< Yahuda 1 >

1 Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub, Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.
Иуда, Иисуса Христа раб, брат же Иакова, сущым о Бозе Отце освященным, Иисус Христом соблюденным званным:
2 Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.
милость вам и мир и любы да умножится.
3 Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak.
Возлюбленнии, всяко тщание творя писати вам о общем спасении вашем, нужду возимех писати вам, моля подвизатися о преданнеи вере святым единою.
4 Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.
Привнидоша бо нецыи человецы, древле предуставленнии на сие осуждение, нечестивии, Бога нашего благодать прелагающии в скверну, и единаго Владыки Бога и Господа нашего Иисуса Христа отметающиися.
5 Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba.
Воспомянути же вам хощу, ведущым и вам единою сие, яко Господь люди от земли Египетския спасе, последи неверовавшыя погуби:
6 Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios g126)
аггелы же не соблюдшыя своего начальства, но оставльшыя свое жилище, на суд великаго дне узами вечными под мраком соблюде. (aïdios g126)
7 Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios g166)
Якоже Содома и Гоморра и окрестнии их грады, подобным им образом преблудивше и ходивше вслед плоти иныя, предлежат в показание, огня вечнаго суд подемше, (aiōnios g166)
8 Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama.
такожде убо и сии, сония видяще, плоть убо сквернят, господства же отметаются, славы же хуляще (не трепещут).
9 Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!”
Михаил же Архангел, егда со диаволом разсуждая глаголаше о Моисеове телеси, не смеяше суда навести хульна, но рече: да запретит тебе Господь.
10 Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.
Сии же, елика убо не ведят, хулят: елика же по естеству яко безсловесная животная ведят, в сих сквернятся.
11 Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.
Горе им. Яко в путь Каинов поидоша, и в лесть Валаамовы мзды устремишася, и в пререкании Корреове погибоша.
12 Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus.
Сии суть в любвах ваших сквернители, с вами ядуще, без боязни себе пасуще: облацы безводни, от ветр преносими: древеса есенна, безплодна, дважды умерша, искоренена.
13 Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn g165)
Волны свирепыя моря, воспеняющя своя стыдения: звезды прелестныя, имже мрак тьмы во веки блюдется. (aiōn g165)
14 Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa
Пророчествова же и о сих седмый от Адама Енох, глаголя: се приидет Господь во тьмах святых Ангел Своих,
15 don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.”
сотворити суд о всех и изобличити всех нечестивых о всех делех нечестия их, имиже нечествоваша, и о всех жестоких словесех их, яже глаголаша Нань грешницы нечестивии.
16 Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.
Сии суть ропотницы, укорители, (часть порочна, ) в похотех своих ходяще нечестием и законопреступлением: и уста их глаголют прегордая: чудящеся лицам пользы ради.
17 Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā.
Вы же, возлюбленнии, поминайте глаголы преждереченныя от Апостол Господа нашего Иисуса Христа.
18 Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.”
Зане глаголаху вам, яко в последнее время будут ругатели, по своих похотех ходяще и нечестиих.
19 Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.
Сии суть отделяюще себе (от единости веры, и суть) телесни, духа не имуще.
20 Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki.
Вы же, возлюбленнии, стою вашею верою назидающе себе, Духом Святым молящеся,
21 Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios g166)
сами себе в любви Божиеи соблюдайте, ждуще милости Господа нашего Иисуса Христа, в жизнь вечную. (aiōnios g166)
22 Ku ji tausayin waɗanda suke shakka;
И овех убо милуйте разсуждающе.
23 ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.
Овех же страхом спасайте, от огня восхищающе. Обличайте же с боязнию, ненавидяще и яже от плоти оскверненую ризу.
24 To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki.
Могущему же сохранити вы без греха и без скверны и поставити пред славою Своею непорочных в радости,
25 Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn g165)
Единому Премудрому Богу и Спасу нашему, Иисусом Христом Господем нашим, слава и величие, держава и власть, прежде всего века, и ныне, и во вся веки. Аминь. (aiōn g165)

< Yahuda 1 >