< Mahukunta 11 >

1 Yefta mutumin Gileyad, jarumi ne ƙwarai. Mahaifinsa ne Gileyad; mahaifiyar kuwa karuwa ce.
[There was a man] from [the] Gilead [region] named Jephthah. He was a great warrior. His father was also named Gilead. But his mother was a prostitute.
2 Matar Gileyad ta haifa masa’ya’ya maza, kuma sa’ad da suka yi girma, sai suka kore Yefta, suka ce “Ba ka da gādo a cikin iyalinmu, domin kai ɗan wata mace ce.”
Gilead’s wife gave birth to several sons. When they grew up, they forced Jephthah to leave home, saying to him, “You are the son of a prostitute, [not the son of our mother]. So [when] our father [dies], you will not receive any of his property.”
3 Saboda haka Yefta ya tsere daga’yan’uwansa ya zauna a ƙasar Tob, inda waɗansu’yan iska suka kewaye shi suka bi shi.
So Jephthah ran away from his brothers, and he went to the Tob region. While he was there, some worthless men started to spend a lot of time with him.
4 Ana nan, sa’ad da Ammonawa suka kai wa Isra’ilawa hari,
Some time later, the Ammon people-group started to fight against the Israelis.
5 dattawan Gileyad suka je suka nemo Yefta daga ƙasar Tob.
When that happened [DOU], the leaders of [the] Gilead [region] went to Jephthah to bring him back from the Tob region [to their area].
6 Suka ce masa, “Ka zo ka zama mana shugaba, don mu yaƙi Ammonawa.”
They said to him, “Come [with us] and lead our army, and [help us to] fight against the men from the Ammon people-group!”
7 Yefta ya ce musu, “Ba kun ƙi ni kuka kuma kore ni daga gidan mahaifina ba? Me ya sa kuke zuwa wurina yanzu sa’ad da kuke cikin wahala?”
But Jephthah replied, “You hated me [RHQ] previously! You forced me to leave my father’s house! So why are you coming to me now, [asking me to help you] when you are experiencing trouble?”
8 Mutanen Gileyad suka ce masa, “Duk da haka, muna juyo wajenka yanzu, ka zo tare da mu mu yaƙi Ammonawa, za ka kuma zama shugaban duk wanda yake zama a Gileyad.”
The leaders from Gilead replied, “[Yes, we are having trouble, and] that is the reason that we have come to you now. If you come with us and [help us to] fight against the Ammon people-group, [after we defeat them, we will appoint] you to be the leader of all us people in [the] Gilead [region].”
9 Yefta ya ce, “A ce kun dawo da ni in yaƙi Ammonawa, Ubangiji kuwa ya ba da su a hannuna, zan zama shugabanku?”
Jephthah replied, “If I go back to Gilead with you to fight against the Ammon people-group, and if Yahweh helps us to defeat them, will you truly appoint me to be your leader?”
10 Dattawan Gileyad suka ce, “Ubangiji ne shaidanmu; za mu yi duk abin da ka ce.”
They replied, “Yahweh is listening to everything that we say. [So he will punish us] if we do not do everything that you tell us to do.”
11 Saboda haka Yefta ya tafi tare da dattawan Gileyad, mutanen kuwa suka naɗa shi shugabansu da kuma sarkinsu. Ya kuwa maimaita dukan maganarsa a gaban Ubangiji a Mizfa.
So Jephthah went with them back to [the] Gilead [region], and the people appointed him to be their leader and the commander of their army. And Jephthah solemnly promised to Yahweh there at Mizpah [to serve him well].
12 Sa’an nan Yefta ya aiki jakadu zuwa wurin sarkin Ammonawa su tambaya, “Me ya haɗa ka da ni, da ka kawo wa ƙasata yaƙi?”
Jephthah sent some messengers to the king of the Ammon people-group. They asked the king, “What have we [done to make you angry, with the result] that your army is coming to fight [against the people] in our land?”
13 Sarkin Ammonawa ya ce wa jakadu, “Sa’ad da Isra’ilawa suka fito daga Masar, sun ƙwace mini ƙasa tun daga Arnon zuwa Yabbok, har zuwa Urdun. Yanzu ka mayar mini ita cikin salama.”
The king replied, “[We have come to fight against you Israelis because] you took our land when you came here from Egypt. You took all our land east of the Jordan [River], from the Arnon [River in the south] to the Jabbok [River in the north]. So if you now give it back to us, there (will be peace between us/we will not fight against you).”
14 Yefta ya sāke aikan jakadu wurin sarki,
[The messengers returned to Jephthah and told him what the king had said]. So Jephthah sent the messengers to the king again.
15 yana cewa, “Ga abin da Yefta yake faɗi, Isra’ila ba tă ƙwace ƙasar Mowab ko ta Ammonawa ba.
They said to him, “This is what Jephthah says: ‘It is not [true] that we Israelis took the land from the Moab people-group and the Ammon people-group.
