< Yahuda 1 >

1 Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub, Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.
ⲁ̅ⲓⲟⲩⲇⲁⲥ ⲡϩⲙ̅ϩⲁⲗ ⲛ̅ⲓⲥ̅ ⲡⲉⲭⲥ̅. ⲡⲥⲟⲛ ⲇⲉ ⲛ̅ⲓⲁⲕⲱⲃⲟⲥ ⲉϥⲥϩⲁⲓ ⲙ̅ⲙⲉⲣⲁⲧⲉ ⲉⲧϩⲙ̅ⲡⲛⲟⲩⲧⲉ ⲡⲉⲓⲱⲧ. ⲛⲉⲧⲧⲁϩⲙ̅ ⲉⲧⲟⲩϩⲁⲣⲉϩ ⲉⲣⲟⲟⲩ ϩⲛ̅ⲓⲥ̅ ⲡⲉⲭⲥ̅.
2 Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.
ⲃ̅ⲡⲛⲁ ⲉϥⲉⲁϣⲁⲓ ⲛⲏⲧⲛ̅ ⲁⲩⲱ ⲧⲁⲅⲁⲡⲏ ⲙⲛ̅ϯⲣⲏⲛⲏ.
3 Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak.
ⲅ̅ⲛⲁⲙⲉⲣⲁⲧⲉ. ⲉⲓⲉⲓⲣⲉ ⲛ̅ⲁⲡⲁⲧⲟⲟⲧ ⲉⲙⲁⲧⲉ ⲉⲧⲣⲁⲥϩⲁⲓ ⲛⲏⲧⲛ̅ ⲉⲧⲃⲉⲡⲉⲛⲟⲩϫⲁⲓ ϩⲓⲟⲩⲥⲟⲡ. ⲁⲡⲉⲧⲉϣϣⲉ ϣⲱⲡⲉ ⲛⲁⲓ ⲉⲧⲣⲁⲥϩⲁⲓ ⲛⲏⲧⲛ̅. ⲉⲓⲡⲁⲣⲁⲕⲁⲗⲉⲓ ⲙ̅ⲙⲱⲧⲛ̅ ⲉⲧⲣⲉⲧⲛ̅ⲙⲓϣⲉ ⲉϫⲛ̅ⲧⲡⲓⲥⲧⲓⲥ ⲉⲛⲧⲁⲩⲧⲁⲁⲥ ⲉⲧⲟⲟⲧⲟⲩ ⲛ̅ⲛⲉⲧⲟⲩⲁⲁⲃ ⲛ̅ⲟⲩⲥⲟⲡ.
4 Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.
ⲇ̅ⲁϩⲉⲛⲣⲱⲙⲉ ⲅⲁⲣ ⲟϣⲟⲩ ⲉϩⲟⲩⲛ. ⲛⲁⲓ ⲛ̅ⲧⲁⲩⲧⲟϭⲟⲩ ⲉⲃⲟⲗ ϫⲓⲛⲛ̅ϣⲟⲣⲡ̅ ⲉⲡⲉⲓⲕⲣⲓⲙⲁ. ⲉϩⲉⲛⲁⲥⲉⲃⲏⲥ ⲛⲉ. ⲉⲩⲡⲱⲱⲛⲉ ⲛ̅ⲧⲉⲭⲁⲣⲓⲥ ⲙ̅ⲡⲛⲟⲩⲧⲉ ⲉⲩϫⲱϩⲙ̅. ⲁⲩⲱ ⲡϫⲟⲉⲓⲥ ⲟⲩⲁⲁϥ ⲙ̅ⲡⲧⲏⲣϥ̅ ⲡⲉⲛϫⲟⲉⲓⲥ ⲓⲥ̅ ⲡⲉⲭⲥ̅ ⲉⲩⲁⲣⲛⲁ ⲙ̅ⲙⲟϥ.
5 Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba.
ⲉ̅ϯⲟⲩⲱϣ ⲇⲉ ⲉⲧⲣⲉⲧⲛ̅ⲣ̅ⲡⲙⲉⲉⲩⲉ ⲉⲧⲉⲧⲛ̅ⲥⲟⲟⲩⲛ̅ⲛ̅ⲕⲁ ⲛⲓⲙ. ϫⲉⲓⲥ̅ ⲁϥⲧⲟⲩϫⲉⲡⲗⲁⲟⲥ ⲉⲃⲟⲗ ϩⲙ̅ⲡⲕⲁϩ ⲛ̅ⲕⲏⲙⲉ ⲛ̅ⲟⲩⲥⲟⲡ. ⲡⲙⲉϩⲥⲡ̅ⲥⲛⲁⲩ ⲛⲉⲧⲉⲙ̅ⲡⲟⲩⲡⲓⲥⲧⲉⲩⲉ ⲉⲣⲟϥ ⲁϥⲧⲁⲕⲟⲟⲩ.
