< Mahukunta 11 >

1 Yefta mutumin Gileyad, jarumi ne ƙwarai. Mahaifinsa ne Gileyad; mahaifiyar kuwa karuwa ce.
And Jephthah the Gileadite he was a mighty [man] of strength and he [was] [the] son of a woman a prostitute and he fathered Gilead Jephthah.
2 Matar Gileyad ta haifa masa’ya’ya maza, kuma sa’ad da suka yi girma, sai suka kore Yefta, suka ce “Ba ka da gādo a cikin iyalinmu, domin kai ɗan wata mace ce.”
And she bore [the] wife of Gilead to him sons and they grew up [the] sons of the wife and they drove out Jephthah and they said to him not you will have an inheritance in [the] house of father our for [are] [the] son of a woman another you.
3 Saboda haka Yefta ya tsere daga’yan’uwansa ya zauna a ƙasar Tob, inda waɗansu’yan iska suka kewaye shi suka bi shi.
And he fled Jephthah [away] from before brothers his and he dwelt in [the] land of Tob and they joined themselves to Jephthah men unprincipled and they went out with him.
4 Ana nan, sa’ad da Ammonawa suka kai wa Isra’ilawa hari,
And it was from days and they fought [the] people of Ammon with Israel.
5 dattawan Gileyad suka je suka nemo Yefta daga ƙasar Tob.
And it was just when they fought [the] people of Ammon with Israel and they went [the] elders of Gilead to fetch Jephthah from [the] land of Tob.
6 Suka ce masa, “Ka zo ka zama mana shugaba, don mu yaƙi Ammonawa.”
And they said to Jephthah come! and you will become of us a commander so let us fight against [the] people of Ammon.
7 Yefta ya ce musu, “Ba kun ƙi ni kuka kuma kore ni daga gidan mahaifina ba? Me ya sa kuke zuwa wurina yanzu sa’ad da kuke cikin wahala?”
And he said Jephthah to [the] elders of Gilead ¿ not you did you hate me and did you drive out? me from [the] house of father my and why? have you come to me now just when [is] distress to you.
8 Mutanen Gileyad suka ce masa, “Duk da haka, muna juyo wajenka yanzu, ka zo tare da mu mu yaƙi Ammonawa, za ka kuma zama shugaban duk wanda yake zama a Gileyad.”
And they said [the] elders of Gilead to Jephthah therefore now we have returned to you and you will come with us and you will fight against [the] people of Ammon and you will become of us chief of all [the] inhabitants of Gilead.
9 Yefta ya ce, “A ce kun dawo da ni in yaƙi Ammonawa, Ubangiji kuwa ya ba da su a hannuna, zan zama shugabanku?”
And he said Jephthah to [the] elders of Gilead if [are] bringing back you me to fight against [the] people of Ammon and he will deliver up Yahweh them before me I I will become of you chief.
10 Dattawan Gileyad suka ce, “Ubangiji ne shaidanmu; za mu yi duk abin da ka ce.”
And they said [the] elders of Gilead to Jephthah Yahweh he will be hearing between us if not according to word your so we will do.
11 Saboda haka Yefta ya tafi tare da dattawan Gileyad, mutanen kuwa suka naɗa shi shugabansu da kuma sarkinsu. Ya kuwa maimaita dukan maganarsa a gaban Ubangiji a Mizfa.
And he went Jephthah with [the] elders of Gilead and they made the people him over them into chief and into commander and he spoke Jephthah all words his before Yahweh in Mizpah.
12 Sa’an nan Yefta ya aiki jakadu zuwa wurin sarkin Ammonawa su tambaya, “Me ya haɗa ka da ni, da ka kawo wa ƙasata yaƙi?”
And he sent Jephthah messengers to [the] king of [the] people of Ammon saying what? [is] to me and to you that you have come to me to wage war against land my.
13 Sarkin Ammonawa ya ce wa jakadu, “Sa’ad da Isra’ilawa suka fito daga Masar, sun ƙwace mini ƙasa tun daga Arnon zuwa Yabbok, har zuwa Urdun. Yanzu ka mayar mini ita cikin salama.”
And he said [the] king of [the] people of Ammon to [the] messengers of Jephthah that it took Israel land my when came up it from Egypt from [the] Arnon and to the Jabbok and to the Jordan and therefore restore! them in peace.
14 Yefta ya sāke aikan jakadu wurin sarki,
And he repeated again Jephthah and he sent messengers to [the] king of [the] people of Ammon.
15 yana cewa, “Ga abin da Yefta yake faɗi, Isra’ila ba tă ƙwace ƙasar Mowab ko ta Ammonawa ba.
