< Mahukunta 10 >

1 Bayan zamanin Abimelek, sai Tola ɗan Fuwa ɗan Dodo daga Issakar ya tashi don yă ceci Isra’ila. Yana zama a Shamir a ƙasar tudu ta Efraim.
And he arose after Abimelech to deliver Israel Tola [the] son of Puah [the] son of Dodo man of Issachar and he [was] dwelling in Shamir in [the] hill country of Ephraim.
2 Ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da uku sa’an nan ya mutu, aka kuma binne shi a Shamir.
And he judged Israel twenty and three year[s] and he died and he was buried in Shamir.
3 Bayansa kuma sai Yayir daga Gileyad, wanda ya shugabanci Isra’ila shekara ashirin da biyu.
And he arose after him Jair the Gileadite and he judged Israel twenty and two year[s].
4 Yana’ya’ya talatin, waɗanda suke hawan jakuna talatin. Sun shugabanci birane talatin a Gileyad, har wa yau ana ce da biranen Hawwot Yayir.
And it belonged to him thirty sons [who] rode on thirty donkeys and thirty cities [belonged] to them them people call - Havvoth Jair until the day this which [are] in [the] land of Gilead.
5 Sa’ad da Yayir ya mutu, sai aka binne shi a Kamon.
And he died Jair and he was buried in Kamon.
6 Isra’ilawa suka sāke yin mugayen ayyuka a gaban Ubangiji. Suka shiga bautar Ba’al da Ashtarot, da kuma allolin Aram, allolin Sidon, allolin Mowab, Ammonawa da kuma allolin Filistiyawa. Kuma domin Isra’ilawa sun bar Ubangiji ba su ƙara bauta masa ba,
And they repeated - [the] people of Israel to do the evil in [the] eyes of Yahweh and they served the Baals and the Ashtaroth and [the] gods of Aram and [the] gods of Sidon and - [the] gods of Moab and [the] gods of [the] people of Ammon and [the] gods of [the] Philistines and they forsook Yahweh and not they served him.
7 sai ya fusata da su. Ya sayar da su ga hannun Filistiyawa da Ammonawa,
And it burned [the] anger of Yahweh on Israel and he sold them in [the] hand of [the] Philistines and in [the] hand of [the] people of Ammon.
8 waɗanda suka fatattake su a shekarar suka kuma ragargaza su. Shekara goma sha takwas suka yi ta danne dukan Isra’ilawan da suke gabashin Urdun a Gileyad, ƙasar Amoriyawa.
And they shattered and they crushed [the] people of Israel in the year that eight-teen year[s] all [the] people of Israel who [were] on [the] other side of the Jordan in [the] land of the Amorite[s] which [is] in Gilead.
9 Ammonawa su ma suka haye Urdun domin su yi yaƙi da Yahuda, Benyamin da kuma gidan Efraim; Isra’ila kuwa suka kasance cikin wahala ƙwarai da gaske.
And they passed over [the] people of Ammon the Jordan to fight also against Judah and against Benjamin and against [the] house of Ephraim and it was distress to Israel exceedingly.
10 Sa’an nan Isra’ilawa suka yi kuka ga Ubangiji, suka ce, “Mun yi maka zunubi, mun bar Allahnmu muka shiga bautar Ba’al.”
And they cried out [the] people of Israel to Yahweh saying we have sinned to you and for we have forsaken God our and we have served the Baals.
11 Ubangiji ya ce, “Sa’ad da Masarawa, Amoriyawa, Ammonawa, Filistiyawa,
And he said Yahweh to [the] people of Israel ¿ not from Egypt and from the Amorite[s] and from [the] people of Ammon and from [the] Philistines.
12 Sidoniyawa, Amalekawa da kuma mutanen Mawon suka wulaƙanta ku kuka kuwa yi mini kuka, ban cece ku daga hannunsu ba?
And [the] Sidonians and Amalek and Maon they oppressed you and you cried out to me and I delivered! you from hand their.
13 Amma kuka bar ni kuka bauta wa waɗansu alloli, saboda haka ni ma ba zan ƙara cece ku ba.
And you you have forsaken me and you have served gods other therefore not I will repeat to deliver you.
14 Ku tafi ku yi wa allolin da kuka zaɓa. Bari su cece ku sa’ad da kuke cikin wahala!”
Go and cry out to the gods which you have chosen them they let them deliver you at [the] time of distress your.
15 Amma Isra’ilawa suka ce wa Ubangiji, “Mu dai mun yi zunubi. Ka yi da mu abin da ka ga dama, amma muna roƙonka ka cece mu a yanzu.”
And they said [the] people of Israel to Yahweh we have sinned do you to us according to all the good in view your only deliver us please the day this.
16 Sa’an nan suka zubar da allolin nan daga cikinsu suka bauta wa Ubangiji. Ubangiji kuwa bai ƙara daure da azabar da Isra’ila suke sha ba.
And they removed [the] gods of foreignness from midst their and they served Yahweh and it was short self his at [the] trouble of Israel.
17 Sa’ad da aka kira Ammonawa su yi ɗamarar yaƙi, sai su kuma kafa sansani a Gileyad, Isra’ilawa kuwa suka tattaru suka kafa sansani Mizfa.
And they were summoned [the] people of Ammon and they encamped in Gilead and they gathered [the] people of Israel and they encamped at Mizpah.
18 Shugabannin mutanen Gileyad suka cewa juna, “Duk wanda zai fara fāɗa wa Ammonawa shi zai zama shugaban duk waɗanda suke zama a Gileyad.”
And they said the people [the] leaders of Gilead each to neighbor his who? [is] the man who he will begin to fight against [the] people of Ammon he will become chief of all [the] inhabitants of Gilead.

< Mahukunta 10 >