< Mahukunta 13 >

1 Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, saboda haka ya ba da su a hannun Filistiyawa shekara arba’in.
Les enfants d'Israël firent encore ce qui est mal aux yeux de Yahweh, et Yahweh les livra entre les mains des Philistins, pendant quarante ans.
2 Akwai wani mutumin Zora, mai suna Manowa, daga kabilar Dan, matarsa kuwa bakararriya ce, ba ta haihuwa.
Il y avait un homme de Saraa, de la famille des Danites, nommé Manué; sa femme était stérile, et n'avait pas enfanté.
3 Mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare ta ya ce, “Ga shi ke bakararriya ce ba kya haihuwa, amma za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa.
L'Ange de Yahweh apparut à la femme et lui dit: " Voici donc, tu es stérile et sans enfant; mais tu concevras et enfanteras un fils.
4 To, sai ki lura kada ki sha ruwan inabi ko wani abu mai sa maye, kada kuma ki ci wani abu marar tsarki,
Et maintenant, prends bien garde, ne bois ni vin ni liqueur forte et ne mange rien d'impur,
5 gama za ki yi ciki, ki haifi ɗa. Aska ba za tă taɓa kansa ba, domin yaron zai zama Banazare, keɓaɓɓe ga Allah tun daga haihuwa, shi ne kuwa zai soma ceton Isra’ilawa daga hannuwan Filistiyawa.”
car tu vas concevoir et enfanter un fils. Le rasoir ne passera point sur sa tête, car cet enfant sera nazaréen de Dieu, dès le sein de sa mère, et c'est lui qui commencera à délivrer Israël de la main des Philistins. "
6 Sa’an nan matar ta tafi wajen mijinta ta faɗa masa cewa, “Wani mutumin Allah ya zo wurina. Ya yi kama da mala’ikan Allah, yana da bantsoro ƙwarai. Ban tambaye shi inda ya fito ba, kuma bai gaya mini sunansa ba.
La femme alla dire à son mari: " Un homme de Dieu est venu vers moi; il avait l'aspect d'un ange de Dieu, un aspect redoutable. Je ne lui ai pas demandé d'où il était, et il ne m'a pas fait connaître son nom;
7 Sai dai ya ce mini, ‘Za ki yi ciki, ki kuma haifi ɗa. To, fa, kada ki sha ruwan inabi ko abu mai sa maye kada kuma ki ci abin da yake marar tsarki, gama ɗan zai zama Banazare na Allah tun daga haihuwa har ranar mutuwarsa.’”
mais il m'a dit: " Tu vas concevoir et enfanter un fils; et maintenant, ne bois ni vin ni liqueur forte, et ne mange rien d'impur, parce que cet enfant sera nazaréen de Dieu dès le sein de sa mère, jusqu'au jour de sa mort. "
8 Sai Manowa ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, ina roƙonka, bari mutumin Allahn da ka aiko mana yă sāke zuwa don yă koya mana yadda za mu goyi yaron da za a haifa.”
Alors Manué invoqua Yahweh et dit: " Je vous prie, Seigneur, que l'homme de Dieu que vous avez envoyé vienne encore vers nous, et qu'il nous enseigne ce que nous devons faire pour l'enfant qui naîtra! "
9 Allah ya ji Manowa, sai mala’ikan Allah ya sāke zuwa wurin matar yayinda take gona; amma Manowa mijinta ba ya tare da ita.
Dieu exauça la prière de Manué, et l'Ange de Dieu vint encore vers la femme; elle était assise dans un champ, et Manué, son mari, n'était pas avec elle.
10 Sai matar ta ruga don ta faɗa wa mijinta, ta ce, “Ga shi ya zo! Mutumin da ya bayyana mini ran nan!”
La femme courut aussitôt informer son mari et lui dit: " Voici, l'homme qui est venu l'autre jour vers moi m'est apparu. "
11 Manowa ya tashi ya bi matarsa. Da ya zo wurin mutumin, sai ya ce, “Kai ne wanda ka yi magana da matata?” Ya ce, “Ni ne.”
Manué se leva et, suivant sa femme, il alla vers l'homme et lui dit: " Est-ce toi qui as parlé à cette femme? " Il répondit: " C'est moi. "
12 Saboda haka Manowa ya tambaye shi ya ce, “Sa’ad da maganarka ta cika, me za tă zama dokar rayuwar yaron da kuma aikinsa?”