16 Amma sa’ad da suka bar Masar, Isra’ila ta bi ta hamada zuwa Jan Teku har suka zo Kadesh.
When the Israeli people came out of Egypt, they walked through the desert to the Red Sea, and then [walked across it and traveled to Kadesh town at the border of the Edom region].
17 Sa’an nan Isra’ila ta aiki jakadu zuwa ga sarkin Edom cewa, ‘Ka ba mu izini mu ratsa ƙasarka,’ amma sarkin Edom bai saurara ba. Suka kuma aika wa sarkin Mowab, shi ma ya ƙi. Saboda haka Isra’ila ta zauna a Kadesh.
They sent messengers to the king of the Edom people-group, to say to him, “Please allow us Israelis to walk across your land.” But the king of the Edom people-group refused. Later we sent the same message to the king of the Moab people-group, but he also refused to allow the Israelis to go through his land. So the Israelis stayed at Kadesh [for a long time].
18 “Daga can suka ci gaba ta hamada, suka zaga ƙasashen Edom da Mowab, suka wuce ta gabashin ƙasar Mowab, sa’an nan suka yi sansani a ɗaya gefen Arnon. Ba su shiga yankin Mowab ba, gama Arnon ce iyakarta.
Then the Israelis went into the desert and walked outside the borders of the Edom and Moab regions. They walked east of the Moab region, east of the Arnon [River, which is the eastern border of the Moab region]. They did not cross that river to enter [the] Moab [region].
19 “Sa’an nan Isra’ila ta aiki jakadu zuwa ga Sihon sarkin Amoriyawa, wanda yake mulki a Heshbon, ta ce masa, ‘Ka bar mu mu ratsa ƙasarka mu wuce zuwa wurinmu.’
‘Then the Israelis sent a message to Sihon, the king of the Amor people-group, who lived in Heshbon [city]. They asked him, “Will you please allow us Israeli people to cross through your land to arrive at the land to which we [are going].”
20 Sihon dai, bai amince da Isra’ila su ratsa ƙasarsa ba. Ya tattara dukan mutanensa suka yi sansani a Yahza suka kuwa yaƙi Isra’ila.
But Sihon did not trust the Israelis; [he thought that they would steal some of the things in his land]. So he gathered all his troops and they set up their tents at Jahaz [village] and then they attacked the Israelis.
21 “Sa’an nan Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya ba da Sihon da dukan mutanensa a hannun Isra’ila, suka kuwa ci nasara a kansu. Isra’ila ta ƙwace dukan ƙasar Amoriyawa da suke zaune a ƙasar,
But Yahweh, the God whom we Israelis [worship], enabled the Israeli army to defeat [IDM] Sihon and his army. Then they (took possession of/started to live in) all the land where the Amor people-group had lived.
22 suka ƙwace dukan yankin Amoriyawa tun daga ƙasar Arnon zuwa Yabbok, daga hamada har zuwa Urdun.
The Israelis took all the land that belonged to the Amor people-group, from the Arnon [River in the south] to the Jabbok [River in the north], and from the desert [in the east] to the Jordan [River in the west].
23 “To, da yake Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya kori Amoriyawa a gaban mutanensa Isra’ila, wane’yanci kake da shi da za ka karɓe ta?
‘It was Yahweh, the God whom we Israelis [worship], who forced the Amor people-group to leave as the Israelis advanced. So do you now think that you can force the Israelis to leave [RHQ]?
24 Ba za ka karɓi abin da allahnka Kemosh ya ba ka ba? Haka mu ma, duk abin da Ubangiji Allahnmu ya riga ya ba mu, za mu mallake shi.
You take the land that your god Chemosh has given to you. And we will live in the land that Yahweh our God has given to us!
25 Ka fi Balak ɗan Ziffor, sarkin Mowab ne? Ka taɓa ji ya yi hamayya da Isra’ila ko yă yi yaƙi da su?
(You are no/Are you) better than Zippor’s son Balak, who was the king of the Moab people-group? He never [RHQ] quarreled with the Israeli people, and he never started to fight against us [RHQ]!
26 Shekara ɗari uku Isra’ilawa suka yi zamansu a Heshbon, Arower da ƙauyukan kewayenta da dukan biranen da suke gefen Arnon. Me ya sa ba ka karɓe su a lokacin ba?
For 300 years the Israeli people have lived in Heshbon and Aroer [cities in your region], and in the surrounding towns, and in all the cities along the Arnon [River]. Why have you people of the Ammon people-group not taken back those cities during all those years [RHQ]?
27 Ban yi maka laifi ba, amma kana musguna mini ta wurin kawo mini hari. Bari Ubangiji yă zama Alƙali, yă yanke hukunci tsakani Isra’ilawa da Ammonawa.”
We have not sinned against you, but you are sinning against me by attacking me [and my army]. I trust that Yahweh, the great judge, will decide whether we Israelis are right, or whether you people of the Ammon people-group are right.’”