And he said to him thus he says Jephthah not it has taken Israel [the] land of Moab and [the] land of [the] people of Ammon.
16 Amma sa’ad da suka bar Masar, Isra’ila ta bi ta hamada zuwa Jan Teku har suka zo Kadesh.
That when came up they from Egypt and it went Israel in the wilderness to [the] sea of reed[s] and it came Kadesh towards.
17 Sa’an nan Isra’ila ta aiki jakadu zuwa ga sarkin Edom cewa, ‘Ka ba mu izini mu ratsa ƙasarka,’ amma sarkin Edom bai saurara ba. Suka kuma aika wa sarkin Mowab, shi ma ya ƙi. Saboda haka Isra’ila ta zauna a Kadesh.
And it sent Israel messengers - to [the] king of Edom - saying let me pass please in land your and not he listened [the] king of Edom and also to [the] king of Moab it sent and not he was willing and it remained Israel at Kadesh.
18 “Daga can suka ci gaba ta hamada, suka zaga ƙasashen Edom da Mowab, suka wuce ta gabashin ƙasar Mowab, sa’an nan suka yi sansani a ɗaya gefen Arnon. Ba su shiga yankin Mowab ba, gama Arnon ce iyakarta.
And it went in the wilderness and it went around [the] land of Edom and [the] land of Moab and it came from [the] rising of [the] sun of [the] land of Moab and they encamped! on [the] other side of [the] Arnon and not they went in [the] territory of Moab for [the] Arnon [was] [the] border of Moab.
19 “Sa’an nan Isra’ila ta aiki jakadu zuwa ga Sihon sarkin Amoriyawa, wanda yake mulki a Heshbon, ta ce masa, ‘Ka bar mu mu ratsa ƙasarka mu wuce zuwa wurinmu.’
And it sent Israel messengers to Sihon [the] king of the Amorite[s] [the] king of Heshbon and it said to him Israel let us pass please in land your to own place my.
20 Sihon dai, bai amince da Isra’ila su ratsa ƙasarsa ba. Ya tattara dukan mutanensa suka yi sansani a Yahza suka kuwa yaƙi Isra’ila.
And not he trusted Sihon Israel to pass in territory his and he gathered Sihon all people his and they encamped at Jahaz and he fought with Israel.
21 “Sa’an nan Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya ba da Sihon da dukan mutanensa a hannun Isra’ila, suka kuwa ci nasara a kansu. Isra’ila ta ƙwace dukan ƙasar Amoriyawa da suke zaune a ƙasar,
And he gave Yahweh [the] God of Israel Sihon and all people his in [the] hand of Israel and they defeated them and it took possession of Israel all [the] land of the Amorite[s] [who] dwelt of the land that.
22 suka ƙwace dukan yankin Amoriyawa tun daga ƙasar Arnon zuwa Yabbok, daga hamada har zuwa Urdun.
And they took possession of all [the] territory of the Amorite[s] from [the] Arnon and to the Jabbok and from the wilderness and to the Jordan.
23 “To, da yake Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya kori Amoriyawa a gaban mutanensa Isra’ila, wane’yanci kake da shi da za ka karɓe ta?
And now Yahweh - [the] God of Israel he has dispossessed the Amorite[s] from before people his Israel and you will you take possession of? it.
24 Ba za ka karɓi abin da allahnka Kemosh ya ba ka ba? Haka mu ma, duk abin da Ubangiji Allahnmu ya riga ya ba mu, za mu mallake shi.
¿ Not [that] which he will cause to possess you Chemosh god your it will you take possession of and all that he has dispossessed Yahweh God our from before us it we will take possession of.
25 Ka fi Balak ɗan Ziffor, sarkin Mowab ne? Ka taɓa ji ya yi hamayya da Isra’ila ko yă yi yaƙi da su?
And now ¿ really good [are] you more than Balak [the] son of Zippor [the] king of Moab ¿ really did he quarrel with Israel or? ever did he wage war against them.
26 Shekara ɗari uku Isra’ilawa suka yi zamansu a Heshbon, Arower da ƙauyukan kewayenta da dukan biranen da suke gefen Arnon. Me ya sa ba ka karɓe su a lokacin ba?
When dwelt Israel in Heshbon and in daughters its and in Aroer and in daughters its and in all the cities which [were] on [the] sides of [the] Arnon three hundred year[s] and why? not did you recover [them] at the time that.
27 Ban yi maka laifi ba, amma kana musguna mini ta wurin kawo mini hari. Bari Ubangiji yă zama Alƙali, yă yanke hukunci tsakani Isra’ilawa da Ammonawa.”
And I not I have sinned to you and you [are] doing with me evil by waging war against me may he judge Yahweh the judge this day between [the] people of Israel and between [the] people of Ammon.
