< Mahukunta 14 >
1 Samson ya gangara zuwa Timna a can ya ga wata daga cikin’yan mata Filistiyawa.
And Samson went down to Timnathah, and saw a woman in Timnathah of the daughters of the Philistines.
2 Da ya komo, sai ya gaya wa mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, “Na ga wata mace a Timna; ku auro mini ita ta zama matata.”
And he went up, and told his father and his mother, and said, I have seen a woman in Timnathah of the daughters of the Philistines; and now take her to me for wife.
3 Mahaifinsa da mahaifiyarsa suka ce, “Babu wata karɓaɓɓiyar yarinya a cikin zuriyarku ko cikin dukan mutanenmu ne? Dole ne ka tafi wajen Filistiyawa marasa kaciya ka nemi aure?” Amma Samson ya ce wa mahaifinsa, “A auro mini ita dai. Ita ta dace da ni.”
Then said unto him his father and his mother, Is there not among the daughters of thy brethren, or among all my people, a woman, that thou art going to take a wife from the Philistines, the uncircumcised? And Samson said unto his father, This one take for me; for she pleaseth me well.
4 (Iyayensa ba su san cewa wannan daga wurin Ubangiji ne ba, wanda yake neman hanyar da za a kai wa Filistiyawa hari; gama a lokacin suna mulkin Isra’ila.)
But his father and his mother knew not that it was from the Lord, that he sought but an occasion against the Philistines; and at that time the Philistines had dominion over Israel.
5 Sai Samson ya gangara zuwa Timna tare da mahaifinsa da kuma mahaifiyarsa. Da suka yi kusa da gonar inabin Timna, nan da nan sai ga ɗan zaki ya taso ya nufe shi yana ruri.
And Samson thus went down, with his father and his mother, to Timnathah; and when they were come as far as the vineyards of Timnathah, behold, a young lion came roaring toward him.
6 Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko masa da ƙarfi, ya sa ya yaga zakin kashi biyu da hannu kamar yadda akan yayyage ɗan akuya. Sai dai bai gaya wa iyayensa abin da ya yi ba.
And the Spirit of the Lord came suddenly over him, and he rent him as he would have rent a kid, and he had nothing in his hand; but he told not his father or his mother what he had done.
7 Sa’an nan ya gangara ya yi magana da yarinyar, yana kuwa sonsa.
And he went down, and spoke unto the woman; and she pleased Samson well.
8 Daga baya, da ya koma don yă aure ta, sai ya ratse don yă ga gawar zakin. Sai ga taron ƙudan zuma da zuma a ciki,
And when he returned after a time to take her, he turned aside to see the carcass of the lion: and, behold, there was a swarm of bees in the carcass of the lion and honey likewise.
9 wanda ya sa hannu ya ɗebo yana tafiya yana sha. Sa’ad da ya iso wurin iyayensa, ya ba su zuman, su ma suka sha. Sai dai bai gaya musu cewa ya ɗebo zuman daga gawar zaki ba.
And he took it out in his hands, and went on, eating as he was going, and came to his father and mother, and he gave unto them, and they did eat; but he told them not that out of the carcass of the lion he had taken the honey.
10 To, mahaifinsa ya gangara don yă ga yarinyar. Samson kuwa ya shirya wata liyafa a can, yadda yake bisa ga al’adar angwaye.
And his father went down unto the woman; and Samson made there a feast; for so used the young men to do.
11 Sa’ad da ya bayyana, sai aka haɗa shi abokai talatin.
And it came to pass, when they saw him, that they brought thirty companions, and they remained with him.
12 Sai Samson ya ce, “Bari in yi muku kacici-kacici, in kun ba ni amsa cikin kwana bakwai na wannan biki, zan ba ku riguna lilin talatin da kuma tufafi talatin.
And Samson said unto them, I will now propound unto you a riddle; if ye can in anywise tell it me within the seven days of the feast, and find it out, then will I give you thirty shirts and thirty changes of garments;
13 In kuma ba ku iya ba ni amsar ba, dole ku ba ni rigunan lilin talatin da tufafi talatin.” Suka ce, “Ka gaya mana kacici-kacicin.”
But if ye will not be able to tell it to me, then shall ye give me thirty shirts and thirty changes of garments. And they said unto him, Propound thy riddle, that we may hear it.
14 Sai ya ce, “Daga mai ci, abinci ya fito; daga mai ƙarfi, abu mai zaki ya fito.” Har kwana uku ba su iya ba da amsa ba.
And he said unto them, Out of the eater came forth food, and out of the strong came forth sweetness. And they could not solve the riddle in three days.
15 A rana ta huɗu suka ce wa matar Samson “Ki rarrashi mijinki yă bayyana mana kacici-kacicin, ko kuwa mu ƙone ki da gidan mahaifinki duka da wuta. Kun kira mu domin ku yi mana fashi ne?”
And it came to pass on the seventh day, that they said unto Samson's wife, Persuade thy husband, that he may solve unto us the riddle, lest we burn thee and thy father's house with fire: have ye invited us to impoverish us? is it not so?
16 Sa’an nan matar Samson ta kwanta masa a jiki tana kuka tana cewa, “Kai maƙiyina ne, lalle ba ka ƙaunata, ka yi wa mutanena kacici-kacici, amma ba ka gaya mini amsar ba.” Ya amsa ya ce, “Ban ma bayyana wa mahaifina ko mahaifiyata ba, to, don me zan bayyana miki?”
And Samson's wife wept before him, and said, Thou doest but hate me, and lovest me not: that riddle hast thou propounded unto the children of my people, and me hast thou not told [the solution]. And he said unto her, Behold, I have not told it to my father and to my mother, and thee shall I tell it?
17 Ta yi ta kuka har kwana bakwai na bikin. Saboda haka a rana ta bakwai sai ya gaya mata, don ta dame shi. Ita kuwa ta bayyana kacici-kacicin wa mutanenta.
And she wept before him the seven days, while their feast lasted; and it came to pass on the seventh day, that he told her, because she had worried him: and she told [the solution of] the riddle to the children of her people.
18 Kafin rana ta fāɗi a rana ta bakwai mutane garin suka ce masa, “Me ya fi zuma zaki? Me ya fi zaki ƙarfi?” Samson ya ce musu, “Da ba don kun haɗa baki da matata ba, da ba za ku san amsar kacici-kacici ba.”
Then said unto him the men of the city on the seventh day before the sun was yet gone down, What is sweeter than honey? and what is stronger than a lion? And he said unto them, If ye had not ploughed with my heifer, ye had not found out my riddle.
19 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko masa da iko. Sai ya fita ya gangara zuwa Ashkelon, ya kashe mutanensu talatin, ya kwashe kayansu ya kuma ba da rigunarsu ga waɗanda suka bayyana kacici-kacicin. Cike da fushi, ya haura zuwa gidan mahaifinsa.
And the Spirit of the Lord came suddenly over him, and he went down to Ashkelon, and slew of them thirty men, and he took their apparel, and gave the changes of garments unto the expounders of the riddle; but his anger was kindled, and he went up to his father's house.
20 Aka kuma ɗauki matar Samson aka ba wa ɗaya daga cikin waɗanda suka yi masa hidima a bikin.
And Samson's wife was given to his companion who had been given him as his associate.