< Mahukunta 1 >
1 Bayan da Yoshuwa ya rasu, Isra’ilawa suka tambayi Ubangiji suka ce, “Wane ne zai fara tafiya don yă yaƙi Kan’aniyawa dominmu?”
Après la mort de Josué, les enfants d'Israël consultèrent l'Éternel, et dirent: Qui d'entre nous montera le premier contre les Cananéens pour les combattre?
2 Sai Ubangiji ya ce, “Yahuda zai tafi. Na riga na ba da ƙasar a hannunsu.”
Et l'Éternel répondit: Juda y montera; voici, j'ai livré le pays entre ses mains.
3 Sa’an nan mutane Yahuda suka ce wa mutanen Simeyon “Ku zo tare da mu a yankin da aka ba mu rabon mu don mu yaƙi Kan’aniyawa. Mu ma mu bi ku wurin naku.” Saboda haka mutanen Simeyon suka tafi tare da su.
Et Juda dit à Siméon, son frère: Monte avec moi dans mon lot, et nous combattrons les Cananéens; et j'irai aussi avec toi dans ton lot. Ainsi Siméon s'en alla avec lui.
4 Sa’ad da Yahuda ya fāɗa musu, Ubangiji kuwa ya ba da Kan’aniyawa da Ferizziyawa a hannunsu, suka kuwa kashe mutum dubu goma a Bezek.
Juda monta donc, et l'Éternel livra les Cananéens et les Phéréziens entre leurs mains, et ils battirent à Bézek dix mille hommes.
5 A can suka iske Adoni-Bezek, suka yaƙe shi, suka fatattaki Kan’aniyawa da Ferizziyawa.
Et, ayant trouvé Adoni-Bézek à Bézek, ils l'attaquèrent, et battirent les Cananéens et les Phéréziens.
6 Sai Adoni-Bezek ya gudu, amma suka bi shi suka kama shi, suka yayyanka manyan yatsotsinsa na hannu da na ƙafa.
Cependant Adoni-Bézek s'enfuit; mais ils le poursuivirent, le saisirent, et lui coupèrent les pouces des mains et des pieds.
7 Sa’an nan Adoni-Bezek ya ce, “Sarakuna saba’in waɗanda aka yayyanka manyan yatsotsinsu na hannu da na ƙafa, sun yi kalan abinci a ƙarƙashin teburina. Ga shi yanzu Allah ya rama abin da na yi musu.” Suka zo da shi Urushalima, a can kuwa ya mutu.
Alors Adoni-Bézek dit: Soixante et dix rois, dont les pouces des mains et des pieds avaient été coupés, recueillaient sous ma table ce qui en tombait. Ce que j'ai fait aux autres, Dieu me l'a rendu. Et, ayant été amené à Jérusalem, il y mourut.
8 Mutanen Yahuda suka yaƙi Urushalima ita ma suka ci ta. Suka karkashe mutanen birnin suka cinna mata wuta.
Or, les descendants de Juda attaquèrent Jérusalem, et la prirent; et l'ayant frappée du tranchant de l'épée, ils mirent le feu à la ville.
9 Bayan wannan, mutanen Yahuda suka gangara suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a ƙasar tudu, Negeb, da gindin tuddai a yammanci.
Ensuite les descendants de Juda descendirent pour combattre contre les Cananéens qui habitaient la montagne, et le midi, et la plaine.
10 Suka ci gaba suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a Hebron (wadda dā ake kira Kiriyat Arba) suka kuma ci Sheshai, Ahiman da Talmai da yaƙi.
Juda marcha contre les Cananéens qui habitaient à Hébron (or, le nom d'Hébron était auparavant Kirjath-Arba), et il battit Sheshaï, Ahiman et Talmaï;
11 Daga nan kuma suka ci gaba suka yaƙi mutanen da suke zaune a Debir (da ake kira a dā Kiriyat Sefer).
Et de là il marcha contre les habitants de Débir, dont le nom était auparavant Kirjath-Sépher.
12 Sai Kaleb ya ce, “Duk wanda ya fāɗa wa Kiriyat Sefer ya kuma ci ta da yaƙi, zan ba shi’yata Aksa yă aura.”
Et Caleb dit: Qui battra Kirjath-Sépher et la prendra, je lui donnerai ma fille Acsa pour femme.
