< Yahuda 1 >
1 Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub, Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.
Judas, Jesu Kristi tjener og Jakobs bror - til de kalte, som er elsket i Gud Fader og bevart for Jesus Kristus:
2 Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.
Miskunn og fred og kjærlighet bli eder mangfoldig til del!
3 Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak.
I elskede! mens jeg gjorde mig all flid for å skrive til eder om vår felles frelse, så jeg mig nødt til å skrive til eder med formaning om å stride for den tro som én gang er overgitt til de hellige.
4 Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.
For nogen mennesker har sneket sig inn, som denne dom allerede for lenge siden er opskrevet for: ugudelige, som forvender vår Guds nåde til skamløshet og nekter vår eneste hersker og herre, Jesus Kristus.
5 Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba.
Men da I nu engang vet alt, vil jeg minne eder om at Herren, efterat han hadde frelst folket ut av Egyptens land, siden ødela dem som ikke trodde,
6 Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios )
og om at de engler som ikke tok vare på sin høie stand, men forlot sin egen bolig, dem holder han i varetekt i evige lenker under mørket til dommen på den store dag; (aïdios )
7 Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios )
likesom Sodoma og Gomorra og byene deromkring, som på samme måte som disse drev hor og gikk efter fremmed kjød, ligger for våre øine som et eksempel, idet de lider en evig ilds straff. (aiōnios )
8 Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama.
Og dog gjør også disse like ens: idet de går i drømme, gjør de kjødet urent, ringeakter herredømme, spotter høie makter.
9 Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!”
Overengelen Mikael vågde dog ikke å uttale en spottende dom dengang han trettet med djevelen om Mose legeme, men sa: Herren refse dig!
10 Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.
Disse derimot spotter det de ikke kjenner; men det de av naturen skjønner, likesom de ufornuftige dyr, med det ødelegger de sig.
11 Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.
Ve dem! for de har gått Kains vei og for vinnings skyld kastet sig inn i Bileams forvillelse og er gått under ved Korahs gjenstridighet.
12 Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus.
Disse er skamflekkene ved eders kjærlighets-måltider, uten blygsel holder de gilde med eder og forer sig selv; vannløse skyer som drives avsted av vinden; trær, nakne som om høsten, ufruktbare, to ganger død, oprykket med rot;
13 Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn )
ville havsbårer som utskummer sin egen skam; villfarende stjerner, for hvem mørkets natt er rede til evig tid. (aiōn )
14 Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa
Disse var det også Enok, den syvende fra Adam, spådde om da han sa: Se, Herren kommer med sine mange tusen hellige
15 don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.”
for å holde dom over alle og refse alle de ugudelige for alle de ugudelige gjerninger som de gjorde, og for alle de hårde ord som de talte mot ham, de ugudelige syndere.
16 Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.
Disse er folk som knurrer og klager over sin skjebne, enda de farer frem efter sine lyster, og deres munn taler skrytende ord, enda de smigrer for folk for vinnings skyld.
17 Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā.
Men I, elskede, kom i hu de ord som forut er talt av vår Herre Jesu Kristi apostler,
18 Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.”
hvorledes de sa til eder at det i den siste tid skal komme spottere som farer frem efter sine ugudelige lyster!
19 Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.
Disse er de som skiller sig ut, naturlige mennesker, som ikke har ånd.
20 Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki.
Men I, elskede, opbygg eder på eders høihellige tro, bed i den Hellige Ånd,
21 Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios )
og hold eder således i Guds kjærlighet, mens I venter på vår Herre Jesu Kristi miskunn til evig liv! (aiōnios )
22 Ku ji tausayin waɗanda suke shakka;
Og nogen skal I tale til rette fordi de tviler,
23 ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.
andre skal I frelse ved å rive dem ut av ilden, andre igjen skal I miskunne eder over med frykt, idet I hater endog den av kjødet smittede kjortel.
24 To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki.
Men ham som er mektig til å verne om eder, så I ikke snubler, og å stille eder lyteløse frem for sin herlighet i fryd,
25 Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn )
den eneste Gud, vår frelser ved Jesus Kristus, vår Herre, ham tilhører herlighet, storhet, styrke og makt før all tid og nu og i all evighet. Amen. (aiōn )