6 Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios g126)
ⲋ̅ⲁⲩⲱ ⲛ̅ⲁⲅⲅⲉⲗⲟⲥ ⲉⲧⲉⲙ̅ⲡⲟⲩϩⲁⲣⲉϩ ⲉⲧⲉⲩⲁⲣⲭⲏ ⲁⲩⲟⲧⲡⲟⲩ ⲉϩⲟⲩⲛ ⲉⲡϩⲁⲡ ⲙ̅ⲡⲛⲟϭ ⲛ̅ϩⲟⲟⲩ ϩⲛ̅ϩⲉⲛⲥⲛⲁⲩϩ ⲛ̅ϣⲁⲉⲛⲉϩ ϩⲛ̅ⲟⲩϩⲧⲟⲙⲧⲙ̅. (aïdios g126)
7 Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios g166)
ⲍ̅ⲛ̅ⲑⲉ ⲛ̅ⲥⲟⲇⲟⲙⲁ ⲙⲛ̅ⲅⲟⲙⲟⲣⲣⲁ ⲙⲛ̅ⲛ̅ⲕⲉⲡⲟⲗⲓⲥ ⲉⲧⲕⲱⲧⲉ ⲉⲣⲟⲟⲩ ⲉⲁⲩⲡⲟⲣⲛⲉⲩⲉ ϩⲱⲟⲩ ϩⲙ̅ⲡⲉⲓⲥⲙⲟⲧ ⲛ̅ⲟⲩⲱⲧ ⲛ̅ⲧⲉⲧⲙⲛ̅ⲧⲁⲧⲛⲁϩⲧⲉ ⲉⲁⲩⲟⲩⲁϩⲟⲩ ⲛ̅ⲥⲁⲕⲉⲥⲁⲣⲝ̅. ⲥⲉⲕⲏ ⲉϩⲣⲁⲓ ϫⲓⲛⲛ̅ϣⲟⲣⲡ̅ ⲛ̅ⲥⲙⲟⲧ. ⲉⲁⲩϯϩⲁⲡ ⲉⲣⲟⲟⲩ ϩⲛ̅ⲟⲩⲕⲱϩⲧ̅ ⲛ̅ϣⲁⲉⲛⲉϩ. (aiōnios g166)
8 Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama.
ⲏ̅ϩⲟⲙⲟⲓⲱⲥ ⲛⲉⲓⲕⲟⲟⲩⲉ ⲉⲩⲡⲉⲣⲉⲣⲁⲥⲟⲩ. ⲛ̅ⲥⲁⲣⲝ̅ ⲙⲉⲛ ⲥⲉϫⲱϩⲙ̅ ⲙ̅ⲙⲟⲟⲩ ⲙ̅ⲙⲛ̅ⲧϫⲟⲉⲓⲥ ⲥⲉⲁⲑⲉⲧⲉⲓ ⲙ̅ⲙⲟⲟⲩ. ⲛⲉⲟⲟⲩ ⲥⲉϫⲓⲟⲩⲁ ⲉⲣⲟⲟⲩ.
9 Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!”
ⲑ̅ⲙⲓⲭⲁⲏⲗ ⲇⲉ ⲡⲁⲣⲭⲁⲅⲅⲉⲗⲟⲥ ⲉϥϣⲁϫⲉ ⲙⲛ̅ⲡⲇⲓⲁⲃⲟⲗⲟⲥ. ⲛ̅ⲧⲉⲣⲉϥϫⲓϩⲁⲡ ⲛⲙ̅ⲙⲁϥ ⲉⲧⲃⲉⲡⲥⲱⲙⲁ ⲙ̅ⲙⲱⲩⲥⲏⲥ ⲙ̅ⲡϥ̅ⲧⲟⲗⲙⲁ ⲉⲧⲣⲉϥⲉⲓⲛⲉ ⲛ̅ⲟⲩϩⲁⲡ ⲛ̅ⲟⲩⲁ ⲉϩⲣⲁⲓ ⲉϫⲱϥ. ⲁⲗⲗⲁ ⲛ̅ⲧⲁϥϫⲟⲟⲥ. ϫⲉⲉⲣⲉⲡϫⲟⲉⲓⲥ ⲉⲡⲓⲧⲓⲙⲁ ⲛⲁⲕ.
10 Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.