28 Duk da haka sarkin Ammonawa bai kula da saƙon da Yefta ya aika ba.
But the king of the Ammon people-group did not pay attention to that message from Jephthah.
29 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko wa Yefta. Sai ya haye Gileyad da Manasse, ya ratsa ta Mizfa zuwa Gileyad, daga can kuma ya kai wa Ammonawa hari.
Then the Spirit of Yahweh took control of Jephthah. Jephthah went through [the] Gilead [region] and through the area where the tribe of Manasseh lived, [to enlist/gather men for his army]. [He finally gathered them together] in Mizpah [city] in [the] Gilead [region] to fight against the Ammon people-group.
30 Yefta kuwa ya yi wa’adi da Ubangiji ya ce, “In ka ba da Ammonawa a hannuwana,
There Jephthah made a solemn promise to Yahweh. He said, “If you will enable my army to defeat [IDM] the Ammon people-group,
31 duk abin da ya fara fitowa daga ƙofar gidana don yă tarye ni, sa’ad da na komo daga yaƙi da Ammonawa, zai zama na Ubangiji, zan miƙa shi hadaya ta ƙonawa.”
when I return from the battle, I will sacrifice to you the first person who comes out of my house [to greet me]. It will be a sacrifice that will be completely burned [on the altar].”
32 Sa’an nan Yefta ya haye zuwa wajen Ammonawa don yaƙi da su. Ubangiji kuwa ya ba da su a hannuwansa.
Then Jephthah [and his men] went from Mizpah to attack the Ammon people-group, and Yahweh enabled his army to defeat them.
33 Ya hallaka birane ashirin tun daga Arower zuwa yankin Minnit, har zuwa Abel-Keramim. Haka Isra’ila ta cinye Ammonawa ƙaf.
Jephthah and his men killed them, from Aroer [city] all the way to the area around the city of Minnith. They destroyed 20 cities, as far as [the city of] Abel Keramim. So the Israelis [completely] defeated the Ammon people-group.
34 Sa’ad da Yefta ya komo gida a Mizfa, wa ya fito yă tarye shi,’yarsa tilo, tana rawa kiɗin ganguna! Ita ce kaɗai’yarsa. Ban da ita ba shi da ɗa ko’ya.
When Jephthah returned to his home in Mizpah, his daughter was the first one to come out of the house to meet him. She was [joyfully] playing a tambourine and dancing. She was his only child; he had no sons and no other daughters.
35 Da ya gan ta, sai ya yayyage tufafinsa ya yi kuka ya ce, “Kaito!’Yata! Kin karya mini gwiwa, kuma na lalace, domin na yi wa’adi ga Ubangiji da ba zan iya in karya ba.”
When Jephthah saw his daughter, he tore his clothes [to show that he was very sad about what he was going to do]. He said to her, “My daughter, you have caused me to become very sad [DOU] because I made a solemn promise to Yahweh [to sacrifice the first one who came out of my house], and I must do what I promised.”
36 Ta ce, “Mahaifina, idan ka riga ka yi wa Ubangiji magana, sai ka yi da ni yadda ka yi alkawari, da yake Ubangiji ya ɗau maka fansa a kan Ammonawa.”
His daughter said, “My father, you made a solemn promise to Yahweh. So you must do to me what you promised, because [you said that you would do that if] Yahweh helped you to defeat our enemies, the Ammon people-group.”
37 Sai ta kuma ce, “Sai dai, ka biya mini wannan bukata guda. Ka ba ni wata biyu in yi ta yawo da ni da ƙawayena a kan duwatsu mu yi makoki, domin ba zan yi aure ba.”
Then she also said, “But allow me to do one thing. (First/before you do what you promised), allow me to go up into the hilly area and wander around for two months. Since I will never be married [and have children], allow me and my friends to go and cry together.”
38 Ya ce mata, “Ki tafi,” Ya bar ta tă tafi har wata biyu. Ita da’yan matan suka tafi a kan duwatsu suka yi ta makoki domin ba za tă taɓa aure ba.
Jephthah replied, “All right, you may go.” So she left for two months. She and her friends stayed in the hills and they cried for her because she would never be married.
39 Bayan watanni biyu ɗin sai ta komo wurin mahaifinta ya kuwa yi da ita yadda ya yi wa’adi. Ita kuwa ba tă taɓa san namiji ba. Wannan ya zama al’ada a Isra’ila,
After two months, she returned to her father Jephthah, and he did to her what he had vowed. So his daughter never was married. Because of that, the Israelis now have a custom.
40 cewa kowace shekara’yan mata sukan fita kwana huɗu don yin bikin tunawa da’yar Yefta mutumin Gileyad.
Every year the young Israeli women go [into the hills] for four days to remember [and cry about what happened to] the daughter of Jephthah.

< Mahukunta 11 >