< Mahukunta 13 >

1 Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji, saboda haka ya ba da su a hannun Filistiyawa shekara arba’in.
Tedy opět synové Izraelští činili to, což jest zlého před očima Hospodinovýma, i vydal je Hospodin v ruce Filistinských za čtyřidceti let.
2 Akwai wani mutumin Zora, mai suna Manowa, daga kabilar Dan, matarsa kuwa bakararriya ce, ba ta haihuwa.
Byl pak muž jeden z Zaraha, z čeledi Dan, jménem Manue, jehož manželka byla neplodná a nerodila.
3 Mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare ta ya ce, “Ga shi ke bakararriya ce ba kya haihuwa, amma za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa.
I ukázal se anděl Hospodinův ženě té a řekl jí: Aj, nyní jsi neplodná, aniž jsi rodila; počneš pak a porodíš syna.
4 To, sai ki lura kada ki sha ruwan inabi ko wani abu mai sa maye, kada kuma ki ci wani abu marar tsarki,
Protož nyní vystříhej se, abys vína nepila aneb nápoje opojného, a abys nejedla nic nečistého.
5 gama za ki yi ciki, ki haifi ɗa. Aska ba za tă taɓa kansa ba, domin yaron zai zama Banazare, keɓaɓɓe ga Allah tun daga haihuwa, shi ne kuwa zai soma ceton Isra’ilawa daga hannuwan Filistiyawa.”
Nebo aj, počneš a porodíš syna, a břitva ať nevchází na hlavu jeho, nebo bude to dítě od života Nazarejský Boží, a tenť počne vysvobozovati Izraele z ruky Filistinských.
6 Sa’an nan matar ta tafi wajen mijinta ta faɗa masa cewa, “Wani mutumin Allah ya zo wurina. Ya yi kama da mala’ikan Allah, yana da bantsoro ƙwarai. Ban tambaye shi inda ya fito ba, kuma bai gaya mini sunansa ba.
I přišla žena a pověděla to muži svému, řkuci: Muž Boží přišel ke mně, jehož oblíčej byl jako oblíčej anděla Božího, hrozný velmi, a neotázala jsem se jeho, odkud by byl, ani mi svého jména neoznámil.
7 Sai dai ya ce mini, ‘Za ki yi ciki, ki kuma haifi ɗa. To, fa, kada ki sha ruwan inabi ko abu mai sa maye kada kuma ki ci abin da yake marar tsarki, gama ɗan zai zama Banazare na Allah tun daga haihuwa har ranar mutuwarsa.’”
Ale řekl mi: Aj, počneš a porodíš syna, protož nyní nepí vína aneb nápoje opojného, aniž jez co nečistého, nebo to dítě od života bude Nazarejský Boží až do dne smrti své.
8 Sai Manowa ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, ina roƙonka, bari mutumin Allahn da ka aiko mana yă sāke zuwa don yă koya mana yadda za mu goyi yaron da za a haifa.”
Tedy Manue modlil se Hospodinu a řekl: Vyslyš mne, můj Pane, prosím, nechť muž Boží, kteréhož jsi byl poslal, zase přijde k nám, a naučí nás, co máme dělati s dítětem, kteréž se má naroditi.
9 Allah ya ji Manowa, sai mala’ikan Allah ya sāke zuwa wurin matar yayinda take gona; amma Manowa mijinta ba ya tare da ita.
I vyslyšel Bůh hlas Manue; nebo přišel anděl Boží opět k ženě té, když seděla na poli. Manue pak muž její nebyl s ní.
10 Sai matar ta ruga don ta faɗa wa mijinta, ta ce, “Ga shi ya zo! Mutumin da ya bayyana mini ran nan!”
A protož s chvátáním běžela žena ta, a oznámila muži svému, řkuci jemu: Hle, ukázal se mi muž ten, kterýž byl ke mně prvé přišel.
11 Manowa ya tashi ya bi matarsa. Da ya zo wurin mutumin, sai ya ce, “Kai ne wanda ka yi magana da matata?” Ya ce, “Ni ne.”
Vstav pak Manue, šel za manželkou svou, a přišed k muži tomu, řekl jemu: Ty-li jsi ten muž, kterýž jsi mluvil k manželce mé? Odpověděl: Jsem.
12 Saboda haka Manowa ya tambaye shi ya ce, “Sa’ad da maganarka ta cika, me za tă zama dokar rayuwar yaron da kuma aikinsa?”
I řekl Manue: Nechť se nyní stane slovo tvé, ale jaká péče o to dítě a správa při něm býti má?
