< Yahuda 1 >

1 Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub, Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.
Juda, sługa Jezusa Chrystusa, a brat Jakuba, do uświęconych przez Boga Ojca, zachowanych w Jezusie Chrystusie i powołanych:
2 Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.
Miłosierdzie, pokój i miłość niech się wam pomnożą.
3 Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak.
Umiłowani, podejmując usilne starania, aby pisać wam o wspólnym zbawieniu, uznałem za konieczne napisać do was i zachęcić do walki o wiarę raz przekazaną świętym.
4 Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.
Wkradli się bowiem pewni ludzie, od dawna przeznaczeni na to potępienie, bezbożni, którzy łaskę naszego Boga zamieniają na rozpustę i wypierają się jedynego Pana Boga i naszego Pana Jezusa Chrystusa.
5 Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba.
Chcę więc wam przypomnieć, chociaż już kiedyś o tym wiedzieliście, że Pan, który wybawił lud z ziemi Egiptu, potem wytracił tych, którzy nie uwierzyli.
6 Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios g126)
Także aniołów, którzy nie zachowali swego pierwotnego stanu, lecz opuścili własne mieszkanie, zatrzymał w wiecznych pętach w ciemnościach na sąd wielkiego dnia. (aïdios g126)
7 Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios g166)
Tak samo Sodoma i Gomora oraz okoliczne miasta, które w podobny sposób jak i one oddały się nierządowi i podążały za cudzym ciałem, służą za przykład, ponosząc karę wiecznego ognia. (aiōnios g166)
8 Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama.
Podobnie ci [ludzie] rojący sny plugawią ciało, gardzą panowaniem i bluźnią przełożonym.
9 Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!”
Lecz archanioł Michał, rozprawiając z diabłem, spierał się o ciało Mojżesza, nie ośmielił się wypowiedzieć [przeciwko niemu] bluźnierczego oskarżenia, ale powiedział: Niech cię Pan zgromi.
10 Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.
Ci zaś bluźnią przeciwko temu, czego nie znają, a to, co znają w sposób naturalny, jak bezrozumne zwierzęta, w tym psują samych siebie.
11 Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.
Biada im, bo poszli drogą Kaina, udali się za błędem Baalama dla zapłaty i zginęli w buncie Korego.
12 Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus.
Oni są zakałami na waszych ucztach braterskich, którzy z wami bez bojaźni ucztują, pasąc samych siebie. Są to bezwodne chmury wiatrami unoszone; drzewa zwiędłe, bez owoców, dwukrotnie obumarłe i wykorzenione;
13 Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn g165)
Rozhukane fale morskie wypluwające swoją hańbę; błąkające się gwiazdy, dla których mroki ciemności zachowane są na wieki. (aiōn g165)
14 Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa
O nich też prorokował Henoch, siódmy po Adamie, mówiąc: Oto idzie Pan z tysiącami swoich świętych;
15 don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.”
Aby dokonać sądu nad wszystkimi i ukarać wszystkich bezbożników spośród nich za wszystkie ich bezbożne czyny, których się bezbożnie dopuścili, i za wszystkie ostre [słowa], które wypowiadali przeciwko niemu bezbożni grzesznicy.
16 Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.
Oni to zawsze szemrają, narzekają, postępują według swoich pożądliwości. Ich usta wypowiadają zuchwałe [słowa] i schlebiają ludziom dla korzyści.
17 Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā.
Wy zaś, umiłowani, pamiętajcie słowa wcześniej wypowiedziane przez apostołów naszego Pana Jezusa Chrystusa;
18 Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.”
Gdy mówili do was, że w czasach ostatecznych pojawią się szydercy, postępujący według własnych bezbożnych pożądliwości.
19 Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.
Oni są tymi, którzy sami się odłączają, zmysłowi, niemający Ducha.
20 Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki.
Wy jednak, umiłowani, budując samych siebie na waszej najświętszej wierze, modląc się w Duchu Świętym;
21 Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios g166)
Zachowajcie samych siebie w miłości Boga, oczekując miłosierdzia naszego Pana Jezusa Chrystusa ku życiu wiecznemu. (aiōnios g166)
22 Ku ji tausayin waɗanda suke shakka;
I rozróżniając, nad jednymi zmiłujcie się;
23 ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.
Innych zaś ratujcie przez strach, wyrywając ich z ognia, mając w nienawiści nawet szatę, która została skalana przez ciało.
24 To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki.
A temu, który może was ustrzec od upadku i z radością przedstawić jako nienagannych przed obliczem swojej chwały;
25 Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn g165)
Jedynemu mądremu Bogu, naszemu Zbawicielowi, [niech będzie] chwała i majestat, moc i władza, teraz i po wszystkie wieki. Amen. (aiōn g165)

< Yahuda 1 >