< Mahukunta 14 >

1 Samson ya gangara zuwa Timna a can ya ga wata daga cikin’yan mata Filistiyawa.
Ensuite Samson descendit à Thamnatha; et voyant là une femme d’entre les filles des Philistins,
2 Da ya komo, sai ya gaya wa mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, “Na ga wata mace a Timna; ku auro mini ita ta zama matata.”
Il monta, et il l’annonça à son père et à sa mère, disant: J’ai vu à Thamnatha une femme d’entre les filles des Philistins, que je vous prie d’accepter pour mon épouse.
3 Mahaifinsa da mahaifiyarsa suka ce, “Babu wata karɓaɓɓiyar yarinya a cikin zuriyarku ko cikin dukan mutanenmu ne? Dole ne ka tafi wajen Filistiyawa marasa kaciya ka nemi aure?” Amma Samson ya ce wa mahaifinsa, “A auro mini ita dai. Ita ta dace da ni.”
Son père et sa mère lui répondirent: Est-ce qu’il n’y a point de femme parmi les filles de tes frères, et dans tout mon peuple, puisque tu veux prendre une femme d’entre les Philistins qui sont incirconcis? Et Samson dit à son père: Acceptez-la pour moi, parce qu’elle a plu à mes yeux.
4 (Iyayensa ba su san cewa wannan daga wurin Ubangiji ne ba, wanda yake neman hanyar da za a kai wa Filistiyawa hari; gama a lokacin suna mulkin Isra’ila.)
Mais ses parents ne savaient pas que la chose se faisait par le Seigneur, et qu’il cherchait une occasion contre les Philistins; car en ce temps-là les Philistins dominaient sur Israël.
5 Sai Samson ya gangara zuwa Timna tare da mahaifinsa da kuma mahaifiyarsa. Da suka yi kusa da gonar inabin Timna, nan da nan sai ga ɗan zaki ya taso ya nufe shi yana ruri.
C’est pourquoi Samson descendit avec son père et sa mère à Thamnatha. Et, lorsqu’ils furent arrivés aux vignes de la ville, parut le petit d’un lion furieux et rugissant, et il vint à la rencontre de Samson.
6 Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko masa da ƙarfi, ya sa ya yaga zakin kashi biyu da hannu kamar yadda akan yayyage ɗan akuya. Sai dai bai gaya wa iyayensa abin da ya yi ba.
Mais l’Esprit du Seigneur s’empara de Samson, qui déchira le lion comme il aurait mis un chevreau en pièces, n’ayant absolument rien dans la main; et il ne voulut pas le déclarer à son père et à sa mère.
7 Sa’an nan ya gangara ya yi magana da yarinyar, yana kuwa sonsa.
Et il descendit, et il parla à la femme qui avait plu à ses yeux.
8 Daga baya, da ya koma don yă aure ta, sai ya ratse don yă ga gawar zakin. Sai ga taron ƙudan zuma da zuma a ciki,
Et, après quelques jours, revenant pour l’épouser, il se détourna pour voir le corps du lion, et voilà qu’un essaim d’abeilles était dans la gueule du lion, et un rayon de miel.
9 wanda ya sa hannu ya ɗebo yana tafiya yana sha. Sa’ad da ya iso wurin iyayensa, ya ba su zuman, su ma suka sha. Sai dai bai gaya musu cewa ya ɗebo zuman daga gawar zaki ba.
Ayant pris ce rayon dans ses mains, il le mangeait en chemin; et étant arrivé chez son père et sa mère, il leur en donna une partie, qu’eux-mêmes aussi mangèrent; mais cependant il ne voulut pas leur déclarer qu’il avait pris le miel dans la gueule du lion.
10 To, mahaifinsa ya gangara don yă ga yarinyar. Samson kuwa ya shirya wata liyafa a can, yadda yake bisa ga al’adar angwaye.
Son père descendit donc chez cette femme, et il fit pour son fils Samson un festin; car c’est ainsi que les jeunes gens avaient coutume de faire.
11 Sa’ad da ya bayyana, sai aka haɗa shi abokai talatin.
Or, lorsque les habitants de ce lieu l’eurent vu, ils lui donnèrent trente jeunes hommes pour être avec lui.
