< Yahuda 1 >
1 Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub, Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.
Surat ini ditulis oleh Yudas, pelayan dari Yesus Kristus, dan saudara Yakobus. Saya menuliskan ini untuk mereka yang dipanggil dan dikasihi oleh Allah Bapa, dan dilindungi oleh Yesus Kristus:
2 Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.
Kiranya belas kasihan, damai, dan kasih Allah semakin bertambah dalam perjalanan hidupmu!
3 Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak.
Teman-teman, saya sudah menanti-nantikan untuk menuliskan tentang berita keselamatan yang kita bagikan. Tetapi saat ini saya perlu segera menulis kepada kalian dan menguatkan kalian untuk membela kebenaran tentang Allah dengan penuh semangat, yang diberikan sekali dan untuk selamanya kepada umat Allah yang kudus.
4 Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.
Bagi sebagian orang telah diam-diam menyusup di antara kalian Mereka ditulis dan dikutuk sejak lama, karena mereka adalah orang-orang jahat yang memutarbalikkan kasih karunia Allah, mengubahnya menjadi izin untuk amoralitas, sementara juga menyangkal Tuhan dan tuan kita Yesus Kristus.
5 Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba.
Sekalipun kalian sudah tahu akan hal ini, saya ingin mengingatkan kalian bahwa sekalipun Tuhan menyelamatkan umat-Nya keluar dari negeri Mesir, dia masih membinasakan mereka yang tidak percaya kepada-Nya.
6 Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios )
Bahkan para malaikat yang tidak puas dengan posisi yang Allah berikan kepada mereka dan meninggalkan posisi mereka yang benar — ditempatkannya mereka di dalam kegelapan dengan rantai kekekalan sampai pada hari Penghakiman Besar. (aïdios )
7 Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios )
Dengan cara yang sama, Sodom dan Gomora dan kota-kota di sekitarnya yang mengejar amoralitas dan seks sesat diberikan sebagai contoh dari mereka yang mengalami hukuman api abadi. (aiōnios )
8 Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama.
Dengan cara yang sama, para pemimpi ini mengotori tubuh jasmani mereka, meremehkan otoritas, dan menghina mahkluk-mahkluk surgawi.
9 Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!”
Bahkan Mikael, pemimpin tertinggi malaikat, ketika dia berdebat dengan Iblis mengenai mayat Musa, tidak berani mendakwa Iblis dengan hinaan seperti itu, hanya berkata, “Semoga Tuhan menghardik kamu.”
10 Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.
Tetapi orang-orang ini mengejek apa pun yang tidak mereka pahami; dan apa yang mereka pahami secara naluriah mereka ikuti seperti binatang yang tidak berpikir — inilah yang menghancurkan mereka.
11 Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.
Mereka dalam kesulitan besar! Karena mereka sudah mengikuti cara Kain. Seperti Bileam dan khayalannya, mereka tersesat karena gila uang. Seperti Korah dan pemberontakannya, mereka menghancurkan diri mereka sendiri.
12 Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus.
Orang-orang ini merusak makanan persekutuan kalian, karena mereka seperti para gembala yang egois yang tidak memiliki rasa malu sedikit pun — mereka hanya menjaga diri sendiri. Mereka seperti awan yang tertiup angin tetapi tidak membawa hujan. Mereka seperti pohon gundul tanpa buah — mati dua kali, dicabut dari akarnya.
13 Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn )
Mereka seperti gelombang laut yang ganas, berbuih dalam aib mereka sendiri. Mereka seperti bintang-bintang palsu, dikutuk selamanya ke dalam kegelapan total. (aiōn )
14 Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa
Henokh, tujuh generasi sesudah Adam, sudah bernubuat tentang orang-orang ini: “Lihat! Tuhan akan datang, bersama dengan jutaan orang suci-Nya
15 don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.”
untuk menghakimi semua orang, untuk mengungkapkan semua perbuatan jahat yang sudah dilakukan orang-orang, dan semua hal mengerikan yang dikatakan orang-orang berdosa yang bermusuhan terhadap-Nya.”
16 Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.
Orang seperti itu penggerutu, selalu mengeluh. Mereka mengikuti keinginan jahat mereka sendiri, berbicara dengan sombong tentang diri mereka sendiri, dan menyanjung orang lain untuk mendapatkan apa yang mereka inginkan.
17 Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā.
Tetapi kalian, teman-teman terkasih, mohon ingat apa yang para rasul Tuhan kita Yesus Kristus katakan kepada kalian.
18 Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.”
Mereka menjelaskan kepadamu bahwa pada saat-saat terakhir para pengejek akan datang, mengikuti keinginan jahat mereka sendiri.
19 Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.
Mereka menyebabkan perpecahan; mereka adalah orang-orang duniawi yang tidak memiliki Roh.
20 Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki.
Tetapi kalian, teman-teman saya, haruslah membangun diri kalian sendiri melalui keyakinan kalian kepada Allah. Berdoa dalam Roh Kudus,
21 Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios )
jaga dirimu aman dalam kasih Tuhan, dan nantikan pengampunan Allah kita Yesus Kristus yang membawa kita kepada hidup yang untuk selama-lamanya. (aiōnios )
22 Ku ji tausayin waɗanda suke shakka;
Tunjukkan kebaikan hati kepada orang yang ragu.
23 ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.
Selamatkan mereka yang bisa kalian selamatkan dengan mengeluarkan mereka dari api. Tunjukkan pengampunan — tetapi dengan sangat hati-hati, bahkan membenci “tampilan luar” yang terkontaminasi oleh sifat manusia yang berdosa.
24 To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki.
Sekarang bagi Dia yang dapat mencegah kita agar tidak jatuh dalam dosa, dan yang dapat membawa kita ke dalam kehadiran-Nya yang mulia tanpa dosa, dan dengan sukacita yang besar,
25 Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn )
kepada satu-satunya Allah Juruselamat kita, melalui Yesus Kristus Tuhan kita, biarlah kemuliaan, keagungan, kuasa, dan otoritas, dahulu, sekarang, dan selamanya. Amin. (aiōn )