ⲓ̅ⲛⲁⲓ ⲇⲉ ⲛⲉⲧⲉⲛ̅ⲥⲉⲥⲟⲟⲩⲛ̅ ⲙ̅ⲙⲟⲟⲩ ⲁⲛ ⲥⲉϫⲓⲟⲩⲁ ⲉⲣⲟⲟⲩ. ⲛⲉⲧⲟⲩⲥⲟⲟⲩⲛ̅ ⲇⲉ ⲙ̅ⲙⲟⲟⲩ ⲛ̅ⲑⲉ ⲙ̅ⲡⲉⲥⲙⲟⲧ ⲛ̅ⲛ̅ⲧⲃ̅ⲛⲟⲟⲩⲉ ⲥⲉⲧⲁⲕⲟ ϩⲣⲁⲓ ⲛ̅ϩⲏⲧⲟⲩ.
11 Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.
ⲓ̅ⲁ̅ⲟⲩⲟⲓ ⲛⲁⲩ. ϫⲉⲁⲩⲙⲟⲟϣⲉ ϩⲛ̅ⲧⲉϩⲓⲏ ⲛ̅ⲕⲁⲓⲛ. ⲁⲩϫⲱⲱⲣⲉ ⲉⲃⲟⲗ ϩⲛ̅ⲧⲉⲡⲗⲁⲛⲏ ⲙ̅ⲡⲃⲉⲕⲉ ⲛ̅ⲃⲁⲗⲁϩⲁⲙ. ⲁⲩⲱ ⲁⲩⲧⲁⲕⲟ ϩⲛ̅ⲧⲁⲛⲧⲓⲗⲟⲅⲓⲁ ⲛ̅ⲕⲟⲣⲉ. ϩⲉⲛⲣⲉϥⲕⲣⲙ̅ⲣⲙ̅ ⲛ̅ⲣⲉϥϭⲛ̅ⲁⲣⲓⲕⲉ. ⲉⲩⲙⲟⲟϣⲉ ⲕⲁⲧⲁⲛⲉⲩⲉⲡⲓⲑⲩⲙⲓⲁ.
12 Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus.
ⲓ̅ⲃ̅ⲛⲁⲓ ⲛⲉⲧϫⲁϩⲙ̅ ϩⲛ̅ⲛⲉⲧⲛ̅ⲁⲅⲁⲡⲏ ⲉⲩⲟⲩⲛⲟϥ ⲛⲙ̅ⲙⲏⲧⲛ̅ ⲁϫⲛ̅ϩⲟⲧⲉ ⲉⲩϫⲱϩⲙ̅ ⲙ̅ⲙⲟⲟⲩ. ⲉϩⲉⲛⲕⲗⲟⲟⲗⲉ ⲉⲩϣⲟⲩⲉⲓⲧ ⲛⲉ. ⲉⲣⲉϩⲉⲛⲧⲏⲩ ϩⲓⲟⲩⲉ ⲛ̅ⲥⲱⲟⲩ. ⲁⲩⲱ ϩⲉⲛϣⲏⲛ ⲉⲩϣⲟⲩⲱⲟⲩ ⲛⲉ ⲛ̅ⲁⲧⲕⲁⲣⲡⲟⲥ. ⲉⲁⲩⲙⲟⲩ ⲛ̅ⲕⲉⲥⲟⲡ ϩⲛ̅ⲛⲉⲩⲛⲟⲩⲛⲉ.
13 Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn g165)
ⲓ̅ⲅ̅ⲛ̅ϩⲟⲉⲓⲙ ⲉⲧⲛⲁϣⲧ̅ ⲛ̅ⲧⲉⲑⲁⲗⲁⲥⲥⲁ ⲉⲩⲧⲁⲩⲟ ⲉⲃⲟⲗ ⲙ̅ⲡⲉⲩϣⲓⲡⲉ. ⲛ̅ⲥⲓⲟⲩ ⲉⲛⲧⲁⲩⲥⲱⲣⲙ̅. ⲛⲁⲓ ⲉⲛⲧⲁⲩⲥⲟⲃⲧⲉ ⲛⲁⲩ ⲛ̅ϣⲁⲉⲛⲉϩ ⲙ̅ⲡⲕⲁⲕⲉ ⲉⲧϩⲧⲙ̅ⲧⲱⲙ. (aiōn g165)
14 Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa
ⲓ̅ⲇ̅ⲉⲛⲱⲭ ⲇⲉ ⲁϥⲡⲣⲟⲫⲏⲧⲉⲩⲉ ⲛ̅ⲛⲉⲓⲕⲟⲟⲩⲉ ⲉⲡⲙⲉϩⲥⲁϣϥ̅ ⲡⲉ ϫⲓⲛⲁⲇⲁⲙ ⲉϥϫⲱ ⲙ̅ⲙⲟⲥ. ϫⲉⲉⲓⲥⲡϫⲟⲉⲓⲥ ⲁϥⲉⲓ ϩⲛ̅ⲛⲉϥⲧⲃⲁ ⲛ̅ⲁⲅⲅⲉⲗⲟⲥ ⲉⲧⲟⲩⲁⲁⲃ.
