< Yahuda 1 >
1 Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub, Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.
Jude, a servant of Jesus Christ, and brother of James, to those who are beloved in God the Father, and who are guarded and called in Jesus Christ:
2 Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.
May mercy, and peace, and love be fulfilled in you.
3 Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak.
Most beloved, taking all care to write to you about your common salvation, I found it necessary to write to you in order to beg you to contend earnestly for the faith that was handed down once to the saints.
4 Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.
For certain men entered unnoticed, who were written of beforehand unto this judgment: impious persons who are transforming the grace of our God into self-indulgence, and who are denying both the sole Ruler and our Lord Jesus Christ.
5 Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba.
So I want to caution you. Those who once knew everything that Jesus did, in saving the people from the land of Egypt, afterwards perished because they did not believe.
6 Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios )
And truly, the Angels, who did not keep to their first place, but instead abandoned their own domiciles, he has reserved with perpetual chains under darkness, unto the great day of judgment. (aïdios )
7 Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios )
And also Sodom and Gomorrah, and the adjoining cities, in similar ways, having given themselves over to fornication and to the pursuing of other flesh, were made an example, suffering the punishment of eternal fire. (aiōnios )
8 Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama.
Similarly also, these ones certainly defile the flesh, and they despise proper authority, and they blaspheme against majesty.
9 Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!”
When Michael the Archangel, disputing with the devil, contended about the body of Moses, he did not dare to bring against him a judgment of blasphemy, so instead he said: “The Lord commands you.”
10 Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.
But these men certainly blaspheme against whatever they do not understand. And yet, whatever they, like mute animals, know from nature, in these things they are corrupted.
11 Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.
Woe to them! For they have gone after the way of Cain, and they have poured out the error of Balaam for profit, and they have perished in the sedition of Korah.
12 Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus.
These ones are defiled within their banquets, enjoying themselves and feeding themselves without fear; waterless clouds, which are tossed about by winds; autumn trees, unfruitful, twice dead, uprooted;
13 Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn )
raging waves of the sea, foaming from their own confusion; wandering stars, for whom the whirlwind of darkness has been reserved forever! (aiōn )
14 Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa
And about these, Enoch, the seventh from Adam, also prophesied, saying: “Behold, the Lord is arriving with thousands of his saints,
15 don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.”
to execute judgment against everyone, and to reprove all the impious concerning all the works of their impiety, by which they have acted impiously, and concerning all the harsh things that impious sinners have spoken against God.”
16 Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.
These ones are complaining murmurers, walking according to their own desires. And their mouth is speaking arrogance, admiring persons for the sake of gain.
17 Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā.
But as for you, most beloved, be mindful of the words which have been foretold by the Apostles of our Lord Jesus Christ,
18 Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.”
who declared to you that, in the end time, there would arrive mockers, walking according to their own desires, in impieties.
19 Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.
These are the ones who segregate themselves; they are animals, not having the Spirit.
20 Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki.
But you, most beloved, are building yourselves up by your most holy faith, praying in the Holy Spirit,
21 Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios )
keeping yourselves in the love of God, and anticipating the mercy of our Lord Jesus Christ unto eternal life. (aiōnios )
22 Ku ji tausayin waɗanda suke shakka;
So certainly, reprove them, after they have been judged.
23 ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.
Yet truly, save them, seizing them from the fire. And have mercy on others: in fear, hating even that which is of the flesh, the defiled garment.
24 To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki.
Then, to him who has the power to keep you free from sin and to present you, immaculate, with exultation, before the presence of his glory at the advent of our Lord Jesus Christ,
25 Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn )
to the only God, our Savior, through Jesus Christ our Lord: to him be glory and magnificence, dominion and power, before all ages, and now, and in every age, forever. Amen. (aiōn )