< Mahukunta 15 >

1 Daga baya, a lokacin girbin alkama, Samson ya ɗauki ɗan akuya ya tafi yă ziyarci matarsa. Sai ya ce, “Zan in shiga ɗakin matata.” Amma mahaifinta ya hana shi shiga.
Or il arriva quelques jours après, au temps de la moisson des bleds, que Samson alla visiter sa femme, [lui] portant un chevreau de lait, et il dit: J'entrerai vers ma femme en sa chambre; mais son père ne lui permit point d'y entrer;
2 Ya ce wa, “Na tabbata ba ka sonta sam-sam, don haka na ba da ita ga abokinka. Ba ƙanuwarta ta fi kyau ba? Ka ɗauke ta a maimako.”
Car il lui dit: J'ai cru que tu avais certainement de l'aversion pour elle, c'est pourquoi je l'ai donnée à ton compagnon. Sa sœur puînée n'est-elle pas plus belle qu'elle? je te prie donc qu'elle soit ta [femme] au lieu d'elle.
3 Samson kuwa ya ce musu, “A wannan lokaci ina da iko in rama a kan Filistiyawa; tabbatacce zan ji musu.”
Et Samson leur dit: A présent je serai innocent à l'égard des Philistins quand je leur ferai du mal.
4 Saboda haka ya tafi ya kama yanyawa ɗari uku ya ɗaura wutsiyoyinsu wutsiya da wutsiya. Sa’an nan ya daure acibalbal a tsakanin ko waɗanne wutsiya biyu,
Samson donc s'en alla, et prit trois cents renards; il prit aussi des flambeaux, et il tourna les renards queue contre queue, et mit un flambeau entre les deux queues, tout au milieu.
5 sai ya sa wa acibalbal wuta, ya saki yanyawan suka shiga gonakin Filistiyawa. Suka ƙone dammunan hatsi da hatsin da yake tsaye, tare da gonakin inabi da na zaitun.
Puis il mit le feu aux flambeaux, et lâcha les [renards] aux bleds des Philistins qui étaient sur le pied; et il brûla tant le bled qui était en gerbes, que celui qui était sur le pied, même jusqu'aux vignes et aux oliviers.
6 Filistiyawa suka yi tambaya suka ce, “Wane ne ya yi wannan abu?” Sai aka ce musu, “Ai, Samson ne surukin mutumin Timna, domin an ba wa abokinsa matarsa.” Saboda haka Filistiyawa suka haura suka je suka ƙone ta da mahaifinta ƙurmus da wuta.
Et les Philistins dirent: Qui a fait cela? Et on répondit: Samson, le beau-fils du Timnien, parce qu'il lui a pris sa femme, et qu'il l'a donnée à son compagnon. Les Philistins donc montèrent, et la brûlèrent au feu, avec son père.
7 Samson ya ce musu, “Tun da kun aikata wannan, ba zan bari ba har sai na ɗau fansa a kanku.”
Alors Samson leur dit: Est-ce donc ainsi que vous faites? Cependant je me vengerai de vous avant que je cesse.
8 Ya kuwa fāɗa musu ya kuma karkashe su da yawa. Sa’an nan ya gangara ya zauna a kogo a dutsen Etam.
Et il les battit entièrement, et en fit un grand carnage; puis il descendit, et s'arrêta dans un quartier du rocher de Hétam.
9 Filistiyawa suka haura suka yi sansani a Yahuda, suka bazu kusa da Lehi.
Alors les Philistins montèrent, et se campèrent en Juda, et se répandirent en Léhi.
10 Mutanen Yahuda suka ce, “Me ya sa kuka zo mana da yaƙi?” Sai suka ce, “Mun zo ne mu kama Samson, a matsayin fursunan yaƙi, mu yi masa kamar yadda ya yi mana.”
Et les hommes de Juda dirent: Pourquoi êtes-vous montés contre nous? Ils répondirent: Nous sommes montés pour lier Samson, afin que nous lui fassions comme il nous a fait.
