< Mahukunta 10 >

1 Bayan zamanin Abimelek, sai Tola ɗan Fuwa ɗan Dodo daga Issakar ya tashi don yă ceci Isra’ila. Yana zama a Shamir a ƙasar tudu ta Efraim.
After Abimelech died, Tola the son of Puah and grandson of Dodo became the leader to rescue the Israeli people [from their enemies]. He belonged to the tribe of Issachar, but he lived in Shamir [city] in the hilly area where the descendants of Ephraim live.
2 Ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da uku sa’an nan ya mutu, aka kuma binne shi a Shamir.
He ruled the Israeli people for 23 years. Then he died and was buried in Shamir.
3 Bayansa kuma sai Yayir daga Gileyad, wanda ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da biyu.
After Tola died, Jair, from [the] Gilead [region], became the Israelis’ leader, and he ruled them for 22 years.
4 Yana’ya’ya talatin, waɗanda suke hawan jakuna talatin. Sun shugabanci birane talatin a Gileyad, har wa yau ana ce da biranen Hawwot Yayir.
He had thirty sons, and each of them had his own donkey to ride on. They each controlled a different town in [the] Gilead [region]. That region is still named ‘The Towns of Jair’.
5 Sa’ad da Yayir ya mutu, sai aka binne shi a Kamon.
When Jair died, he was buried in Kamon [city].
6 Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji. Suka shiga bautar Ba’al da Ashtarot, da kuma allolin Aram, allolin Sidon, allolin Mowab, Ammonawa da kuma allolin Filistiyawa. Kuma domin Isra’ilawa sun bar Ubangiji ba su ƙara bauta masa ba,
Again the Israelis did things that Yahweh said were wrong/evil. They worshiped [the idols of their god] Baal and [their goddess] Astarte. They also worshiped the gods of the Aram, Sidon, Moab, and Ammon people-groups, and the gods of the Philistia people-group. They abandoned Yahweh and stopped worshiping him.
7 sai ya fusata da su. Ya sayar da su ga hannun Filistiyawa da Ammonawa,
So Yahweh was very angry with them, and he allowed the Philistia and Ammon people-groups to defeat [IDM] the Israelis.
8 waɗanda suka fatattake su a shekarar suka kuma ragargaza su. Shekara goma sha takwas suka yi ta danne dukan Isra’ilawan da suke gabashin Urdun a Gileyad, ƙasar Amoriyawa.
In that same year, those people started to oppress the Israelis who lived in [the] Gilead [region] on the east side of the Jordan [River]. That was where the Amor people-group also lived. were They caused the Israelis who lived in that region to suffer for 18 years.
9 Ammonawa su ma suka haye Urdun domin su yi yaƙi da Yahuda, Benyamin da kuma gidan Efraim; Isra’ila kuwa suka kasance cikin wahala ƙwarai da gaske.
Then the people of the Ammon people-group crossed the Jordan [River] to fight against the people of the tribes of Judah, Benjamin, and Ephraim. They caused the Israelis’ lives to be very miserable.
10 Sa’an nan Isra’ilawa suka yi kuka ga Ubangiji, suka ce, “Mun yi maka zunubi, mun bar Allahnmu muka shiga bautar Ba’al.”
So the Israelis cried out to Yahweh, saying “We have sinned against you. We have abandoned you, and we have been worshiping [the idols of their god] Baal.”
11 Ubangiji ya ce, “Sa’ad da Masarawa, Amoriyawa, Ammonawa, Filistiyawa,
Yahweh answered them, saying, “When the people of Egypt, and the Amor and Ammon and Philistia people-groups
12 Sidoniyawa, Amalekawa da kuma mutanen Mawon suka wulaƙanta ku kuka kuwa yi mini kuka, ban cece ku daga hannunsu ba?
and the Sidon and Amalek and Maon people-groups were cruel to you, you cried out to me, and then I rescued you.
13 Amma kuka bar ni kuka bauta wa waɗansu alloli, saboda haka ni ma ba zan ƙara cece ku ba.
But now you have abandoned me again, and you have been worshiping other gods. So I will not rescue you again.
14 Ku tafi ku yi wa allolin da kuka zaɓa. Bari su cece ku sa’ad da kuke cikin wahala!”
You have chosen those gods [to be the ones that you worship]. So call to them to help you. Allow them to rescue you when you have a lot of trouble!”
15 Amma Isra’ilawa suka ce wa Ubangiji, “Mu dai mun yi zunubi. Ka yi da mu abin da ka ga dama, amma muna roƙonka ka cece mu a yanzu.”
But the Israeli people said to Yahweh, “Truly we have sinned. Punish us in whatever way you wish to, but please rescue us now!”
16 Sa’an nan suka zubar da allolin nan daga cikinsu suka bauta wa Ubangiji. Ubangiji kuwa bai ƙara daure da azabar da Isra’ila suke sha ba.
Then the Israelis threw away the [idols of the] gods that belonged to other people-groups, and they worshiped Yahweh again. He saw that they were suffering very much, and he felt sorry [IDM] for them.
17 Sa’ad da aka kira Ammonawa su yi ɗamarar yaƙi, sai su kuma kafa sansani a Gileyad, Isra’ilawa kuwa suka tattaru suka kafa sansani Mizfa.
The Ammon people-group gathered to fight [against the Israelis], and they set up their tents in [the] Gilead [region]. The Israeli men also gathered and set up their tents at Mizpah, [which was a city in Gilead].
18 Shugabannin mutanen Gileyad suka cewa juna, “Duk wanda zai fara fāɗa wa Ammonawa shi zai zama shugaban duk waɗanda suke zama a Gileyad.”
The Israeli leaders said, “Who will lead our soldiers to attack the Ammon people-group? The one who will lead us will become the leader of all us who live in this Gilead [region].”

< Mahukunta 10 >