13 Mala’ikan Ubangiji ya ce, “Dole matarka ta kiyaye duk abin da na riga na gaya mata.
Odpověděl anděl Hospodinův Manue: Ode všeho toho, o čemž jsem oznámil ženě, ať se ona vystříhá.
14 Kada tă ci kowane iri abin da ya fito daga inabi, ba kuwa za tă sha ruwan inabi, ko abu mai sa maye ko ta ci abu marar tsarki ba. Dole tă kiyaye duk abin da na umarce mata.”
Ničeho, což pochází z vinného kmene, ať neužívá, to jest, vína aneb nápoje opojného ať nepije, a nic nečistého ať nejí; cožkoli jsem jí přikázal, ať ostříhá.
15 Manowa ya ce wa mala’ikan Ubangiji, “Muna roƙonka ka jira mu yanka maka ɗan akuya.”
Tedy řekl Manue andělu Hospodinovu: Medle, nechť tě pozdržíme, a připravímeť kozlíka.
16 Mala’ikan Ubangiji ya ce, “Ko kun sa na tsaya, ba zan ci abincinku ba. Amma in kun shirya hadaya ta ƙonawa, ku miƙa wa Ubangiji.” (Manowa bai gane cewa mala’ikan Ubangiji ne ba.)
I odpověděl anděl Hospodinův Manue: Bys mne i pozdržel, nebuduť jísti pokrmu tvého, ale jestliže připravíš obět zápalnou, Hospodinu ji obětuj. Nebo nevěděl Manue, že byl anděl Hospodinův.
17 Sa’an nan Manowa ya sāke tambayi mala’ikan Ubangiji ya ce, “Mene ne sunanka, don mu girmama ka sa’ad da maganarka ta tabbata.”
Řekl opět Manue andělu Hospodinovu: Jaké jest jméno tvé, abychom, když se naplní řeč tvá, poctili tebe?
18 Ya ce, “Me ya sa kake tambaya sunana? Ai, ya wuce fahimta.”
Jemuž odpověděl anděl Hospodinův: Proč se ptáš na jméno mé, kteréž jest divné?
19 Sa’an nan Manowa ya ɗauki ɗan akuya, tare da hadaya ta hatsi ya miƙa wa Ubangiji a kan dutse. Ubangiji kuwa ya yi abin mamaki yayinda Manowa da matarsa suke kallo.
Vzav tedy Manue kozlíka a obět suchou, obětoval to na skále Hospodinu, a on divnou věc učinil, an na to hledí Manue a manželka jeho.
20 Yayinda harshen wuta ya yi sama daga bagaden, sai mala’ikan Ubangiji ya haura cikin harshen wutar. Da ganin wannan Manowa da matarsa suka fāɗi da fuskokinsu har ƙasa.
Nebo když vstupoval plamen s oltáře k nebi, vznesl se anděl Hospodinův v plameni s oltáře, Manue pak a manželka jeho vidouce to, padli na tvář svou na zemi.
21 Da mala’ikan Ubangiji bai ƙara bayyana kansa ga Manowa da matarsa ba, sai Manowa ya gane cewa mala’ikan Ubangiji ne.
A již se více neukázal anděl Hospodinův Manue ani manželce jeho. Tedy porozuměl Manue, že byl anděl Hospodinův.
22 Ya ce wa matar, “Ba shakka za mu mutu, gama mun ga Allah!”
I řekl Manue manželce své: Jistě my zemřeme, nebo jsme Boha viděli.
23 Amma matar ta ce, “Da Ubangiji yana nufin kashe mu ne, da ba zai karɓi hadaya ta ƙonawa da hadaya ta hatsi daga hannunmu, ko yă nuna mana dukan waɗannan abubuwa ko abin da ya gaya mana ba.”
Jemuž odpověděla manželka jeho: Kdyby nás chtěl Hospodin usmrtiti, nebyl by přijal z rukou našich oběti zápalné a suché, aniž by nám byl ukázal čeho toho, aniž by na tento čas byl nám ohlásil věcí takových.
24 Matar kuwa ta haifi ɗa, aka sa masa suna Samson. Ya yi girma Ubangiji kuma ya albarkace shi,
A tak žena ta porodila syna a nazvala jméno jeho Samson. I rostlo dítě, a žehnal jemu Hospodin.
25 Ruhun Ubangiji kuwa ya fara iza shi yayinda yake a Mahane Dan, tsakanin Zora da Eshtawol.
I počal ho Duch Hospodinův ponoukati v Mahane Dan, mezi Zaraha a Estaol.

< Mahukunta 13 >