Manué dit: " Maintenant, quand ta parole s'accomplira, que faudra-t-il observer à l'égard de cet enfant, et qu'y aura-t-il à faire pour lui? "
13 Mala’ikan Ubangiji ya ce, “Dole matarka ta kiyaye duk abin da na riga na gaya mata.
L'Ange de Yahweh répondit à Manué: " La femme s'abstiendra de tout ce que je lui ai dit:
14 Kada tă ci kowane iri abin da ya fito daga inabi, ba kuwa za tă sha ruwan inabi, ko abu mai sa maye ko ta ci abu marar tsarki ba. Dole tă kiyaye duk abin da na umarce mata.”
elle ne mangera rien de ce qui provient de la vigne, elle ne boira ni vin ni liqueur forte, et elle ne mangera rien d'impur: tout ce que je lui ai prescrit, elle l'observera. "
15 Manowa ya ce wa mala’ikan Ubangiji, “Muna roƙonka ka jira mu yanka maka ɗan akuya.”
Manué dit à l'Ange de Yahweh: " Permets que nous te retenions et que nous t'apprêtions un chevreau. "
16 Mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ko kun sa na tsaya, ba zan ci abincinku ba. Amma in kun shirya hadaya ta ƙonawa, ku miƙa wa Ubangiji.” (Manowa bai gane cewa mala’ikan Ubangiji ne ba.)
L'Ange de Yahweh répondit à Manué: " Quand tu me retiendrais, je ne mangerais pas de ton mets; mais si tu veux préparer un holocauste, à Yahweh, offre-le. " — Manué ne savait pas que c'était l'Ange de Yahweh —
17 Sa’an nan Manowa ya sāke tambayi mala’ikan Ubangiji ya ce, “Mene ne sunanka, don mu girmama ka sa’ad da maganarka ta tabbata.”
Et Manué dit à l'Ange de Yahweh: " Quel est ton nom, afin que nous t'honorions, quand ta parole s'accomplira? "
18 Ya ce, “Me ya sa kake tambaya sunana? Ai, ya wuce fahimta.”
L'Ange de Yahweh lui répondit: " Pourquoi m'interroges-tu sur mon nom? Il est Merveilleux. "
19 Sa’an nan Manowa ya ɗauki ɗan akuya, tare da hadaya ta hatsi ya miƙa wa Ubangiji a kan dutse. Ubangiji kuwa ya yi abin mamaki yayinda Manowa da matarsa suke kallo.
Manué prit le chevreau avec l'oblation et l'offrit à Yahweh sur le rocher, et Yahweh fit un prodige pendant que Manué et sa femme regardaient.
20 Yayinda harshen wuta ya yi sama daga bagaden, sai mala’ikan Ubangiji ya haura cikin harshen wutar. Da ganin wannan Manowa da matarsa suka fāɗi da fuskokinsu har ƙasa.
Comme la flamme montait de dessus l'autel vers le ciel, l'Ange de Yahweh monta dans la flamme de l'autel. A cette vue, Manué et sa femme tombèrent la face contre terre.
21 Da mala’ikan Ubangiji bai ƙara bayyana kansa ga Manowa da matarsa ba, sai Manowa ya gane cewa mala’ikan Ubangiji ne.
Et l'Ange de Yahweh n'apparut plus à Manué et à sa femme. Alors Manué comprit que c'était l'Ange de Yahweh.
22 Ya ce wa matar, “Ba shakka za mu mutu, gama mun ga Allah!”
Et Manué dit à sa femme: " Nous allons mourir, car nous avons vu Dieu. "
23 Amma matar ta ce, “Da Ubangiji yana nufin kashe mu ne, da ba zai karɓi hadaya ta ƙonawa da hadaya ta hatsi daga hannunmu, ko yă nuna mana dukan waɗannan abubuwa ko abin da ya gaya mana ba.”
Sa femme lui répondit: " Si Yahweh voulait nous faire mourir, il n'aurait pas reçu de nos mains l'holocauste et l'oblation, il ne nous aurait pas fait voir tout cela, il ne nous aurait pas fait entendre aujourd'hui de pareilles choses. "
24 Matar kuwa ta haifi ɗa, aka sa masa suna Samson. Ya yi girma Ubangiji kuma ya albarkace shi,
La femme enfanta un fils et lui donna le nom de Samson. L'enfant grandit et Yahweh le bénit;
25 Ruhun Ubangiji kuwa ya fara iza shi yayinda yake a Mahane Dan, tsakanin Zora da Eshtawol.
l'esprit de Yahweh commença à le pousser à Machanêh-Dan, entre Saraa et Esthaol.

< Mahukunta 13 >