< Yahuda 1 >

1 Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub, Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.
Judas, Jesu Kristi tjänare och Jakobs broder, hälsar de kallade, dem som äro upptagna i Guds, Faderns, kärlek och bevarade åt Jesus Kristus.
2 Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.
Barmhärtighet och frid och kärlek föröke sig hos eder.
3 Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak.
Mina älskade, då jag nu med all iver har tagit mig för att skriva till eder om vår gemensamma frälsning, finner jag det nödigt att i min skrivelse förmana eder att kämpa för den tro som en gång för alla har blivit meddelad åt de heliga.
4 Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.
Några människor hava nämligen innästlat sig hos eder -- några om vilka det för länge sedan blev skrivet att de skulle hemfalla under den domen -- ogudaktiga människor, som missbruka vår Guds nåd till lösaktighet och förneka vår ende härskare och herre, Jesus Kristus.
5 Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba.
Men fastän I redan en gång haven fått kunskap om alltsammans, vill jag påminna eder därom, att Herren, sedan han hade frälst sitt folk ur Egyptens land, efteråt förgjorde dem som icke trodde,
6 Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios g126)
så ock därom, att de änglar som icke behöllo sin furstehöghet, utan övergåvo sin boning, hava av honom med eviga bojor blivit förvarade i mörker till den stora dagens dom. (aïdios g126)
7 Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios g166)
Likaså hava ock Sodom och Gomorra med kringliggande städer, vilka på samma sätt som de förra bedrevo otukt och stodo efter annat umgänge än det naturliga, blivit satta till ett varnande exempel, i det att de få lida straff i evig eld. (aiōnios g166)
8 Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama.
Dock göra nu också dessa människor på samma sätt, förblindade av sina drömmar: köttet besmitta de, men andevärldens herrar förakta de, och dess härlige smäda de.
9 Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!”
Icke så Mikael, överängeln; när denne tvistade med djävulen angående Moses' kropp, dristade han sig icke att över honom uttala någon smädande dom, utan sade allenast: »Herren näpse dig.»
10 Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.
Dessa åter smäda vad de icke känna till; och vad de, likasom de oskäliga djuren, med sina naturliga sinnen kunna fatta, det bruka de till sitt fördärv.
11 Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.
Ve dem! De hava trätt in på Kains väg, de hava för löns skull störtat sig i Balaams villfarelse och hava gått förlorade till följd av en gensträvighet lik Koras.
12 Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus.
Det är dessa som få hålla gästabud med eder, där de sitta såsom skamfläckar vid edra kärleksmåltider och oförsynt se sig själva till godo. De äro skyar utan vatten, skyar som drivas bort av vindarna. De äro träd som stå nakna på senhösten, ofruktbara, i dubbel måtto döda, uppryckta med rötterna.
13 Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn g165)
De äro vilda havsvågor som uppkasta sina egna skändligheters skum. De äro irrande stjärnor, åt vilka det svarta mörkret är förvarat till evig tid. (aiōn g165)
14 Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa
Om dessa var det ock som Enok, den sjunde från Adam, profeterade och sade: »Se, Herren kommer med sina mångtusen heliga,
15 don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.”
för att hålla dom över alla och bestraffa alla de ogudaktiga för alla de ogudaktiga gärningar som de hava övat, och för alla de förmätna ord som de i sin syndiga ogudaktighet hava talat mot honom.»
16 Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.
De äro människor som alltid knorra och knota över sin lott, medan de likväl vandra efter sina egna begärelser. Och deras mun talar stora ord, under det att de dock av egennytta söka vara människor till behag.
17 Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā.
Men kommen ihåg, I mina älskade, vad som har blivit förutsagt av vår Herres, Jesu Kristi, apostlar,
18 Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.”
huru de sade till eder: »I den yttersta tiden skola bespottare uppstå, som vandra efter sina egna ogudaktiga begärelser.»
19 Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.
Det är dessa människor som vålla söndringar, dessa som äro »själiska» och icke hava ande.
20 Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki.
Men I, mina älskade, uppbyggen eder på eder allraheligaste tro, bedjen i den helige Ande,
21 Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios g166)
och bevaren eder så i Guds kärlek, under det att I vänten på vår Herres, Jesu Kristi, barmhärtighet, till evigt liv. (aiōnios g166)
22 Ku ji tausayin waɗanda suke shakka;
Mot somliga av dem, sådana som äro tvivlande, mån I vara barmhärtiga
23 ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.
och frälsa dem genom att rycka dem ur elden; mot de andra mån I också vara barmhärtiga, dock med fruktan, så att I avskyn till och med deras livklädnad, den av köttet befläckade.
24 To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki.
Men honom som förmår bevara eder ifrån fall och ställa eder inför sin härlighet ostraffliga, i fröjd,
25 Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn g165)
honom som allena är Gud, och som är vår Frälsare genom Jesus Kristus, vår Herre, honom tillhör ära, majestät, välde och makt, såsom före all tid, så ock nu och i alla evigheter. Amen. Se Själisk i Ordförkl (aiōn g165)

< Yahuda 1 >