< Mahukunta 10 >
1 Bayan zamanin Abimelek, sai Tola ɗan Fuwa ɗan Dodo daga Issakar ya tashi don yă ceci Isra’ila. Yana zama a Shamir a ƙasar tudu ta Efraim.
Avimelek'in ölümünden sonra İsrail'i kurtarmak için İssakar oymağından Dodo oğlu Pua oğlu Tola adında bir adam ortaya çıktı. Tola Efrayim'in dağlık bölgesindeki Şamir'de yaşardı.
2 Ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da uku sa’an nan ya mutu, aka kuma binne shi a Shamir.
İsrail'i yirmi üç yıl yönettikten sonra öldü, Şamir'de gömüldü.
3 Bayansa kuma sai Yayir daga Gileyad, wanda ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da biyu.
Ondan sonra Gilatlı Yair başa geçti. Yair İsrail'i yirmi iki yıl yönetti.
4 Yana’ya’ya talatin, waɗanda suke hawan jakuna talatin. Sun shugabanci birane talatin a Gileyad, har wa yau ana ce da biranen Hawwot Yayir.
Otuz oğlu vardı. Bunlar otuz eşeğe biner, otuz kenti yönetirlerdi. Gilat yöresindeki bu kentler bugün de Havvot-Yair diye anılıyor.
5 Sa’ad da Yayir ya mutu, sai aka binne shi a Kamon.
Yair ölünce Kamon'da gömüldü.
6 Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji. Suka shiga bautar Ba’al da Ashtarot, da kuma allolin Aram, allolin Sidon, allolin Mowab, Ammonawa da kuma allolin Filistiyawa. Kuma domin Isra’ilawa sun bar Ubangiji ba su ƙara bauta masa ba,
İsrailliler yine RAB'bin gözünde kötü olanı yaptılar; Baallar'a, Aştoretler'e, Aram, Sayda, Moav, Ammon ve Filist ilahlarına kulluk ettiler. RAB'bi terk ettiler, O'na kulluk etmediler.
7 sai ya fusata da su. Ya sayar da su ga hannun Filistiyawa da Ammonawa,
Bu yüzden İsrailliler'e öfkelenen RAB, onları Filistliler'e ve Ammonlular'a tutsak etti.
8 waɗanda suka fatattake su a shekarar suka kuma ragargaza su. Shekara goma sha takwas suka yi ta danne dukan Isra’ilawan da suke gabashin Urdun a Gileyad, ƙasar Amoriyawa.
Bunlar o yıldan başlayarak İsrailliler'i baskı altında ezdiler; Şeria Irmağı'nın ötesinde, Gilat'taki Amorlular ülkesinde yaşayan bütün İsrailliler'i on sekiz yıl baskı altında tuttular.
9 Ammonawa su ma suka haye Urdun domin su yi yaƙi da Yahuda, Benyamin da kuma gidan Efraim; Isra’ila kuwa suka kasance cikin wahala ƙwarai da gaske.
Ammonlular Yahuda, Benyamin ve Efrayim oymaklarıyla savaşmak için Şeria Irmağı'nın ötesine geçtiler. İsrail büyük sıkıntı içindeydi.
10 Sa’an nan Isra’ilawa suka yi kuka ga Ubangiji, suka ce, “Mun yi maka zunubi, mun bar Allahnmu muka shiga bautar Ba’al.”
İsrailliler RAB'be, “Sana karşı günah işledik” diye seslendiler, “Seni, Tanrımız'ı terk edip Baallar'a kulluk ettik.”
11 Ubangiji ya ce, “Sa’ad da Masarawa, Amoriyawa, Ammonawa, Filistiyawa,
RAB, “Sizi Mısırlılar'dan, Amorlular'dan, Ammonlular'dan, Filistliler'den kurtaran ben değil miyim?” diye karşılık verdi,
12 Sidoniyawa, Amalekawa da kuma mutanen Mawon suka wulaƙanta ku kuka kuwa yi mini kuka, ban cece ku daga hannunsu ba?
“Saydalılar, Amalekliler, Maonlular size baskı yaptıklarında bana yakardınız, ben de sizi onların elinden kurtardım.
13 Amma kuka bar ni kuka bauta wa waɗansu alloli, saboda haka ni ma ba zan ƙara cece ku ba.
Sizse beni terk ettiniz, başka ilahlara kulluk ettiniz. Bu yüzden sizi bir daha kurtarmayacağım.
14 Ku tafi ku yi wa allolin da kuka zaɓa. Bari su cece ku sa’ad da kuke cikin wahala!”
Gidin, seçtiğiniz ilahlara yakarın; sıkıntıya düştüğünüzde sizi onlar kurtarsın.”
15 Amma Isra’ilawa suka ce wa Ubangiji, “Mu dai mun yi zunubi. Ka yi da mu abin da ka ga dama, amma muna roƙonka ka cece mu a yanzu.”
İsrailliler, “Günah işledik” dediler, “Bize ne istersen yap. Yalnız bugün bizi kurtar.”
16 Sa’an nan suka zubar da allolin nan daga cikinsu suka bauta wa Ubangiji. Ubangiji kuwa bai ƙara daure da azabar da Isra’ila suke sha ba.
Sonra aralarındaki yabancı putları atıp RAB'be tapındılar. RAB de onların daha fazla acı çekmesine dayanamadı.
17 Sa’ad da aka kira Ammonawa su yi ɗamarar yaƙi, sai su kuma kafa sansani a Gileyad, Isra’ilawa kuwa suka tattaru suka kafa sansani Mizfa.
Ammonlular toplanıp Gilat'ta ordugah kurunca İsrailliler de toplanarak Mispa'da ordugah kurdular.
18 Shugabannin mutanen Gileyad suka cewa juna, “Duk wanda zai fara fāɗa wa Ammonawa shi zai zama shugaban duk waɗanda suke zama a Gileyad.”
Gilat halkının önderleri birbirlerine, “Ammonlular'a karşı ilk saldırıyı başlatan kişi, bütün Gilat halkının önderi olacak” dediler.