< Mahukunta 14 >
1 Samson ya gangara zuwa Timna a can ya ga wata daga cikin’yan mata Filistiyawa.
Or, Samson descendit à Thimna, et y vit une femme d'entre les filles des Philistins.
2 Da ya komo, sai ya gaya wa mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, “Na ga wata mace a Timna; ku auro mini ita ta zama matata.”
Et étant remonté en sa maison, il le déclara à son père et à sa mère, et leur dit: J'ai vu à Thimna une femme, d'entre les filles des Philistins; maintenant, prenez-la, afin qu'elle soit ma femme.
3 Mahaifinsa da mahaifiyarsa suka ce, “Babu wata karɓaɓɓiyar yarinya a cikin zuriyarku ko cikin dukan mutanenmu ne? Dole ne ka tafi wajen Filistiyawa marasa kaciya ka nemi aure?” Amma Samson ya ce wa mahaifinsa, “A auro mini ita dai. Ita ta dace da ni.”
Et son père et sa mère lui dirent: N'y a-t-il point de femme parmi les filles de tes frères et dans tout ton peuple, que tu ailles prendre une femme chez les Philistins incirconcis? Et Samson dit à son père: Prends-la pour moi, car elle plaît à mes yeux.
4 (Iyayensa ba su san cewa wannan daga wurin Ubangiji ne ba, wanda yake neman hanyar da za a kai wa Filistiyawa hari; gama a lokacin suna mulkin Isra’ila.)
Or, son père et sa mère ne savaient point que cela venait de l'Éternel; car Samson cherchait une occasion contre les Philistins. En ce temps-là, les Philistins dominaient sur Israël.
5 Sai Samson ya gangara zuwa Timna tare da mahaifinsa da kuma mahaifiyarsa. Da suka yi kusa da gonar inabin Timna, nan da nan sai ga ɗan zaki ya taso ya nufe shi yana ruri.
Samson descendit donc à Thimna avec son père et sa mère, et comme ils arrivaient aux vignes de Thimna, voici, un jeune lion rugissant vint à sa rencontre.
6 Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko masa da ƙarfi, ya sa ya yaga zakin kashi biyu da hannu kamar yadda akan yayyage ɗan akuya. Sai dai bai gaya wa iyayensa abin da ya yi ba.
Et l'Esprit de l'Éternel saisit Samson, et il déchira le lion comme il eût déchiré un chevreau, sans avoir rien en sa main. Et il ne raconta point à son père ni à sa mère ce qu'il avait fait.
7 Sa’an nan ya gangara ya yi magana da yarinyar, yana kuwa sonsa.
Il descendit donc, et il parla à la femme, et elle plut aux yeux de Samson.
8 Daga baya, da ya koma don yă aure ta, sai ya ratse don yă ga gawar zakin. Sai ga taron ƙudan zuma da zuma a ciki,
Puis, retournant quelques jours après pour la prendre, il se détourna pour voir le cadavre du lion; et voici, il y avait dans le corps du lion un essaim d'abeilles et du miel.
9 wanda ya sa hannu ya ɗebo yana tafiya yana sha. Sa’ad da ya iso wurin iyayensa, ya ba su zuman, su ma suka sha. Sai dai bai gaya musu cewa ya ɗebo zuman daga gawar zaki ba.
Et il en prit dans ses mains, et continua son chemin en mangeant. Puis, arrivé auprès de son père et de sa mère, il leur en donna, et ils en mangèrent; mais il ne leur raconta pas qu'il avait pris ce miel dans le corps du lion.
10 To, mahaifinsa ya gangara don yă ga yarinyar. Samson kuwa ya shirya wata liyafa a can, yadda yake bisa ga al’adar angwaye.
Cependant son père descendit chez cette femme, et Samson fit là un festin; car c'était la coutume des jeunes gens.
11 Sa’ad da ya bayyana, sai aka haɗa shi abokai talatin.
Et sitôt qu'on le vit, on prit trente convives, pour lui faire compagnie.
12 Sai Samson ya ce, “Bari in yi muku kacici-kacici, in kun ba ni amsa cikin kwana bakwai na wannan biki, zan ba ku riguna lilin talatin da kuma tufafi talatin.
