< Mahukunta 12 >
1 Mutanen Efraim suka tattaro mayaƙansu, suka haye zuwa Zafon suka cewa Yefta, “Don me ka tafi ka yaƙi Ammonawa ba ka gayyace mu ba? Za mu ƙone gidanka a kanka.”
A call went out to the men of Ephraim; they passed through Zaphon and said to Jephthah, “Why did you pass through to fight against the people of Ammon and did not call us to go with you? We will burn your house down over you.”
2 Yefta ya ce, “Ni da mutanena mun yi ta jayayya sosai da Ammonawa, ko da yake na kira ku, amma ba ku cece ni daga hannuwansu ba.
Jephthah said to them, “I and my people were in a great conflict with the people of Ammon. When I called you, you did not rescue me from them.
3 Da na ga ba za ku taimake ni ba, sai na yi kasai da raina na kuwa haye don in yaƙi Ammonawa, Ubangiji kuwa ya ba ni nasara a kansu. To, don me kuka zo yau don ku yaƙe ni?”
When I saw that you did not rescue me, When I saw that you did not rescue me, I put my life in my own hand and passed through against the people of Ammon, and Yahweh gave me victory. Why have you come to fight against me today?”
4 Sa’an nan Yefta ya tara mutanen Gileyad wuri guda ya kuma yaƙi Efraim. Mutanen Gileyad suka fatattake su domin mutanen Efraim sun ce, “Ku Mutanen Gileyad masu neman mafaka ne cikin Efraim da Manasse.”
Jephthah gathered together all the men of Gilead and he fought against Ephraim. The men of Gilead attacked the men of Ephraim because they said, “You Gileadites are fugitives in Ephraim—in Ephraim and Manasseh.”
5 Mutanen Gileyad suka ƙwace mashigan Urdun masu zuwa Efraim, duk sa’ad da wani daga Efraim da ya tsira ya ce, “Bari in haye,” sai mutane Gileyad su ce “Kai mutumin Efraim ne?” In ya ce, “A’a,”
The Gileadites captured the fords of the Jordan leading to Ephraim. When any of the survivors of Ephraim said, “Let me go over the river,” the men of Gilead would say to him, “Are you an Ephraimite?” If he said, “No,”
6 sai su ce, “To, ka ce, ‘Shibbolet.’” In ya ce, “Sibbolet,” saboda ba sa iya faɗin kalmar daidai, sai su kama shi su kashe a mashigan Urdun. Aka kashe mutanen Efraim dubu arba’in da biyu a ta haka.
then they would say to him, “Say: Shibboleth,” and if he said “Sibboleth” (for he could not pronounce the word correctly), the Gileadites would seize him and kill him at the fords of the Jordan. Forty-two thousand Ephraimites were killed at that time.
7 Yefta ya shugabanci Isra’ila shekara shida. Sa’an nan Yefta mutumin Gileyad ya mutu, aka kuwa binne shi wani gari a Gileyad.
Jephthah served as a judge over Israel for six years. Then Jephthah the Gileadite died and was buried in one of the cities of Gilead.
8 Bayansa, Ibzan mutumin Betlehem, ya shugabanci Isra’ila.
After him, Ibzan of Bethlehem served as a judge over Israel.
9 Yana’ya’ya maza talatin da’ya’ya mata talatin. Ya ba da auren’ya’yansa mata ga waɗanda ba daga dangi ba, ga’ya’yansa maza kuwa ya kawo’yan mata talatin su zama matansu waje da danginsa. Ibzan ya shugabanci Isra’ila shekara bakwai.
He had thirty sons. He gave away thirty daughters in marriage, and he brought in thirty daughters of other men for his sons, from the outside. He judged Israel for seven years.
10 Sa’an nan Ibzan ya mutu, aka kuwa binne shi Betlehem.
Ibzan died and was buried at Bethlehem.
11 Bayansa, Elon mutumin Zebulun, ya shugabanci Isra’ila shekara goma.
After him Elon the Zebulunite served as judge over Israel. He judged Israel for ten years.
12 Sa’an nan Elon ya mutu, aka kuwa binne shi a Aiyalon a ƙasar Zebulun.
Elon the Zebulunite died and was buried in Aijalon in the land of Zebulun.
13 Bayansa, Abdon ɗan Hillel, daga Firaton, ya shugabanci Isra’ila.
After him, Abdon son of Hillel the Pirathonite served as a judge over Israel.
14 Yana da’ya’ya maza arba’in da’yan taɓa kunne talatin, waɗanda suka hau jakuna saba’in. Ya shugabanci Isra’ila shekara takwas.
He had forty sons and thirty grandsons. They rode on seventy donkeys, and he judged Israel for eight years.
15 Sa’an nan Abdon ɗan Hillel ya mutu, aka kuwa binne shi a Firaton a Efraim, a ƙasar tudu ta Amalekawa.
Abdon son of Hillel the Pirathonite died and was buried in Pirathon in the land of Ephraim in the hill country of the Amalekites.