< Mahukunta 13 >

1 Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, saboda haka ya ba da su a hannun Filistiyawa shekara arba’in.
And the sons of Israel again did the thing that was wicked in the sight of Yahweh, —so Yahweh delivered them up into the hand of the Philistines, forty years.
2 Akwai wani mutumin Zora, mai suna Manowa, daga kabilar Dan, matarsa kuwa bakararriya ce, ba ta haihuwa.
And there was a certain man of Zorah, of the family of the Danites, and, his name, was Manoah; and, his wife, was barren, and had borne no child.
3 Mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare ta ya ce, “Ga shi ke bakararriya ce ba kya haihuwa, amma za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa.
And the messenger of Yahweh appeared unto the woman, —and said unto her—Lo! I pray thee, thou, art barren, and hast borne no child, but thou shalt conceive, and shalt bear a son.
4 To, sai ki lura kada ki sha ruwan inabi ko wani abu mai sa maye, kada kuma ki ci wani abu marar tsarki,
Now, therefore, beware, I pray thee, and do not drink wine or strong drink, —nor eat anything unclean;
5 gama za ki yi ciki, ki haifi ɗa. Aska ba za tă taɓa kansa ba, domin yaron zai zama Banazare, keɓaɓɓe ga Allah tun daga haihuwa, shi ne kuwa zai soma ceton Isra’ilawa daga hannuwan Filistiyawa.”
for lo! thou, art about to conceive and bear a son, and no, razor, shall come on his head, for, one separate unto God, shall the boy be from his birth, —and, he, shall begin to save Israel out of the hand of the Philistines.
6 Sa’an nan matar ta tafi wajen mijinta ta faɗa masa cewa, “Wani mutumin Allah ya zo wurina. Ya yi kama da mala’ikan Allah, yana da bantsoro ƙwarai. Ban tambaye shi inda ya fito ba, kuma bai gaya mini sunansa ba.
So the woman came in, and told her husband, saying, A man of God, came unto me, and, his, appearance, was as the appearance of the messenger of God, reverend exceedingly, —and I asked him not whence he was, and, his name, he told me not.
7 Sai dai ya ce mini, ‘Za ki yi ciki, ki kuma haifi ɗa. To, fa, kada ki sha ruwan inabi ko abu mai sa maye kada kuma ki ci abin da yake marar tsarki, gama ɗan zai zama Banazare na Allah tun daga haihuwa har ranar mutuwarsa.’”
But he said unto me, Lo! thou art about to conceive, and bear a son, —now, therefore, do not drink wine or strong drink, nor eat anything unclean, for, one separate unto God, shall the boy be, from his birth until the day of his death.
8 Sai Manowa ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, ina roƙonka, bari mutumin Allahn da ka aiko mana yă sāke zuwa don yă koya mana yadda za mu goyi yaron da za a haifa.”
Then Manoah made entreaty unto Yahweh, and said: Pardon, O My Lord! the man of God whom thou didst send, I pray thee, let him come again unto us, that he may teach us what we are to do, unto the boy that is to be born.
9 Allah ya ji Manowa, sai mala’ikan Allah ya sāke zuwa wurin matar yayinda take gona; amma Manowa mijinta ba ya tare da ita.
And God hearkened unto the voice of Manoah, —and the messenger of God came again unto the woman, as, she, was sitting in the field, Manoah her husband, not being with her.
10 Sai matar ta ruga don ta faɗa wa mijinta, ta ce, “Ga shi ya zo! Mutumin da ya bayyana mini ran nan!”
So the woman made haste, and ran, and told her husband, —and said unto him, Lo! the man, hath appeared unto me, who came the other day unto me.
11 Manowa ya tashi ya bi matarsa. Da ya zo wurin mutumin, sai ya ce, “Kai ne wanda ka yi magana da matata?” Ya ce, “Ni ne.”
Then Manoah arose, and followed his wife, —and came unto the man, and said unto him—Art, thou, the man that spake unto the wife? And he said—I am.
12 Saboda haka Manowa ya tambaye shi ya ce, “Sa’ad da maganarka ta cika, me za tă zama dokar rayuwar yaron da kuma aikinsa?”
And Manoah said, Now, let thy words come to pass, —What shall be the rule for the boy, and his work?