Or Samson leur dit: Je vais vous proposer une énigme. Si vous me l'expliquez pendant les sept jours du festin, et si vous la devinez, je vous donnerai trente tuniques et trente robes de rechange;
13 In kuma ba ku iya ba ni amsar ba, dole ku ba ni rigunan lilin talatin da tufafi talatin.” Suka ce, “Ka gaya mana kacici-kacicin.”
Mais si vous ne me l'expliquez pas, c'est vous qui me donnerez trente tuniques et trente robes de rechange. Et ils lui répondirent: Propose ton énigme, et nous l'écouterons.
14 Sai ya ce, “Daga mai ci, abinci ya fito; daga mai ƙarfi, abu mai zaki ya fito.” Har kwana uku ba su iya ba da amsa ba.
Il leur dit donc: De celui qui dévorait est sorti la nourriture, et du fort est sorti le doux. Et pendant trois jours ils ne purent expliquer l'énigme.
15 A rana ta huɗu suka ce wa matar Samson “Ki rarrashi mijinki yă bayyana mana kacici-kacicin, ko kuwa mu ƙone ki da gidan mahaifinki duka da wuta. Kun kira mu domin ku yi mana fashi ne?”
Et le septième jour ils dirent à la femme de Samson: Persuade à ton mari de nous expliquer l'énigme; autrement nous te brûlerons, toi et la maison de ton père. C'est pour nous dépouiller que vous nous avez invités, n'est-ce pas?
16 Sa’an nan matar Samson ta kwanta masa a jiki tana kuka tana cewa, “Kai maƙiyina ne, lalle ba ka ƙaunata, ka yi wa mutanena kacici-kacici, amma ba ka gaya mini amsar ba.” Ya amsa ya ce, “Ban ma bayyana wa mahaifina ko mahaifiyata ba, to, don me zan bayyana miki?”
La femme de Samson pleura auprès de lui, en disant: Certaine-ment, tu me hais, et tu ne m'aimes point; n'as-tu pas proposé une énigme aux enfants de mon peuple, et tu ne me l'as pas expliquée? Et il lui répondit: Voici, je ne l'ai point expliquée à mon père, ni à ma mère; te l'expliquerais-je, à toi?
17 Ta yi ta kuka har kwana bakwai na bikin. Saboda haka a rana ta bakwai sai ya gaya mata, don ta dame shi. Ita kuwa ta bayyana kacici-kacicin wa mutanenta.
Elle pleura ainsi auprès de lui pendant les sept jours du festin; et au septième jour il la lui expliqua, parce qu'elle le tourmentait. Puis elle l'expliqua aux gens de son peuple.
18 Kafin rana ta fāɗi a rana ta bakwai mutane garin suka ce masa, “Me ya fi zuma zaki? Me ya fi zaki ƙarfi?” Samson ya ce musu, “Da ba don kun haɗa baki da matata ba, da ba za ku san amsar kacici-kacici ba.”
Les hommes de la ville lui dirent donc le septième jour, avant que le soleil se couchât: Quoi de plus doux que le miel, et quoi de plus fort que le lion? Et il leur dit: Si vous n'aviez pas labouré avec ma génisse, vous n'auriez pas trouvé mon énigme.
19 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko masa da iko. Sai ya fita ya gangara zuwa Ashkelon, ya kashe mutanensu talatin, ya kwashe kayansu ya kuma ba da rigunarsu ga waɗanda suka bayyana kacici-kacicin. Cike da fushi, ya haura zuwa gidan mahaifinsa.
Alors l'Esprit de l'Éternel le saisit, et il descendit à Askélon. Et, y ayant tué trente hommes, il prit leurs dépouilles, et donna les robes de rechange à ceux qui avaient expliqué l'énigme; puis, enflammé de colère, il remonta à la maison de son père.
20 Aka kuma ɗauki matar Samson aka ba wa ɗaya daga cikin waɗanda suka yi masa hidima a bikin.
Et la femme de Samson fut donnée à son compagnon, avec lequel il s'était lié.