15 don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.”
ⲓ̅ⲉ̅ⲉⲧⲣⲉϥⲉⲓⲣⲉ ⲛ̅ⲟⲩⲕⲣⲓⲥⲓⲥ ⲉϫⲛ̅ⲟⲩⲟⲛ ⲛⲓⲙ. ⲁⲩⲱ ⲛϥ̅ϫⲡⲓⲉⲯⲩⲭⲏ ⲛⲓⲙ ⲉⲧⲃⲉϩⲱⲃ ⲛⲓⲙ ⲛ̅ⲧⲁⲩⲣ̅ϣⲁϥⲧⲉ ⲛ̅ϩⲏⲧⲟⲩ. ⲁⲩⲱ ⲉⲧⲃⲉⲛ̅ϣⲁϫⲉ ⲧⲏⲣⲟⲩ ⲉⲧⲛⲁϣⲧ̅ ⲛ̅ⲧⲁⲩϫⲟⲟⲩ ⲉⲣⲟϥ ⲛ̅ϭⲓⲛ̅ⲛ̅ⲣⲉϥⲣ̅ⲛⲟⲃⲉ ⲛ̅ⲁⲥⲉⲃⲏⲥ.
16 Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.
ⲓ̅ⲋ̅ⲛⲁⲓ ⲛⲉ ⲛ̅ⲣⲉϥⲕⲣⲙ̅ⲣⲙ̅ ⲛ̅ⲣⲉϥϭⲛ̅ⲁⲣⲓⲕⲉ ⲉⲩⲙⲟⲟϣⲉ ⲕⲁⲧⲁⲛⲉⲩⲉⲡⲓⲑⲩⲙⲓⲁ. ⲁⲩⲱ ⲧⲉⲩⲧⲁⲡⲣⲟ ⲉⲥϫⲓⲙⲛ̅ⲧϩⲣⲟⲩⲱ. ⲉⲩⲣ̅ϣⲡⲏⲣⲉ ⲛ̅ⲥⲁϩⲉⲛϩⲟ ⲉⲧⲃⲉⲟⲩϩⲏⲩ.
17 Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā.
ⲓ̅ⲍ̅ⲛ̅ⲧⲱⲧⲛ̅ ⲇⲉ. ⲛⲁⲙⲉⲣⲁⲧⲉ. ⲁⲣⲓⲡⲙⲉⲉⲩⲉ ⲛ̅ⲛ̅ϣⲁϫⲉ ⲙ̅ⲡⲉⲛϫⲟⲉⲓⲥ ⲓⲥ̅ ⲡⲉⲭⲥ̅. ⲛⲁⲓ ⲛ̅ⲧⲁⲛⲉϥⲁⲡⲟⲥⲧⲟⲗⲟⲥ ϫⲟⲟⲩ ϫⲓⲛⲛ̅ϣⲟⲣⲡ̅.
18 Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.”
ⲓ̅ⲏ̅ⲉⲃⲟⲗ ϫⲉⲁⲩϫⲟⲟⲥ. ϫⲉϩⲛ̅ⲑⲁⲏ ⲛ̅ⲛⲉⲟⲩⲟⲉⲓϣ ⲟⲩⲛ̅ϩⲉⲛⲣⲉϥϫⲏⲣ ⲛⲏⲩ. ⲉⲩⲙⲟⲟϣⲉ ⲕⲁⲧⲁⲛⲉⲡⲓⲑⲩⲙⲓⲁ ⲛ̅ⲛⲉⲩⲙⲛ̅ⲧϣⲁϥⲧⲉ.
19 Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.
ⲓ̅ⲑ̅ⲛⲁⲓ ⲛⲉ ⲛⲉⲧⲡⲱⲣϫ̅ ⲉⲃⲟⲗ. ⲉϩⲉⲛⲯⲩⲭⲓⲕⲟⲥ ⲛⲉ. ⲉⲙⲛ̅ⲧⲟⲩⲡⲛ̅ⲁ ⲙ̅ⲙⲁⲩ.
20 Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki.