13 Sai Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb ya ci birnin, saboda haka Kaleb ya ba shi’yarsa Aksa ya aura.
Alors Othniel, fils de Kénaz, frère puîné de Caleb, la prit; et Caleb lui donna pour femme sa fille Acsa.
14 Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ta zuga shi yă roƙi mahaifinta fili. Sa’ad da ta sauko daga jakinta, sai Kaleb ya ce mata, “Me zan yi miki?”
Et comme elle venait chez lui, elle l'incita à demander un champ à son père; et elle se jeta de dessus son âne, et Caleb lui dit: Qu'as-tu?
15 Sai ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman. Da yake ka ba ni ƙasa a Negeb, to, sai ka ba ni maɓulɓulan ruwa kuma.” Sai Kaleb ya ba ta maɓulɓulan bisa da kuma na ƙasa.
Et elle lui répondit: Donne-moi un présent; puisque tu m'as donné une terre du midi, donne-moi aussi des sources d'eaux. Et Caleb lui donna les sources supérieures, et les sources inférieures.
16 Zuriyar surukin Musa, Keniyawa, suka haura daga Birnin dabino tare da mutanen Yahuda don su zauna cikin mutanen Hamadan Yahuda a cikin Negeb kusa da Arad.
Or, les enfants du Kénien, beau-père de Moïse, montèrent de la ville des palmiers, avec les descendants de Juda, au désert de Juda, qui est au midi d'Arad; et ils allèrent, et demeurèrent avec le peuple.
17 Sa’an nan mutanen Yahuda suka tafi tare da’yan’uwansu mutanen Simeyon suka fāɗa wa Kan’aniyawan da suke zaune cikin Zefat, suka kuwa hallaka birnin gaba ɗaya. Saboda haka aka kira wurin Horma.
Puis Juda alla avec Siméon son frère, et ils battirent les Cananéens qui habitaient à Tséphath, et ils vouèrent ce lieu à l'interdit, et on appela la ville, Horma (Extermination).
18 Mutanen Yahuda kuma suka ci Gaza, Ashkelon, da Ekron, kowace birni tare da yankinsa.
Juda prit aussi Gaza avec son territoire, Askélon avec son territoire, et Ékron avec son territoire.
19 Ubangiji kuwa yana tare da mutane Yahuda. Suka mallaki ƙasar tudu, amma ba su iya suka kori mutanen daga filaye ba, domin suna da keken yaƙin ƙarfe.
Et l'Éternel fut avec Juda; et ils prirent possession de la montagne; mais ils ne dépossédèrent point les habitants de la vallée, parce qu'ils avaient des chars de fer.
20 Yadda Musa ya yi alkawari, sai aka ba Kaleb Hebron, wanda ya kori daga cikinta’ya’ya maza uku na Anak.
Et, selon que Moïse l'avait dit, on donna Hébron à Caleb, qui en déposséda les trois fils d'Anak.
21 Ko da yake mutanen Benyamin sun kāsa su kori Yebusiyawa, waɗanda suke zaune a Urushalima; har yă zuwa yau, Yebusiyawa suna zaune a can tare da mutanen Benyamin.
Quant aux descendants de Benjamin, ils ne dépossédèrent point les Jébusiens, qui habitaient à Jérusalem; aussi les Jébusiens ont habité avec les enfants de Benjamin, à Jérusalem, jusqu'à ce jour.
22 To, gidan Yusuf suka auka wa Betel, Ubangiji kuwa yana tare da su.
La maison de Joseph monta aussi contre Béthel, et l'Éternel fut avec eux.
23 Sa’ad da suka aike mutane don su leƙi asirin Betel (da dā ake kira Luz),
La maison de Joseph fit donc explorer Béthel, dont le nom était auparavant Luz;
24 ’yan leƙen asirin suka ga wani ya fito daga birnin sai suka ce masa, “Ka nuna mana yadda za mu shiga birnin, mu kuwa za mu yi maka alheri.”
Et les espions virent un homme, qui sortait de la ville, et ils lui dirent: Fais-nous voir, nous t'en prions, par où l'on peut entrer dans la ville, et nous te ferons grâce.
