta ce wa Samson, “Ka faɗa miki asirin ƙarfinka da yadda za a ɗaura ka a yi nasara a kanka.”
Dalila sagde da til Samson: "Sig mig dog, hvad det er, der giver dig dine vældige Kræfter, og hvorledes man kan binde og kue dig!"
7 Samson ya ce mata, “In wani ya ɗaura ni da sababbin igiyoyin da ba su bushe ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
Samson svarede hende: "Hvis man binder mig med syv friske Strenge, som ikke er blevet tørre, bliver jeg svag som ethvert andet Menneske."
8 Sa’an nan shugabannin Filistiyawa suka kawo mata sababbin igiyoyi guda bakwai da ba su bushe ba, sai ta daure shi da su.
Filisternes Fyrster bragte hende da syv friske Strenge, der ikke var blevet tørre, og med dem bandt hun ham;
9 Da mutane a ɓoye a cikin ɗaki tare da ita, sai ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Da jin haka sai ya tsintsinke igiyoyin kamar zaren da ya yi kusa da harshen wuta. Saboda haka asirin ƙarfinsa bai tonu ba.
samtidig havde hun Folk liggende på Lur i Kammeret. Da sagde hun til ham: "Filisterne er over dig, Samson!" Men han rev Strengene over, og de brast som Blårgarn, der kommer Ild for nær; og hvorledes det hang sammen med hans Kræfter, kom ikke for Dagen.
10 Sa’an nan Delila ta ce wa Samson, “Ka mai da ni wawiya; ka ruɗe ni. Yanzu, ka gaya mini yadda za a daure ka.”
Da sagde Dalila til Samson: "Se, du har narret mig og løjet for mig; sig mig dog, hvorledes man kan binde dig!"
11 Ya ce, “In wani ya ɗaura ni sosai da sababbin igiyoyin da ba a taɓa amfani da su ba, zan zama marar ƙarfi kamar kowa.”
Han svarede hende: "Hvis man binder mig med nye Reb, som aldrig har været brug til noget, bliver jeg svag som ethvert andet Menneske!"
12 Saboda haka Delila ta ɗauki sababbin igiyoyi ta ɗaura shi da su. Sa’an nan, tare da mutane a ɓoye a ɗakin, ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Amma sai ya tsintsinke su kamar zare.
Da tog Dalila nye Reb og bandt ham. Så sagde hun til ham: "Filisterne er over dig, Samson!" Samtidig lå der Folk på Lur i Kammeret. Men han flåede Rebene af sine Arme, som var det Tråde.
13 Sa’an nan Delila ta ce, “Har yanzu, ka mai da shashasha, kana mai da ni wawiya kana kuma yin mini ƙarya. Ka gaya mini yadda za a daure ka mana.” Ya ce mata, “In kin yi kitson gashin kaina guda bakwai kika ɗaura su da zare kika buga su da akwasha, zan rasa ƙarfi in zama kamar kowa.” Saboda haka yayinda yake barci, sai Delila ta yi kitson gashin kansa guda bakwai ta ɗinka su da zare,
Da sagde Dalila til Samson: "Hidtil har du narret mig og løjet for mig; sig mig dog, hvorledes man kan binde dig!" Han svarede hende: "Hvis du væver mine syv Hovedlokker ind i Rendegarnet og slår dem fast med Slagelen, bliver jeg svag som ethvert andet Menneske."
14 ta kuma ɗaura su da akwasha. Ta sāke yin ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka.” Ya tashi daga barcinsa ya tumɓuke akwashan tare da zaren da aka ɗaura gashin kansa da su.
Så dyssede hun ham i Søvn og vævede hans syv Hovedlokker ind i Rendegarnet og slog dem fast med Slagelen. Og hun sagde til ham: "Filisterne er over dig, Samson!" Så vågnede han og rykkede Væven op sammen med Rendegarnet.
15 Sa’an nan ta ce masa, “Yaya kake cewa kana sona alhali ba ka yarda da ni ba? Wannan shi ne sau na uku kana mai da ni wawiya kuma ba ka nuna mini asirin ƙarfinka ba.”
Da sagde hun til ham: "Hvor kan du sige, du elsker mig, når du ingen Fortrolighed har til mig? Tre Gange har du nu narret mig og ikke sagt mig, hvad det er, der giver dig dine vældige Kræfter!"
16 Da irin wannan fitina ta tsokane shi kwana da kwanaki har sai da ya gaji kamar zai mutu.
Da hun således stadig pinte og plagede ham med sine Ord, blev hans Sjæl træt til Døden,
17 Saboda haka sai ya faɗa mata kome ya ce, “Ba a taɓa sa reza a kaina ba, domin ni Naziri ne keɓaɓɓe ga Allah tun haihuwa. In kuwa an aske kaina, ƙarfina zai rabu da ni, sai in zama kamar kowa.”
og han talte rent ud og sagde til hende: "Ingen Ragekniv er kommet på mit Hoved, thi jeg har fra Moders Liv af været en Guds Nasiræer; hvis mit Hår rages af, mister jeg mine Kræfter og bliver svag som alle andre Mennesker."
18 Da Delila ta gane ya gaya mata kome yanzu, sai ta aika saƙo zuwa ga shugabannin Filistiyawa ta ce, “Ku ƙara zuwa sau ɗayan nan, ai, ya gaya mini kome.” Saboda haka shugabannin Filistiyawa suka dawo tare da azurfa a hannuwansu.
Da nu Dalila skønnede, at han havde talt rent ud til hende, sendte hun Bud efter Filisternes Fyrster og lod sige: "Kom nu herop, thi han har talt rent ud til mig!" Og Filisternes Fyrster kom op til hende og bragte Pengene med.