28 Duk da haka sarkin Ammonawa bai kula da saƙon da Yefta ya aika ba.
And not he listened [the] king of [the] people of Ammon to [the] words of Jephthah which he sent to him.
29 Sa’an nan Ruhun Ubangiji ya sauko wa Yefta. Sai ya haye Gileyad da Manasse, ya ratsa ta Mizfa zuwa Gileyad, daga can kuma ya kai wa Ammonawa hari.
And it was on Jephthah [the] spirit of Yahweh and he passed through Gilead and Manasseh and he passed through Mizpah of Gilead and from Mizpah of Gilead he he passed on [the] people of Ammon.
30 Yefta kuwa ya yi wa’adi da Ubangiji ya ce, “In ka ba da Ammonawa a hannuwana,
And he vowed Jephthah a vow to Yahweh and he said certainly [if] you will give [the] people of Ammon in hand my.
31 duk abin da ya fara fitowa daga ƙofar gidana don yă tarye ni, sa’ad da na komo daga yaƙi da Ammonawa, zai zama na Ubangiji, zan miƙa shi hadaya ta ƙonawa.”
And it will be whatever comes out which it will come out from [the] doors of house my to meet me when return I in peace from [the] people of Ammon and it will belong to Yahweh and I will offer up it a burnt offering.
32 Sa’an nan Yefta ya haye zuwa wajen Ammonawa don yaƙi da su. Ubangiji kuwa ya ba da su a hannuwansa.
And he passed on Jephthah to [the] people of Ammon to fight against them (and he gave them *L(abh)*) Yahweh in hand his.
33 Ya hallaka birane ashirin tun daga Arower zuwa yankin Minnit, har zuwa Abel-Keramim. Haka Isra’ila ta cinye Ammonawa ƙaf.
And he defeated them from Aroer and until coming you Minnith twenty citi[es] and to Abel Keramim a defeat great very and they were subdued [the] people of Ammon from before [the] people of Israel.
34 Sa’ad da Yefta ya komo gida a Mizfa, wa ya fito yă tarye shi,’yarsa tilo, tana rawa kiɗin ganguna! Ita ce kaɗai’yarsa. Ban da ita ba shi da ɗa ko’ya.
And he came Jephthah Mizpah to house his and there! daughter his [was] coming out to meet him with tambourines and with dancing and only she [was] an only [child] not [belonged] to him from him a son or a daughter.
35 Da ya gan ta, sai ya yayyage tufafinsa ya yi kuka ya ce, “Kaito!’Yata! Kin karya mini gwiwa, kuma na lalace, domin na yi wa’adi ga Ubangiji da ba zan iya in karya ba.”
And it was when saw he her and he tore clothes his and he said alas! O daughter my certainly you have brought low me and you you are among [those who] trouble me and I I have opened mouth my to Yahweh and not I am able to turn back.
36 Ta ce, “Mahaifina, idan ka riga ka yi wa Ubangiji magana, sai ka yi da ni yadda ka yi alkawari, da yake Ubangiji ya ɗau maka fansa a kan Ammonawa.”
And she said to him O father my you have opened mouth your to Yahweh do to me just as it has come out from mouth your after that he did for you Yahweh vengeance from enemies your from [the] people of Ammon.
37 Sai ta kuma ce, “Sai dai, ka biya mini wannan bukata guda. Ka ba ni wata biyu in yi ta yawo da ni da ƙawayena a kan duwatsu mu yi makoki, domin ba zan yi aure ba.”
And she said to father her let it be done for me the thing this refrain from me two months so let me go and I will go down on the mountains so I may weep on virginiti my I (and companions my. *Q(K)*)
38 Ya ce mata, “Ki tafi,” Ya bar ta tă tafi har wata biyu. Ita da’yan matan suka tafi a kan duwatsu suka yi ta makoki domin ba za tă taɓa aure ba.
And he said go and he sent away her two months and she went she and companions her and she wept on virginiti her on the mountains.
39 Bayan watanni biyu ɗin sai ta komo wurin mahaifinta ya kuwa yi da ita yadda ya yi wa’adi. Ita kuwa ba tă taɓa san namiji ba. Wannan ya zama al’ada a Isra’ila,
And it was from [the] end of - two months and she returned to father her and he did to her vow his which he had vowed and she not she had known a man and it was a custom in Israel.
40 cewa kowace shekara’yan mata sukan fita kwana huɗu don yin bikin tunawa da’yar Yefta mutumin Gileyad.
From days - days towards they go [the] daughters of Israel to recount for [the] daughter of Jephthah the Gileadite four days in the year.

< Mahukunta 11 >