< Yahuda 1 >

1 Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub, Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.
ยีศุขฺรีษฺฏสฺย ทาโส ยากูโพ ภฺราตา ยิหูทาสฺตาเตเนศฺวเรณ ปวิตฺรีกฺฤตานฺ ยีศุขฺรีษฺเฏน รกฺษิตำศฺจาหูตานฺ โลกานฺ ปฺรติ ปตฺรํ ลิขติฯ
2 Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.
กฺฤปา ศานฺติ: เปฺรม จ พาหุลฺยรูเปณ ยุษฺมาสฺวธิติษฺฐตุฯ
3 Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak.
เห ปฺริยา: , สาธารณปริตฺราณมธิ ยุษฺมานฺ ปฺรติ เลขิตุํ มม พหุยตฺเน ชาเต ปูรฺวฺวกาเล ปวิตฺรโลเกษุ สมรฺปิโต โย ธรฺมฺมสฺตทรฺถํ ยูยํ ปฺราณวฺยเยนาปิ สเจษฺฏา ภวเตติ วินยารฺถํ ยุษฺมานฺ ปฺรติ ปตฺรเลขนมาวศฺยกมฺ อมเนฺยฯ
4 Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.
ยสฺมาทฺ เอตทฺรูปทณฺฑปฺราปฺตเย ปูรฺวฺวํ ลิขิตา: เกจิชฺชนา อสฺมานฺ อุปสฺฤปฺตวนฺต: , เต 'ธารฺมฺมิกโลกา อสฺมากมฺ อีศฺวรสฺยานุคฺรหํ ธฺวชีกฺฤตฺย ลมฺปฏตามฺ อาจรนฺติ, อทฺวิตีโย 'ธิปติ โรฺย 'สฺมากํ ปฺรภุ รฺยีศุขฺรีษฺฏสฺตํ นางฺคีกุรฺวฺวนฺติฯ
5 Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba.
ตสฺมาทฺ ยูยํ ปุรา ยทฺ อวคตาสฺตตฺ ปุน รฺยุษฺมานฺ สฺมารยิตุมฺ อิจฺฉามิ, ผลต: ปฺรภุเรกกฺฤตฺว: สฺวปฺรชา มิสรเทศาทฺ อุทธาร ยตฺ ตต: ปรมฺ อวิศฺวาสิโน วฺยนาศยตฺฯ
6 Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios g126)
เย จ สฺวรฺคทูตา: สฺวียกรฺตฺฤตฺวปเท น สฺถิตฺวา สฺววาสสฺถานํ ปริตฺยกฺตวนฺตสฺตานฺ ส มหาทินสฺย วิจารารฺถมฺ อนฺธการมเย 'ธ: สฺถาเน สทาสฺถายิภิ รฺพนฺธไนรพธฺนาตฺฯ (aïdios g126)
7 Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios g166)
อปรํ สิโทมมฺ อโมรา ตนฺนิกฏสฺถนคราณิ ไจเตษำ นิวาสินสฺตตฺสมรูปํ วฺยภิจารํ กฺฤตวนฺโต วิษมไมถุนสฺย เจษฺฏยา วิปถํ คตวนฺตศฺจ ตสฺมาตฺ ตานฺยปิ ทฺฤษฺฏานฺตสฺวรูปาณิ ภูตฺวา สทาตนวหฺนินา ทณฺฑํ ภุญฺชเตฯ (aiōnios g166)
8 Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama.
ตไถเวเม สฺวปฺนาจาริโณ'ปิ สฺวศรีราณิ กลงฺกยนฺติ ราชาธีนตำ น สฺวีกุรฺวฺวนฺตฺยุจฺจปทสฺถานฺ นินฺทนฺติ จฯ
9 Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!”
กินฺตุ ปฺรธานทิวฺยทูโต มีขาเยโล ยทา มูสโส เทเห ศยตาเนน วิวทมาน: สมภาษต ตทา ติสฺมนฺ นินฺทารูปํ ทณฺฑํ สมรฺปยิตุํ สาหสํ น กฺฤตฺวากถยตฺ ปฺรภุสฺตฺวำ ภรฺตฺสยตำฯ
10 Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.
กินฺตฺวิเม ยนฺน พุธฺยนฺเต ตนฺนินฺทนฺติ ยจฺจ นิรฺพฺโพธปศว อิเวนฺทฺริไยรวคจฺฉนฺติ เตน นศฺยนฺติฯ
11 Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.
ตานฺ ธิกฺ, เต กาพิโล มารฺเค จรนฺติ ปาริโตษิกสฺยาศาโต พิลิยโม ภฺรานฺติมนุธาวนฺติ โกรหสฺย ทุรฺมฺมุขเตฺวน วินศฺยนฺติ จฯ
12 Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus.