ⲕ̅ⲛ̅ⲧⲱⲧⲛ̅ ⲇⲉ. ⲛⲁⲙⲉⲣⲁⲧⲉ. ⲉⲧⲉⲧⲛ̅ⲕⲱⲧ ⲙ̅ⲙⲱⲧⲛ̅ ϩⲛ̅ⲧⲉⲧⲛ̅ⲡⲓⲥⲧⲓⲥ ⲉⲧⲟⲩⲁⲁⲃ ⲉⲙⲁⲧⲉ. ⲉⲧⲉⲧⲛ̅ϣⲗⲏⲗ ϩⲙ̅ⲡⲉⲡⲛ̅ⲁ ⲉⲧⲟⲩⲁⲁⲃ.
21 Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios g166)
ⲕ̅ⲁ̅ϩⲁⲣⲉϩ ⲉⲣⲱⲧⲛ̅ ϩⲛ̅ⲧⲁⲅⲁⲡⲏ ⲙ̅ⲡⲛⲟⲩⲧⲉ. ⲉⲧⲉⲧⲛ̅ϭⲱϣⲧ̅ ⲉⲃⲟⲗ ϩⲏⲧϥ̅ ⲙ̅ⲡⲛⲁ ⲙ̅ⲡⲉⲛϫⲟⲉⲓⲥ ⲓⲥ̅ ⲡⲉⲭⲥ̅ ⲉⲩⲱⲛϩ̅ ⲛ̅ϣⲁⲉⲛⲉϩ. (aiōnios g166)
22 Ku ji tausayin waɗanda suke shakka;
ⲕ̅ⲃ̅ⲁⲩⲱ ϩⲟⲓⲛⲉ ⲉⲧⲉⲧⲛ̅ⲧⲱⲕⲙ̅ ⲙ̅ⲙⲟⲟⲩ ⲉⲃⲟⲗ ϩⲛ̅ⲧⲥⲁⲧⲉ
23 ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.
ⲕ̅ⲅ̅ⲉⲧⲉⲧⲛ̅ⲛⲁ ⲛ̅ⲛⲉⲧϫⲓϩⲁⲡ ϩⲛ̅ⲟⲩϩⲟⲧⲉ. ⲉⲧⲉⲧⲛ̅ⲙⲟⲥⲧⲉ ⲛ̅ⲧⲉϣⲧⲏⲛ ⲉⲧϫⲁϩⲙ̅ ⲉⲃⲟⲗ ϩⲛ̅ⲧⲥⲁⲣⲝ̅.
24 To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki.
ⲕ̅ⲇ̅ⲡⲉⲧⲉⲩⲛ̅ϭⲟⲙ ⲙ̅ⲙⲟϥ ⲉⲧⲣⲉϥϩⲁⲣⲉϩ ⲉⲣⲱⲧⲛ̅ ⲉⲧⲉⲧⲛ̅ⲧⲁϫⲣⲏⲩ ⲛϥ̅ⲧⲁϩⲱⲧⲛ̅ ⲉⲣⲁⲧⲧⲏⲩⲧⲛ̅ ⲙ̅ⲡⲉⲙⲧⲟ ⲉⲃⲟⲗ ⲙ̅ⲡⲉϥⲉⲟⲟⲩ. ⲉⲧⲉⲧⲛ̅ⲟⲩⲁⲁⲃ ϩⲛ̅ⲟⲩⲧⲉⲗⲏⲗ.
25 Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn g165)
ⲕ̅ⲉ̅ⲡⲛⲟⲩⲧⲉ ⲡⲉⲛⲥⲱⲧⲏⲣ ⲟⲩⲁⲁϥ. ⲡⲉⲟⲟⲩ ⲛⲁϥ ⲉⲃⲟⲗ ϩⲓⲧⲛ̅ⲓⲥ̅ ⲡⲉⲭⲥ̅ ⲡⲉⲛϫⲟⲉⲓⲥ. ⲙⲛ̅ⲧϭⲟⲙ ⲁⲩⲱ ⲡⲁⲙⲁϩⲧⲉ ⲙⲛ̅ⲧⲉⲝⲟⲩⲥⲓⲁ ϩⲁⲑⲏ ⲛ̅ⲛ̅ⲁⲓⲱⲛ ⲧⲏⲣⲟⲩ. ⲁⲩⲱ ϫⲓⲛⲧⲉⲛⲟⲩ ⲉⲛⲁⲓⲱⲛ ⲧⲏⲣⲟⲩ ϩⲁⲙⲏⲛ. (aiōn g165)

< Yahuda 1 >