19 Bayan ta sa shi ya yi barci a cinyarta, sai ta kira wani ya zo ya aske kitso guda bakwai nan a kansa, aka fara rinjayensa. Ƙarfinsa kuwa ya rabu da shi.
Så dyssede hun ham i Søvn imellem sine Knæ og kaldte på en Mand, som ragede hans syv Hovedlokker af. Da blev han svagere og svagere, og Kræfterne veg fra ham.
20 Sa’an nan ta yi ihu ta ce, “Samson ga Filistiyawa sun zo su kama ka!” Sai ya farka daga barci yana tsammani cewa, “Zan fita kamar dā in miƙe jikina.” Amma bai san cewa Ubangiji ya rabu da shi ba.
Derpå sagde hun: Filisterne er over dig, Samson!" Da vågnede han og tænkte: "Jeg skal nok slippe fra det ligesom de andre Gange og ryste det af mig!" Men han vidste ikke, at HERREN var veget fra ham.
21 Sa’an nan Filistiyawa suka fizge shi, suka ƙwaƙule idanunsa suka gangara da shi zuwa Gaza. Da suka daure shi da sarƙoƙin tagulla, sai aka sa shi yana niƙa a kurkuku.
Da greb Filisterne ham og stak Øjnene ud på ham; derpå bragte de ham ned til Gaza og lagde ham i Kobberlænker; og han måtte dreje Kværnen i Fangehuset.
22 Amma gashi kansa ya fara tohuwa kuma bayan an aske shi.
Men hans Hovedhår begyndte at vokse igen, efter at det var raget af.
23 To, sai Filistiyawa suka taru don su miƙa hadaya ga Dagon allahnsu su kuma yi biki cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu Samson a hannuwanmu.”
Filisternes Fyrster samledes nu for at holde en stor Offerfest til Ære for deres Gud Dagon og for at fornøje sig; og de sagde: "Vor Gud gav os i Hænde Samson, vor Fjende!"
24 Sa’ad da mutane suka gan shi, sai suka yabi allahnsu, suna cewa, “Allahnmu ya bashe abokin gābanmu a hannunmu, wanda ya lalace ƙasarmu ya kuma raɓanya kisan mutanenmu.”
Og da Folket så ham, priste de deres Gud og råbte: "Vor Gud gav os i Hænde Samson, vor Fjende, ham, som vort Land monne skænde, på manges Liv gjorde Ende!"
25 Yayinda suke cikin farin ciki, sai suka yi ihu, suka ce, “Fito mana da Samson yă yi mana wasa.” Saboda haka aka zo da Samson daga kurkuku, shi kuwa ya yi wasa a gabansu. Sa’ad da suka tsai da shi a tsakanin ginshiƙai,
Da de nu var kommet i godt Lune, sagde de: "Hent Samson, at vi kan more os over ham!" De lod da Samson hente fra Fangehuset, og de morede sig over ham. De stillede ham op ved Søjlerne;
26 sai Samson ya ce wa bawan da ya riƙe hannunsa, “Ka kai ni inda zan taɓa ginshiƙan da suke ɗauke da wannan haikali, don in jingina a kai.”
Da sagde Samson til den unge Mand, som holdt ham i Hånden: "Slip mig og lad mig røre ved Søjlerne, som bærer Hallen, så jeg kan læne mig til dem!".
27 To, haikalin ya cika da mutane maza da mata; dukan shugabannin Filistiyawa kuwa suna a can, a bisan rufin kuwa akwai mutum wajen dubu uku maza da mata suna kallon Samson yana wasa.
Hallen var fuld af Mænd og Kvinder; der var alle Filisternes Fyrster, og på Taget var der henved 3000 Mænd og Kvinder, som så til, medens de morede sig over Samson.
28 Sa’an nan Samson ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, ya Allah ka tuna da ni, ka ƙarfafa ni sau ɗaya nan kaɗai, ka bar ni da bugu ɗaya kawai in ɗauki fansa a kan Filistiyawa domin idanuna.”
Da råbte Samson til HERREN og sagde: "Herre, HERRE, kom mig i Hu og giv mig Kraft, o Gud, kun denne ene Gang, så jeg kan hævne mig på Filisterne for begge mine Øjne på een Gang!"
29 Sa’an nan Samson ya kai hannuwansa ga ginshiƙan waɗanda haikalin yake a kai, ya jingina jikinsa, hannunsa dama yana a ɗaya, hannun hagu kuma na ɗayan,
Så greb Samson om de to Midtersøjler, som bar Hallen, og stemmede sig imod den ene med højre og imod den anden med venstre Hånd.
30 Samson ya ce, “Bari in mutu tare da Filistiyawa!” Sa’an nan da dukan ƙarfinsa ya tura haikali ya fāɗa a kan shugabanni da dukan mutanen da suke ciki. Ta haka ya kashe mutane da yawa fiye da yayinda yake da rai.
Og Samson sagde: "Lad mig dø sammen med Filisterne!" Derpå bøjede han sig med sådan Kraft, at Hallen styrtede sammen over Fyrsterne og alle Folkene derinde. Således dræbte han ved sin Død flere, end han havde dræbt i levende Live.
31 Sa’an nan’yan’uwansa da dukan dangin mahaifinsa suka gangaro don su ɗauke shi. Suka kawo shi suka binne tsakanin Zora da Eshtawol a kabarin Manowa mahaifinsa. Ya yi mulkin Isra’ila shekara ashirin.
Men hans Brødre og hele hans Faders Hus drog ned og tog ham, bragte ham op og lagde ham i hans Fader Manoas Grav mellem Zora og Esjtaol. Han var Dommer i Israel i tyve År.

< Mahukunta 16 >