< Mahukunta 12 >

1 Mutanen Efraim suka tattaro mayaƙansu, suka haye zuwa Zafon suka cewa Yefta, “Don me ka tafi ka yaƙi Ammonawa ba ka gayyace mu ba? Za mu ƙone gidanka a kanka.”
And the men of Ephraim are called together, and pass over northward, and say to Jephthah, 'Wherefore has thou passed over to fight against the Bene-Ammon, and on us hast not called to go with thee? thy house we burn over thee with fire.'
2 Yefta ya ce, “Ni da mutanena mun yi ta jayayya sosai da Ammonawa, ko da yake na kira ku, amma ba ku cece ni daga hannuwansu ba.
And Jephthah saith unto them, 'A man of great strife I have been (I and my people) with the Bene-Ammon, and I call you, and ye have not saved me out of their hand,
3 Da na ga ba za ku taimake ni ba, sai na yi kasai da raina na kuwa haye don in yaƙi Ammonawa, Ubangiji kuwa ya ba ni nasara a kansu. To, don me kuka zo yau don ku yaƙe ni?”
and I see that thou art not a saviour, and I put my life in my hand, and pass over unto the Bene-Ammon, and Jehovah giveth them into my hand — and why have ye come up unto me this day to fight against me?'
4 Sa’an nan Yefta ya tara mutanen Gileyad wuri guda ya kuma yaƙi Efraim. Mutanen Gileyad suka fatattake su domin mutanen Efraim sun ce, “Ku Mutanen Gileyad masu neman mafaka ne cikin Efraim da Manasse.”
And Jephthah gathered all the men of Gilead, and fighteth with Ephraim, and the men of Gilead smite Ephraim, because they said, 'Fugitives of Ephraim [are] ye Gileadites, in the midst of Ephraim — in the midst of Manasseh.'
5 Mutanen Gileyad suka ƙwace mashigan Urdun masu zuwa Efraim, duk sa’ad da wani daga Efraim da ya tsira ya ce, “Bari in haye,” sai mutane Gileyad su ce “Kai mutumin Efraim ne?” In ya ce, “A’a,”
And Gilead captureth the passages of the Jordan to Ephraim, and it hath been, when [any of] the fugitives of Ephraim say, 'Let me pass over,' and the men of Gilead say to him, 'An Ephramite thou?' and he saith, 'No;'
6 sai su ce, “To, ka ce, ‘Shibbolet.’” In ya ce, “Sibbolet,” saboda ba sa iya faɗin kalmar daidai, sai su kama shi su kashe a mashigan Urdun. Aka kashe mutanen Efraim dubu arba’in da biyu a ta haka.
that they say to him, 'Say, I pray thee, Shibboleth;' and he saith, 'Sibboleth,' and is not prepared to speak right — and they seize him, and slaughter him at the passages of the Jordan, and there fall at that time, of Ephraim, forty and two chiefs.
7 Yefta ya shugabanci Isra’ila shekara shida. Sa’an nan Yefta mutumin Gileyad ya mutu, aka kuwa binne shi wani gari a Gileyad.
And Jephthah judged Israel six years, and Jephthah the Gileadite dieth, and is buried in [one of] the cities of Gilead.
8 Bayansa, Ibzan mutumin Betlehem, ya shugabanci Isra’ila.
And after him Ibzan of Beth-Lehem judgeth Israel,
9 Yana’ya’ya maza talatin da’ya’ya mata talatin. Ya ba da auren’ya’yansa mata ga waɗanda ba daga dangi ba, ga’ya’yansa maza kuwa ya kawo’yan mata talatin su zama matansu waje da danginsa. Ibzan ya shugabanci Isra’ila shekara bakwai.
and he hath thirty sons and thirty daughters, he hath sent without and thirty daughters hath brought in to his sons from without; and he judgeth Israel seven years.
10 Sa’an nan Ibzan ya mutu, aka kuwa binne shi Betlehem.
And Ibzan dieth, and is buried in Beth-Lehem.
11 Bayansa, Elon mutumin Zebulun, ya shugabanci Isra’ila shekara goma.
And after him Elon the Zebulunite judgeth Israel, and he judgeth Israel ten years,
12 Sa’an nan Elon ya mutu, aka kuwa binne shi a Aiyalon a ƙasar Zebulun.
and Elon the Zebulunite dieth, and is buried in Aijalon, in the land of Zebulun.
13 Bayansa, Abdon ɗan Hillel, daga Firaton, ya shugabanci Isra’ila.
And after him, Abdon son of Hillel, the Pirathonite, judgeth Israel,
14 Yana da’ya’ya maza arba’in da’yan taɓa kunne talatin, waɗanda suka hau jakuna saba’in. Ya shugabanci Isra’ila shekara takwas.
and he hath forty sons, and thirty grandsons, riding on seventy ass-colts, and he judgeth Israel eight years.
15 Sa’an nan Abdon ɗan Hillel ya mutu, aka kuwa binne shi a Firaton a Efraim, a ƙasar tudu ta Amalekawa.
And Abdon son of Hillel, the Pirathonite, dieth, and is buried in Pirathon, in the land of Ephraim, in the hill-country of the Amalekite.

< Mahukunta 12 >