< Mahukunta 15 >

1 Daga baya, a lokacin girbin alkama, Samson ya ɗauki ɗan akuya ya tafi yă ziyarci matarsa. Sai ya ce, “Zan in shiga ɗakin matata.” Amma mahaifinta ya hana shi shiga.
And it came to pass after a time, in the days of wheat harvest, that Sampson visited his wife with a kid, and said, I will go in to my wife even into the chamber: but her father did not suffer him to go in.
2 Ya ce wa, “Na tabbata ba ka sonta sam-sam, don haka na ba da ita ga abokinka. Ba ƙanuwarta ta fi kyau ba? Ka ɗauke ta a maimako.”
And her father spoke, saying, I said that you did surely hate her, and I gave her to one of your friends: [is] not her younger sister better than she? let her be to you instead of her.
3 Samson kuwa ya ce musu, “A wannan lokaci ina da iko in rama a kan Filistiyawa; tabbatacce zan ji musu.”
And Sampson said to them, Even for once am I guiltless with regard to the Philistines, in that I do mischief among them.
4 Saboda haka ya tafi ya kama yanyawa ɗari uku ya ɗaura wutsiyoyinsu wutsiya da wutsiya. Sa’an nan ya daure acibalbal a tsakanin ko waɗanne wutsiya biyu,
And Sampson went and caught three hundred foxes, and took torches, and turned tail to tail, and put a torch between two tails, and fastened it.
5 sai ya sa wa acibalbal wuta, ya saki yanyawan suka shiga gonakin Filistiyawa. Suka ƙone dammunan hatsi da hatsin da yake tsaye, tare da gonakin inabi da na zaitun.
And he set fire to the torches, and sent [the foxes] into the corn of the Philistines; and every thing was burnt from the threshing floor to the standing corn, and even to the vineyard and olives.
6 Filistiyawa suka yi tambaya suka ce, “Wane ne ya yi wannan abu?” Sai aka ce musu, “Ai, Samson ne surukin mutumin Timna, domin an ba wa abokinsa matarsa.” Saboda haka Filistiyawa suka haura suka je suka ƙone ta da mahaifinta ƙurmus da wuta.
And the Philistines said, Who [has done] these things? and they said, Sampson the son-in-law of the Thamnite, because he has taken his wife, and given her to one of his friends; and the Philistines went up, and burnt her and her father's house with fire.
7 Samson ya ce musu, “Tun da kun aikata wannan, ba zan bari ba har sai na ɗau fansa a kanku.”
And Sampson said to them, Though you may have dealt thus with her, verily I will be avenged of you, and afterwards I will cease.
8 Ya kuwa fāɗa musu ya kuma karkashe su da yawa. Sa’an nan ya gangara ya zauna a kogo a dutsen Etam.
And he struck them leg on thigh [with] a great overthrow; and went down and lived in a cave of the rock Etam.
9 Filistiyawa suka haura suka yi sansani a Yahuda, suka bazu kusa da Lehi.
And the Philistines went up, and encamped in Juda, and spread themselves abroad in Lechi.
10 Mutanen Yahuda suka ce, “Me ya sa kuka zo mana da yaƙi?” Sai suka ce, “Mun zo ne mu kama Samson, a matsayin fursunan yaƙi, mu yi masa kamar yadda ya yi mana.”
And the men of Juda said, Why are you come up against us? and the Philistines said, We are come up to bind Sampson, and to do to him as he has done to us.
11 Sa’an nan mutane dubu uku daga Yahuda suka gangara wajen Samson a kogo a dutsen Etam. Suka ce masa, “Ba ka san cewa Filistiyawa ne suke mulkinmu ba? Me ke nan ka yi mana?” Ya ce musu, “Na ɗan yi musu abin da suka yi mini ne.”
And the three thousand men of Juda went down to the hole of the rock Etam, and they said to Sampson, Know you not that the Philistines rule over us? and what [is] this [that] you have done to us? and Sampson said to them, As they did to me, so have I done to them.
12 Suka ce masa, “To, mun zo ne mu daure ka mu kai wa Filistiyawa.” Samson ya ce, “Ku rantse mini ba za ku kashe ni da kanku ba.”
And they said to him, We are come down to bind you to deliver you into the hand of the Philistines: and Sampson said to them, Swear to me that you will not fall upon me yourselves.
13 Suka ce, “Mun yarda, za mu dai daure ka mu ba da kai gare su. Ba za mu kashe ka ba.” Saboda haka suka daure shi da sababbin igiyoyi biyu, suka saukar da shi daga dutsen.
And they spoke to him, saying, Nay, but we will only bind you fast, and deliver you into their hand, and will by no means kill you: and they bound him with two new ropes, and brought him from that rock.
14 Yayinda ya zo gab da Lehi, sai Filistiyawa suka sheƙo a guje da ihu suka nufo shi. Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko da iko a kansa. Igiyoyin da suke daure a hannuwansa kuwa suka zama kamar abin da wuta ta babbaka, suka tsintsinke suka zuba daga hannuwansa.
And they came to Lechi: and the Philistines shouted, and ran to meet him: and the Spirit of the Lord came mightily upon him, and the ropes that were upon his arms became as tow which is burnt with fire; and his bonds were consumed from off his hands.
15 Da ya samo muƙamuƙin jaki, ya ɗauka, sai ya karkashe mutane dubu ɗaya.
And he found the jaw-bone of an ass that had been cast away, and he put forth his hand and took it, and struck with it a thousand men.
16 Sa’an nan Samson ya ce, “Da muƙamuƙin jaki na mai da su jakuna. Da muƙamuƙin jaki na kashe mutum dubu.”
And Sampson said, With the jaw-bone of an ass I have utterly destroyed them, for with the jaw-bone of an ass I have struck a thousand men.
17 Da ya gama magana, sai ya jefar da muƙamuƙin; aka ba wa wannan wuri suna Ramat Lehi.
And it came to pass when he ceased speaking, that he cast the jaw-bone out of his hand; and he called that place the Lifting of the jaw-bone.
18 Saboda ƙishirwa ta kama shi ƙwarai, sai ya ce wa Ubangiji, “Ka ba bawanka wannan babbar nasara. To, sai in mutu da ƙishirwa, har in shiga a hannun marasa kaciyan nan su kashe ni?”
And he was very thirsty, and wept before the Lord, and said, You have been well pleased to grant this great deliverance by the hand of your servant, and new shall I die for thirst, and fall into the hand of the uncircumcised?
19 Sa’an nan Allah ya buɗe wani rami a Lehi, ruwa kuwa ya fito daga ciki. Da Samson ya sha, sai ƙarfinsa ya dawo, ya kuma wartsake. Aka sa wa wannan maɓulɓula suna En Hakkore, yana nan a Lehi har wa yau.
And God broke open a hollow place in the jaw, and there came thence water, and he drank; and his spirit returned and he revived: therefore the name of the fountain was called 'The well of the invoker,' which is in Lechi, until this day.
20 Samson kuwa ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin a zamanin Filistiyawa.
And he judged Israel in the days of the Philistines twenty years.

< Mahukunta 15 >