11 Sa’an nan mutane dubu uku daga Yahuda suka gangara wajen Samson a kogo a dutsen Etam. Suka ce masa, “Ba ka san cewa Filistiyawa ne suke mulkinmu ba? Me ke nan ka yi mana?” Ya ce musu, “Na ɗan yi musu abin da suka yi mini ne.”
Alors trois mille hommes de Juda descendirent vers le quartier du rocher de Hétam, et dirent à Samson: Ne sais-tu pas que les Philistins dominent sur nous; pourquoi donc nous as-tu fait ceci? Il leur répondit: Je leur ai fait comme ils m'ont fait.
12 Suka ce masa, “To, mun zo ne mu daure ka mu kai wa Filistiyawa.” Samson ya ce, “Ku rantse mini ba za ku kashe ni da kanku ba.”
Ils lui dirent encore: Nous sommes descendus pour te lier, afin de te livrer entre les mains des Philistins. Et Samson leur dit: Jurez-moi que vous ne vous jetterez point sur moi.
13 Suka ce, “Mun yarda, za mu dai daure ka mu ba da kai gare su. Ba za mu kashe ka ba.” Saboda haka suka daure shi da sababbin igiyoyi biyu, suka saukar da shi daga dutsen.
Et ils répondirent, et dirent: Non, mais nous te lierons très-bien, afin de te livrer entre leurs mains; mais nous ne te tuerons point. Ils le lièrent donc de deux cordes neuves, et le firent monter hors du rocher.
14 Yayinda ya zo gab da Lehi, sai Filistiyawa suka sheƙo a guje da ihu suka nufo shi. Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko da iko a kansa. Igiyoyin da suke daure a hannuwansa kuwa suka zama kamar abin da wuta ta babbaka, suka tsintsinke suka zuba daga hannuwansa.
Or quand il fut venu jusqu'à Léhi, les Philistins jetèrent des cris de joie à sa rencontre, et l'esprit de l'Eternel le saisit, et les cordes qui étaient sur ses bras, devinrent comme du lin où l'on a mis le feu, et ses liens s'écoulèrent de dessus ses mains.
15 Da ya samo muƙamuƙin jaki, ya ɗauka, sai ya karkashe mutane dubu ɗaya.
Et ayant trouvé une mâchoire d'âne qui n'était pas encore desséchée, il avança sa main, la prit, et il en tua mille hommes.
16 Sa’an nan Samson ya ce, “Da muƙamuƙin jaki na mai da su jakuna. Da muƙamuƙin jaki na kashe mutum dubu.”
Puis Samson dit: Avec une mâchoire d'âne, un monceau, deux monceaux; avec une mâchoire d'âne j'ai tué mille hommes.
17 Da ya gama magana, sai ya jefar da muƙamuƙin; aka ba wa wannan wuri suna Ramat Lehi.
Et quand il eut achevé de parler, il jeta de sa main la mâchoire, et nomma ce lieu-là Ramath-léhi.
18 Saboda ƙishirwa ta kama shi ƙwarai, sai ya ce wa Ubangiji, “Ka ba bawanka wannan babbar nasara. To, sai in mutu da ƙishirwa, har in shiga a hannun marasa kaciyan nan su kashe ni?”
Et il eut une fort grande soif, et il cria à l'Eternel en disant: Tu as mis en la main de ton serviteur cette grande délivrance, et maintenant mourrais-je de soif, et tomberais-je entre les mains des incirconcis?
19 Sa’an nan Allah ya buɗe wani rami a Lehi, ruwa kuwa ya fito daga ciki. Da Samson ya sha, sai ƙarfinsa ya dawo, ya kuma wartsake. Aka sa wa wannan maɓulɓula suna En Hakkore, yana nan a Lehi har wa yau.
Alors Dieu fendit une des grosses dents de cette mâchoire d'âne, et il en sortit de l'eau; et quand [Samson] eut bu, l'esprit lui revint, et il reprit ses forces; : c'est pourquoi ce lieu-là a été appelé jusqu'à ce jour Hen-hakkoré, qui est à Léhi.
20 Samson kuwa ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin a zamanin Filistiyawa.
Or [Samson] jugea Israël au temps des Philistins, vingt ans.

< Mahukunta 15 >