< Mahukunta 13 >

1 Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, saboda haka ya ba da su a hannun Filistiyawa shekara arba’in.
Og Israels Børn bleve ved at gøre det, som var ondt for Herrens Øjne, og Herren gav dem i Filisternes Haand fyrretyve Aar.
2 Akwai wani mutumin Zora, mai suna Manowa, daga kabilar Dan, matarsa kuwa bakararriya ce, ba ta haihuwa.
Og der var en Mand fra Zora, af en Daniters Slægt, og hans Navn var Manoa; og hans Hustru var ufrugtbar og fødte ikke.
3 Mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare ta ya ce, “Ga shi ke bakararriya ce ba kya haihuwa, amma za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa.
Og Herrens Engel aabenbaredes for Kvinden, og han sagde til hende: Se, kære, du er ufrugtbar og føder ikke, men du skal blive frugtsommelig og føde en Søn.
4 To, sai ki lura kada ki sha ruwan inabi ko wani abu mai sa maye, kada kuma ki ci wani abu marar tsarki,
Saa, kære, forvar dig nu, at du ikke drikker Vin ej heller stærk Drik, og at du ikke æder noget urent.
5 gama za ki yi ciki, ki haifi ɗa. Aska ba za tă taɓa kansa ba, domin yaron zai zama Banazare, keɓaɓɓe ga Allah tun daga haihuwa, shi ne kuwa zai soma ceton Isra’ilawa daga hannuwan Filistiyawa.”
Thi se, du skal vorde frugtsommelig og føde en Søn, og paa hans Hoved skal ikke komme Bagekniv; thi Drengen skal være en Guds Nasiræer fra Moders Liv af, og han skal begynde at frelse Israel af Filisternes Haand.
6 Sa’an nan matar ta tafi wajen mijinta ta faɗa masa cewa, “Wani mutumin Allah ya zo wurina. Ya yi kama da mala’ikan Allah, yana da bantsoro ƙwarai. Ban tambaye shi inda ya fito ba, kuma bai gaya mini sunansa ba.
Da kom Kvinden og sagde til sin Mand: Der kom en Guds Mand til mig, og hans Udseende var som en Guds Engels Udseende, saare forfærdelig; og jeg spurgte ham ikke, hvorfra han var, og han kundgjorde mig ikke sit Navn.
7 Sai dai ya ce mini, ‘Za ki yi ciki, ki kuma haifi ɗa. To, fa, kada ki sha ruwan inabi ko abu mai sa maye kada kuma ki ci abin da yake marar tsarki, gama ɗan zai zama Banazare na Allah tun daga haihuwa har ranar mutuwarsa.’”
Men han sagde til mig: Se, du skal vorde frugtsommelig og føde en Søn; saa skal du nu ikke drikke Vin eller stærk Drik og ikke æde noget urent; thi Drengen skal være en Guds Nasiræer fra Moders Liv af indtil sin Dødsdag.
8 Sai Manowa ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, ina roƙonka, bari mutumin Allahn da ka aiko mana yă sāke zuwa don yă koya mana yadda za mu goyi yaron da za a haifa.”
Da bad Manoa til Herren og sagde: Hør mig, Herre! Kære, lad den Guds Mand, som du udsendte, atter komme til os, at han kan lære os, hvad vi skulle gøre ved Drengen, som skal fødes.
9 Allah ya ji Manowa, sai mala’ikan Allah ya sāke zuwa wurin matar yayinda take gona; amma Manowa mijinta ba ya tare da ita.
Og Gud hørte Manoas Bøst; og Guds Engel kom atter til Kvinden, og hun sad paa Marken; men hendes Mand Manoa var ikke hos hende.
10 Sai matar ta ruga don ta faɗa wa mijinta, ta ce, “Ga shi ya zo! Mutumin da ya bayyana mini ran nan!”
Da hastede Kvinden og løb og gav sin Mand det til Kende, og hun sagde til ham: Se, den Mand, der kom til mig hin Dag, aabenbaredes for mig.
11 Manowa ya tashi ya bi matarsa. Da ya zo wurin mutumin, sai ya ce, “Kai ne wanda ka yi magana da matata?” Ya ce, “Ni ne.”
Da stod Manoa op og gik efter sin Hustru, og han kom til Manden og sagde til ham: Er du den Mand, som talede med Kvinden? og han sagde: Ja, jeg er.
12 Saboda haka Manowa ya tambaye shi ya ce, “Sa’ad da maganarka ta cika, me za tă zama dokar rayuwar yaron da kuma aikinsa?”
