< Yahuda 1 >

1 Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub, Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.
Jesuh Khritawa mpya, Jakuka na kei Judah naw, Pamhnam naw a jah khü päng khyange, Pa Pamhnama mhläkphyanak ja Jesuh Khritawa kcungvawngnak am xüngseikie veia ka yuk ni.
2 Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.
Mpyenmseinak, dimdeihnak ja mhläkphyanak nami khana be se.
3 Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak.
Ka püi he aw, mi yah khyakhya küikyannaka mawng ning jah yuk law vaia ka ngaih kyaw. Cunüngpi, Pamhnam naw a khyangea üng ahun jumeinak cun angläta phäh a jah peta phäh ngtäknak nami pawh vaia, mcuhmcäinak kca angsüha ka ning jah yuk law vaia ka ktha naki.
4 Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.
Khyümhnam am ksingki cun am mi jah ksinga mi ksunga ngpüi law ve u. Ami ngneisak kse cun ami khümphanaka vaia mi Pamhnama bäkhäknaka mawng cun akhyea jah mtheikie ni. Acun he naw mi Mahpa ja Bawipa, Jesuh Khritaw cun makie. Ami yahei vaia mkatnak ta, ahlana khyüh Cangcim naw a na pyen päng ni.
5 Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba.
Acunakyase, nami ksing pänga kya kyaw lü pi, ning jah mcuhmcäinaka ka pyen hlü ta, Isarel khyang mjüe cen Egypt pe üngkhyüh Bawipa naw a jah küikyan ni. Acunüngpi, ani am jumeiki cun a jah mcimkpyeh be ni.
6 Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. (aïdios g126)
Pamhnam naw a jah peta anaa k’uma am ve hlü lü ami hnün hawihkia khankhawngsä avange pi ngthumkhyah lawa Mhnüp üng a jah mkhuimkha vaia, angsäia mthiyüi am jah khit lü anghmüpnaka ke säiha a jah tak cen jah süm ua. (aïdios g126)
7 Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta. (aiōnios g166)
Sodom ja Komorah, ja a pipeia mlüh üngka khyange pi acuna khankhawngsäe akba awmih u lü hnunglanak, khyanga khyucei ihawmpüi lü mkhyekat u se angsäia mei üng mkhihnak ami khamei cen mi vana phäh mcäinak ni ti cen süm ua. (aiōnios g166)
8 Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama.
Acukba ni, ahina khyange naw amimäta pumsa jah mkhyekatsakia hmuhmdannak ta ve u. Pamhnama johit pi am hnaläü u, khana veki khankhawngsä jomahe pi jah mdihmsuikie.
9 Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!”
Khankhawngsäea mkhawng Mihkhelah hngawh pi acukba am ve. Khawyama dä Mosia yawk u naw bi khai ti lü ani ngcuh üng mkateinaka ngthu am pyen. “Bawipa naw ning kse na se” ti lü ni a pyen.
10 Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.
Acunüngpi, ahina khyange naw ta am ami ksing ngkhai cun mdihmsuinak am ngtäkpüikie. Sakyungea mäiha ami ngtüiei lawpüi am ksing u lü, acuna ksingnak naw jah kpyüpye khai.
11 Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.
Ihlawka kyühei phyaki ni. Kaihnaha hnu läki he ni. Ngui yah vaia phäh biloki Balaama kba mkhyenak pawh ve u. Korah naw pyen a kpetmjaka kba, pyen kpetmjakie. Koraha cimpyak kba cimpyak acun he.
12 Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus.
Nglawinak buh pawi nami pawh üng nami ksunga ngkeei vai am ksing u lü mtuihmlehsakie ni. Amimäta phü vai däk ksingki he. Acun he cun khawkhi naw a jawn hü yawhtui ka khawngmei am tängkie ni. A ngthei kcün pha lü am ngtheipaiki thingdung am tängkie ni. Ami ngthei vaia kcün khawksik khye hngawh üngpi am ngtheikia thingdungea kba, a pya mahmaha phukin lü avana thikia thingdung üng tängkie ni.
13 Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada. (aiōn g165)
Ngkeeikse aksekhyu ami bi lawh cun, mtüihkhehki tuimpawn nawt lawki mpanglai tui ngnawk üng tängkie ni. A phanak vai hnün am ngtekia aisie am tängkie ni. Amimi phäh Pamhnam naw anghmüpnak säih hnün cun angsäia jah tak petki. (aiōn g165)
14 Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa
Adam üngkhyüh ngsawn khyühnak Enawk naw sahma lü a na pyen ta, “Bawipa cun a khankhawngsä ngcim thawng khawkän am kyum law lü avana khana ngthumkhyah law khai. Mhnam kaa mäiha am dawki ami pawhnak naküt ja mhnam kaa mäiha khyangka he naw ani kpetnaka ngthu kyühei phyaki ami pyen naküta phäh acune jah mkhuimkha law khai” a ti.
15 don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.”
16 Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.
Acuna khyange cun aläa ngikcak u lü khyang jah mkateikie. Ami mlungkaw ngnei ksea hnu läki he. Amimät mhlünmtaiei u lü, amimäta dawnak vaia khyang jah mhläki he.
17 Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā.
Ka püi he aw, mi Bawipa Jesuh Khritawa ngsäe naw ami pyen khawi, “Akpäihnaka kcün üng, ning yaihyünei acun he po law acun he. Khyang he naw mhnam am ksinga mtisa hlü läklam law acun he” ti cen süm ua.
18 Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.”
19 Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.
Ahin he cun ngphüingkyanak pawhkie ni, Ngmüimkhya am takia khyange, ami mlung hlü naw a jah nängeia khyange ni.
20 Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki.
Acunüngpi, ka püi he aw, nami jumeinak ngcingcaih säih am namimät ngsawngsaei ua. Ngmüimkhya Ngcima johit am ktaiyü ua.
21 Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami. (aiōnios g166)
Pamhnama mhläkphyanak am namimät ve nglät ua. Angsäia xünnak a ning jah pet vaia phäh mi Bawipa Jesuh Khritawa mpyenmseinak äpei lü ve ua. (aiōnios g166)
22 Ku ji tausayin waɗanda suke shakka;
Ami mlung uplatkie khana mpyeneinak ta ua.
23 ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.
Khyang kce he xünnak ami yah vai mei kdäi üngkhyüh jah kset be lü jah kumei ua. Mceieinak am jah mpyenei ua. Cunüngpi, ami mkhyenak mtisa hlükaw am beki ami suisak ta nami mtuihei vai.
24 To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki.
Jumeinak üng kyukngpänak üngkhyüh, mkhyenak am vekia jekyainak üng a hlüngtainaka maa ning jah cehpüi khawhki,
25 Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin. (aiōn g165)
Jah Küikyanki Pamhnam mat däka jotai, dämduh hlüngtainak ja ana cun, Mi Bawipa Jesuh Khritaw üngkhyüh, päih pängki kcüne ja atuh üngkhyüh, angsäia hlüngtai se. Amen. (aiōn g165)

< Yahuda 1 >