25 Saboda haka ya nuna musu, suka kuwa hallaka birnin, suka bar mutumin da dukan iyalinsa da rai.
Et il leur montra par où l'on pouvait entrer dans la ville, et ils la firent passer au fil de l'épée; mais ils laissèrent aller cet homme-là et toute sa famille.
26 Sa’an nan ya tafi ƙasar Hittiyawa, inda ya gina birni ya kuma kira shi Luz, haka ake kira birnin har wa yau.
Puis, cet homme se rendit au pays des Héthiens; il y bâtit une ville, et l'appela Luz, nom qu'elle a porté jusqu'à ce jour.
27 Amma Manasse ba su kori mutane Bet-Sheyan ko Ta’anak ko Dor ko Ibileyam ko Megiddo tare da ƙauyukansu ba, gama Kan’aniyawa sun dāge su zauna a wannan ƙasa.
Manassé ne déposséda point les habitants de Beth-Shéan et des villes de son ressort, ni les habitants de Thaanac et des villes de son ressort, ni les habitants de Dor et des villes de son ressort, ni les habitants de Jibléam et des villes de son ressort, ni les habitants de Méguiddo et des villes de son ressort; ainsi les Cananéens persistèrent à habiter ce pays-là.
28 Sa’ad da Isra’ila ta yi ƙarfi, sai suka tilasta Kan’aniyawa yin aikin gandu amma ba su kore su gaba ɗaya ba.
Cependant, quand Israël fut devenu plus fort, il rendit les Cananéens tributaires; mais il ne les chassa pas entièrement.
29 Haka Efraim ma bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Gezer ba, amma Kan’aniyawa suka ci gaba da zama tare da su.
Éphraïm ne déposséda point non plus les Cananéens qui habitaient à Guézer; mais les Cananéens habitèrent avec lui à Guézer.
30 Haka kuma Zebulun bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Kitron da Nahalol, waɗanda suka rage a cikinsu ba; sai dai sun sa su aikin gandu.
Zabulon ne déposséda point les habitants de Kitron, ni les habitants de Nahalol; et les Cananéens habitèrent avec lui, mais ils lui furent tributaires.
31 Haka Asher ma bai kori waɗanda suke zama a Akko ko Sidon ko Ahlab ko Akzib ko Helba ko Afik ko kuma Rehob ba,
Asser ne déposséda point les habitants d'Acco, ni les habitants de Sidon, ni d'Achlab, ni d'Aczib, ni d'Helba, ni d'Aphik, ni de Réhob;
32 kuma saboda wannan ne mutanen Asher suke zaune cikin mazaunan ƙasar Kan’aniyawa.
Mais ceux d'Asser habitèrent parmi les Cananéens, habitants du pays; car ils ne les dépossédèrent point.
33 Haka kuma Naftali bai kori waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh ko Bet-Anat; amma mutanen Naftali su ma suna zama a ciki Kan’aniyawa mazaunan ƙasar, waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh da Bet-Anat kuwa suka zama masu yi musu aikin gandu.
Nephthali ne déposséda point les habitants de Beth-Shémèsh, ni les habitants de Beth-Anath; mais il habita parmi les Cananéens, habitants du pays; et les habitants de Beth-Shémèsh et de Beth-Anath leur furent tributaires.
34 Amoriyawa suka matsa wa mutanen Dan a ƙasar tudu, ba su yarda musu su gangaro zuwa filaye ba.
Et les Amoréens resserrèrent dans la montagne les descendants de Dan, et ne les laissèrent point descendre dans la vallée.
35 Su Amoriyawa kuma suka dāge su zauna a Dutsen-Heres, Aiyalon, da Sha’albim. Amma yayinda mutanen Yusuf suka ƙara ƙarfi, sai suka su yin musu aikin gandu.
Et ces Amoréens persistèrent à demeurer à Har-Hérès, à Ajalon, et à Shaalbim; mais la main de la maison de Joseph pesa sur eux, et ils furent rendus tributaires.
36 Iyakar Amoriyawa kuwa daga Mashigin Kunama zuwa Sela da kuma zuwa gaba.
Or, le territoire des Amoréens s'étendait depuis la montée d'Akrabbim, depuis Séla (la Roche), et au-dessus.