ยุษฺมากํ เปฺรมโภเชฺยษุ เต วิฆฺนชนกา ภวนฺติ, อาตฺมมฺภรยศฺจ ภูตฺวา นิรฺลชฺชยา ยุษฺมาภิ: สารฺทฺธํ ภุญฺชเตฯ เต วายุภิศฺจาลิตา นิโสฺตยเมฆา เหมนฺตกาลิกา นิษฺผลา ทฺวิ รฺมฺฤตา อุนฺมูลิตา วฺฤกฺษา: ,
13 Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn g165)
สฺวกียลชฺชาเผโณทฺวมกา: ปฺรจณฺฑา: สามุทฺรตรงฺคา: สทากาลํ ยาวตฺ โฆรติมิรภาคีนิ ภฺรมณการีณิ นกฺษตฺราณิ จ ภวนฺติฯ (aiōn g165)
14 Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa
อาทมต: สปฺตม: ปุรุโษ โย หโนก: ส ตานุทฺทิศฺย ภวิษฺยทฺวากฺยมิทํ กถิตวานฺ, ยถา, ปศฺย สฺวกียปุณฺยานามฺ อยุไต เรฺวษฺฏิต: ปฺรภุ: ฯ
15 don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.”
สรฺวฺวานฺ ปฺรติ วิจาราชฺญาสาธนายาคมิษฺยติฯ ตทา จาธารฺมฺมิกา: สรฺเวฺว ชาตา ไยรปราธิน: ฯ วิธรฺมฺมกรฺมฺมณำ เตษำ สรฺเวฺวษาเมว การณาตฺฯ ตถา ตไทฺวปรีเตฺยนาปฺยธรฺมฺมาจาริปาปินำฯ อุกฺตกโฐรวากฺยานำ สรฺเวฺวษามปิ การณาตฺฯ ปรเมเศน โทษิตฺวํ เตษำ ปฺรกาศยิษฺยเต๚
16 Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.
เต วากฺกลหการิณ: สฺวภาคฺยนินฺทกา: เสฺวจฺฉาจาริโณ ทรฺปวาทิมุขวิศิษฺฏา ลาภารฺถํ มนุษฺยสฺตาวกาศฺจ สนฺติฯ
17 Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā.
กินฺตุ เห ปฺริยตมา: , อสฺมากํ ปฺรโภ รฺยีศุขฺรีษฺฏสฺย เปฺรริไต รฺยทฺ วากฺยํ ปูรฺวฺวํ ยุษฺมภฺยํ กถิตํ ตตฺ สฺมรต,
18 Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.”
ผลต: เศษสมเย เสฺวจฺฉาโต 'ธรฺมฺมาจาริโณ นินฺทกา อุปสฺถาสฺยนฺตีติฯ
19 Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.
เอเต โลกา: สฺวานฺ ปฺฤถกฺ กุรฺวฺวนฺต: สำสาริกา อาตฺมหีนาศฺจ สนฺติฯ
20 Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki.
กินฺตุ เห ปฺริยตมา: , ยูยํ เสฺวษามฺ อติปวิตฺรวิศฺวาเส นิจียมานา: ปวิเตฺรณาตฺมนา ปฺรารฺถนำ กุรฺวฺวนฺต
21 Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios g166)
อีศฺวรสฺย เปฺรมฺนา สฺวานฺ รกฺษต, อนนฺตชีวนาย จาสฺมากํ ปฺรโภ รฺยีศุขฺรีษฺฏสฺย กฺฤปำ ปฺรตีกฺษธฺวํฯ (aiōnios g166)
22 Ku ji tausayin waɗanda suke shakka;
อปรํ ยูยํ วิวิจฺย กำศฺจิทฺ อนุกมฺปธฺวํ
23 ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.
กำศฺจิทฺ อคฺนิต อุทฺธฺฤตฺย ภยํ ปฺรทรฺศฺย รกฺษต, ศารีริกภาเวน กลงฺกิตํ วสฺตฺรมปิ ฤตียธฺวํฯ
24 To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki.
อปรญฺจ ยุษฺมานฺ สฺขลนาทฺ รกฺษิตุมฺ อุลฺลาเสน สฺวียเตชส: สากฺษาตฺ นิรฺทฺโทษานฺ สฺถาปยิตุญฺจ สมรฺโถ
25 Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn g165)
โย 'สฺมากมฺ อทฺวิตียสฺตฺราณกรฺตฺตา สรฺวฺวชฺญ อีศฺวรสฺตสฺย เคารวํ มหิมา ปรากฺรม: กรฺตฺฤตฺวญฺเจทานีมฺ อนนฺตกาลํ ยาวทฺ ภูยาตฺฯ อาเมนฺฯ (aiōn g165)

< Yahuda 1 >