12 Sai Samson ya ce, “Bari in yi muku kacici-kacici, in kun ba ni amsa cikin kwana bakwai na wannan biki, zan ba ku riguna lilin talatin da kuma tufafi talatin.
Samson leur dit: Je vous proposerai une énigme; si vous me l’expliquez pendant les sept jours du festin, je vous donnerai trente vêtements de dessous et autant de tuniques;
13 In kuma ba ku iya ba ni amsar ba, dole ku ba ni rigunan lilin talatin da tufafi talatin.” Suka ce, “Ka gaya mana kacici-kacicin.”
Mais si vous ne pouvez pas l’expliquer, c’est vous qui me donnerez trente vêtements de dessous et des tuniques en même nombre. Ils lui répondirent: Propose l’énigme afin que nous l’entendions.
14 Sai ya ce, “Daga mai ci, abinci ya fito; daga mai ƙarfi, abu mai zaki ya fito.” Har kwana uku ba su iya ba da amsa ba.
Alors Samson leur dit: De celui qui mangeait est sortie une nourriture, et du fort est sorti de la douceur; et ils ne purent point pendant trois jours expliquer l’énigme.
15 A rana ta huɗu suka ce wa matar Samson “Ki rarrashi mijinki yă bayyana mana kacici-kacicin, ko kuwa mu ƙone ki da gidan mahaifinki duka da wuta. Kun kira mu domin ku yi mana fashi ne?”
Mais, lorsqu’approchait le septième jour, ils dirent à la femme de Samson: Gagne ton mari par tes caresses, et persuade-lui de te donner la signification de l’énigme; que si tu ne veux pas le faire, nous te brûlerons, toi et la maison de ton père; est-ce que tu ne nous as appelés aux noces que pour nous dépouiller?
16 Sa’an nan matar Samson ta kwanta masa a jiki tana kuka tana cewa, “Kai maƙiyina ne, lalle ba ka ƙaunata, ka yi wa mutanena kacici-kacici, amma ba ka gaya mini amsar ba.” Ya amsa ya ce, “Ban ma bayyana wa mahaifina ko mahaifiyata ba, to, don me zan bayyana miki?”
Elle répandait des larmes auprès de Samson, et se plaignait, disant: Tu me hais et tu ne m’aimes point; c’est pour cela que tu ne veux pas m’expliquer l’énigme que tu as proposée aux fils de mon peuple. Mais Samson répondit: Je ne l’ai point voulu dire à mon père et à ma mère; et je pourrai te l’expliquer?
17 Ta yi ta kuka har kwana bakwai na bikin. Saboda haka a rana ta bakwai sai ya gaya mata, don ta dame shi. Ita kuwa ta bayyana kacici-kacicin wa mutanenta.
Ainsi, pendant les sept jours du festin elle pleurait devant lui; et enfin le septième jour, comme elle lui était importune, il lui expliqua. Elle aussitôt la fit connaître à ses concitoyens.
18 Kafin rana ta fāɗi a rana ta bakwai mutane garin suka ce masa, “Me ya fi zuma zaki? Me ya fi zaki ƙarfi?” Samson ya ce musu, “Da ba don kun haɗa baki da matata ba, da ba za ku san amsar kacici-kacici ba.”
Et eux dirent à Samson le septième jour avant le coucher du soleil: Quoi de plus doux que du miel, et de plus fort que le lion? Et Samson leur répondit: Si vous n’aviez pas labouré avec ma génisse, vous n’auriez pas découvert mon énigme.
19 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko masa da iko. Sai ya fita ya gangara zuwa Ashkelon, ya kashe mutanensu talatin, ya kwashe kayansu ya kuma ba da rigunarsu ga waɗanda suka bayyana kacici-kacicin. Cike da fushi, ya haura zuwa gidan mahaifinsa.
C’est pourquoi l’esprit du Seigneur s’empara de Samson, et il descendit à Ascalon: et là il tua trente hommes dont il donna les vêtements qu’il leur avait pris à ceux qui avaient expliqué l’énigme. Et étant très irrité il monta à la maison de son père.
20 Aka kuma ɗauki matar Samson aka ba wa ɗaya daga cikin waɗanda suka yi masa hidima a bikin.
Or, sa femme prit pour mari un de ses amis, un de ceux qui l’avaient accompagné à ses noces.

< Mahukunta 14 >