13 Mala’ikan Ubangiji ya ce, “Dole matarka ta kiyaye duk abin da na riga na gaya mata.
And the messenger of Yahweh said unto Manoah, —Of all that I said unto the woman, let her beware.
14 Kada tă ci kowane iri abin da ya fito daga inabi, ba kuwa za tă sha ruwan inabi, ko abu mai sa maye ko ta ci abu marar tsarki ba. Dole tă kiyaye duk abin da na umarce mata.”
Of nothing that cometh of the vine, may she eat, nor wine nor strong drink, let her drink, nor, anything unclean, let her eat, —all that I commanded her, let her observe.
15 Manowa ya ce wa mala’ikan Ubangiji, “Muna roƙonka ka jira mu yanka maka ɗan akuya.”
And Manoah said unto the messenger of Yahweh, —I pray thee, let us detain thee, that we may make ready for thy presence, a kid.
16 Mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ko kun sa na tsaya, ba zan ci abincinku ba. Amma in kun shirya hadaya ta ƙonawa, ku miƙa wa Ubangiji.” (Manowa bai gane cewa mala’ikan Ubangiji ne ba.)
But the messenger of Yahweh said unto Manoah—Though thou detain me, yet will I not eat of thy food, and, though thou make ready an ascending-sacrifice, unto Yahweh, must thou cause it to ascend. For Manoah had not discerned that, the angel of Yahweh, he was.
17 Sa’an nan Manowa ya sāke tambayi mala’ikan Ubangiji ya ce, “Mene ne sunanka, don mu girmama ka sa’ad da maganarka ta tabbata.”
Then said Manoah unto the messenger of Yahweh, What is thy name, —that, when thy word cometh to pass, we may do thee honour?
18 Ya ce, “Me ya sa kake tambaya sunana? Ai, ya wuce fahimta.”
And the messenger of Yahweh said unto him, Wherefore is it, that thou shouldst ask after my name, —seeing that, it, is Wonderful?
19 Sa’an nan Manowa ya ɗauki ɗan akuya, tare da hadaya ta hatsi ya miƙa wa Ubangiji a kan dutse. Ubangiji kuwa ya yi abin mamaki yayinda Manowa da matarsa suke kallo.
So Manoah took the kid, and the meal-offering, and caused them to ascend upon the rock unto Yahweh, who was about to do, wondrously, while Manoah and his wife were looking on.
20 Yayinda harshen wuta ya yi sama daga bagaden, sai mala’ikan Ubangiji ya haura cikin harshen wutar. Da ganin wannan Manowa da matarsa suka fāɗi da fuskokinsu har ƙasa.
And it came to pass, when the flame ascended from off the altar, towards the heavens, that the messenger of Yahweh ascended in the flame of the altar, —while Manoah and his wife were looking on. Then fell they on their faces, to the earth.
21 Da mala’ikan Ubangiji bai ƙara bayyana kansa ga Manowa da matarsa ba, sai Manowa ya gane cewa mala’ikan Ubangiji ne.
And the messenger of Yahweh did no more appear unto Manoah or unto his wife. Then, Manoah knew that, the messenger of Yahweh, he was.
22 Ya ce wa matar, “Ba shakka za mu mutu, gama mun ga Allah!”
And Manoah said unto his wife, We shall, die, —for, upon God, have we looked.
23 Amma matar ta ce, “Da Ubangiji yana nufin kashe mu ne, da ba zai karɓi hadaya ta ƙonawa da hadaya ta hatsi daga hannunmu, ko yă nuna mana dukan waɗannan abubuwa ko abin da ya gaya mana ba.”
But his wife said unto him, If Yahweh had been pleased to put us to death, he would not have received at our hand, an ascending-sacrifice and a meal-offering, nor would he have shewed us all these things, —and, at such a time, have let us hear the like of this!
24 Matar kuwa ta haifi ɗa, aka sa masa suna Samson. Ya yi girma Ubangiji kuma ya albarkace shi,
So the woman bare a son, and called his name Samson, —and the boy grew, and Yahweh blessed him.
25 Ruhun Ubangiji kuwa ya fara iza shi yayinda yake a Mahane Dan, tsakanin Zora da Eshtawol.
And the spirit of Yahweh began to urge him to and fro, in the camp of Dan, —between Zorah and Eshtaol.

< Mahukunta 13 >