< Mahukunta 12 >

1 Mutanen Efraim suka tattaro mayaƙansu, suka haye zuwa Zafon suka cewa Yefta, “Don me ka tafi ka yaƙi Ammonawa ba ka gayyace mu ba? Za mu ƙone gidanka a kanka.”
And the men of Ephraim were called together, and went northward, and said unto Yiphthach, Wherefore didst thou pass over to fight against the children of 'Ammon, and didst not call for us to go with thee? thy house will we burn over thee with fire.
2 Yefta ya ce, “Ni da mutanena mun yi ta jayayya sosai da Ammonawa, ko da yake na kira ku, amma ba ku cece ni daga hannuwansu ba.
And Yiphthach said unto them, I and my people were greatly engaged in strife with the children of 'Ammon; and I called you, but ye helped me not out of their hand.
3 Da na ga ba za ku taimake ni ba, sai na yi kasai da raina na kuwa haye don in yaƙi Ammonawa, Ubangiji kuwa ya ba ni nasara a kansu. To, don me kuka zo yau don ku yaƙe ni?”
And when I saw that ye helped me not, I put my life in my hand, and passed over to the children of 'Ammon, and the Lord delivered them into my hand; and why then are ye come up unto me this day, to fight against me?
4 Sa’an nan Yefta ya tara mutanen Gileyad wuri guda ya kuma yaƙi Efraim. Mutanen Gileyad suka fatattake su domin mutanen Efraim sun ce, “Ku Mutanen Gileyad masu neman mafaka ne cikin Efraim da Manasse.”
Then Yiphthach gathered together all the men of Gil'ad, and fought with Ephraim; and the men of Gil'ad smote Ephraim, because they said, Ye are fugitives of Ephraim: Gil'ad is in the midst, between Ephraim and Menasseh.
5 Mutanen Gileyad suka ƙwace mashigan Urdun masu zuwa Efraim, duk sa’ad da wani daga Efraim da ya tsira ya ce, “Bari in haye,” sai mutane Gileyad su ce “Kai mutumin Efraim ne?” In ya ce, “A’a,”
And the Gil'adites seized on the passages of the Jordan before the Ephraimites: and it came to pass, when the Ephraimites who had escaped said, Let me pass over; that the men of Gil'ad said unto him, Art thou an Ephrathite? and if he said, No;
6 sai su ce, “To, ka ce, ‘Shibbolet.’” In ya ce, “Sibbolet,” saboda ba sa iya faɗin kalmar daidai, sai su kama shi su kashe a mashigan Urdun. Aka kashe mutanen Efraim dubu arba’in da biyu a ta haka.
Then said they unto him, Do say, Shibboleth; but when he said, Sibboleth, and was not able to pronounce it correctly, they laid hold of him and slew him on the passages of the Jordan; and there fell at that time of the Ephraimites forty and two thousand.
7 Yefta ya shugabanci Isra’ila shekara shida. Sa’an nan Yefta mutumin Gileyad ya mutu, aka kuwa binne shi wani gari a Gileyad.
And Yiphthach judged Israel six years; and then died Yiphthach the Gil'adite, and was buried in [one of] the cities of Gil'ad.
8 Bayansa, Ibzan mutumin Betlehem, ya shugabanci Isra’ila.
And after him there judged Israel Ibzan of Beth-lechem.
9 Yana’ya’ya maza talatin da’ya’ya mata talatin. Ya ba da auren’ya’yansa mata ga waɗanda ba daga dangi ba, ga’ya’yansa maza kuwa ya kawo’yan mata talatin su zama matansu waje da danginsa. Ibzan ya shugabanci Isra’ila shekara bakwai.
And he had thirty sons; and thirty daughters he sent abroad, and thirty daughters he brought in for his sons from abroad: and he judged Israel seven years.
10 Sa’an nan Ibzan ya mutu, aka kuwa binne shi Betlehem.
Then died Ibzan, and was buried at Beth-lechem.
11 Bayansa, Elon mutumin Zebulun, ya shugabanci Isra’ila shekara goma.
And after him there judged Israel Elon the Zebulonite; and he judged Israel ten years.
12 Sa’an nan Elon ya mutu, aka kuwa binne shi a Aiyalon a ƙasar Zebulun.
Then died Elon the Zebulonite, and was buried in Ayalon in the country of Zebulun.
13 Bayansa, Abdon ɗan Hillel, daga Firaton, ya shugabanci Isra’ila.
And after him there judged Israel 'Abdon the son of Hillel the Pir'athonite.
14 Yana da’ya’ya maza arba’in da’yan taɓa kunne talatin, waɗanda suka hau jakuna saba’in. Ya shugabanci Isra’ila shekara takwas.
And he had forty sons and thirty grandsons, that rode on seventy ass-colts; and he judged Israel eight years.
15 Sa’an nan Abdon ɗan Hillel ya mutu, aka kuwa binne shi a Firaton a Efraim, a ƙasar tudu ta Amalekawa.
Then died 'Abdon the son of Hillel the Pir'athonite, and was buried in Pir'athon in the land of Ephraim, in the mountain of the 'Amalekites.

< Mahukunta 12 >