Og Manoa sagde: Naar det nu kommer, som du har sagt, hvad skulle vi iagttage med Drengen, og hvad skulle vi gøre ved ham?
13 Mala’ikan Ubangiji ya ce, “Dole matarka ta kiyaye duk abin da na riga na gaya mata.
Og Herrens Engel sagde til Manoa: For alt det, som jeg har sagt til Kvinden, skal hun tage sig i Vare.
14 Kada tă ci kowane iri abin da ya fito daga inabi, ba kuwa za tă sha ruwan inabi, ko abu mai sa maye ko ta ci abu marar tsarki ba. Dole tă kiyaye duk abin da na umarce mata.”
Hun skal ikke æde af noget, som kommer af Vinstokken, og ikke drikke Vin eller stærk Drik og intet urent æde; alt det, som jeg har budet hende, skal hun holde.
15 Manowa ya ce wa mala’ikan Ubangiji, “Muna roƙonka ka jira mu yanka maka ɗan akuya.”
Og Manoa sagde til Herrens Engel: Kære, lad os opholde dig lidt, saa ville vi lave et Bukkekid for dit Ansigt.
16 Mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ko kun sa na tsaya, ba zan ci abincinku ba. Amma in kun shirya hadaya ta ƙonawa, ku miƙa wa Ubangiji.” (Manowa bai gane cewa mala’ikan Ubangiji ne ba.)
Men Herrens Engel sagde til Manoa: Dersom du opholder mig, æder jeg dog ikke af din Mad, men dersom du vil gøre dit Brændoffer, maa du ofre Herren det; thi Manoa vidste ikke, at det var Herrens Engel.
17 Sa’an nan Manowa ya sāke tambayi mala’ikan Ubangiji ya ce, “Mene ne sunanka, don mu girmama ka sa’ad da maganarka ta tabbata.”
Og Manoa sagde til Herrens Engel: Hvad er dit Navn, at vi kunne ære dig, naar det kommer, som du har sagt.
18 Ya ce, “Me ya sa kake tambaya sunana? Ai, ya wuce fahimta.”
Og Herrens Engel sagde til ham: Hvi spørger du om mit Navn? se, det er underligt.
19 Sa’an nan Manowa ya ɗauki ɗan akuya, tare da hadaya ta hatsi ya miƙa wa Ubangiji a kan dutse. Ubangiji kuwa ya yi abin mamaki yayinda Manowa da matarsa suke kallo.
Da tog Manoa et Bukkekid og Madofret og ofrede det for Herren paa Klippen; og Engelen gjorde et Under, men Manoa og hans Hustru saa til.
20 Yayinda harshen wuta ya yi sama daga bagaden, sai mala’ikan Ubangiji ya haura cikin harshen wutar. Da ganin wannan Manowa da matarsa suka fāɗi da fuskokinsu har ƙasa.
Og det skete, der Luen for op fra Alteret til Himmelen, da for Herrens Engel op i Luen fra Alteret; der Manoa og hans Hustru saa det, da faldt de paa deres Ansigt til Jorden.
21 Da mala’ikan Ubangiji bai ƙara bayyana kansa ga Manowa da matarsa ba, sai Manowa ya gane cewa mala’ikan Ubangiji ne.
Og Herrens Engel lod sig ikke ydermere se for Manoa og for hans Hustru; da fornam Manoa, at det var Herrens Engel.
22 Ya ce wa matar, “Ba shakka za mu mutu, gama mun ga Allah!”
Og Manoa sagde til sin Hustru: Vi dø visseligen; thi vi have set Gud.
23 Amma matar ta ce, “Da Ubangiji yana nufin kashe mu ne, da ba zai karɓi hadaya ta ƙonawa da hadaya ta hatsi daga hannunmu, ko yă nuna mana dukan waɗannan abubuwa ko abin da ya gaya mana ba.”
Men hans Hustru sagde til ham: Om Herren havde haft Lyst til at ihjelslaa os, havde han ikke taget Brændoffer og Madoffer af vor Haand, ej heller ladet os se alt dette og paa denne Tid ej ladet os høre saadanne Ting.
24 Matar kuwa ta haifi ɗa, aka sa masa suna Samson. Ya yi girma Ubangiji kuma ya albarkace shi,
Og Kvinden fødte en Søn og kaldte hans Navn Samson; og Drengen blev stor, og Herren velsignede ham.
25 Ruhun Ubangiji kuwa ya fara iza shi yayinda yake a Mahane Dan, tsakanin Zora da Eshtawol.
Og Herrens Aand begyndte at drive ham i Dans Lejr imellem Zora og Esthaol.

< Mahukunta 13 >