< Yoshuwa 1 >
1 Bayan mutuwar Musa bawan Ubangiji, sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa ɗan Nun, mataimakin Musa,
Efter Mose, Herrans tjenares död, sade Herren till Josua, Nuns son, Mose tjenare:
2 “Bawana Musa ya mutu. Yanzu sai ka tashi tare da mutanen nan duka, ku yi shirin ƙetare kogin Urdun zuwa cikin ƙasar da zan ba su Isra’ilawa.
Min tjenare Mose är död; så gör dig nu redo och drag öfver denna Jordan, du och allt detta folket, in uti det land, som jag dem, nämliga Israels barnom, gifvit hafver.
3 Zan ba ku duk ƙasar da za ku taka, kamar yadda na yi wa Musa alkawari.
Allt rum, der edart fotbjelle på trädandes varder, hafver jag gifvit eder, såsom jag Mose sagt hafver;
4 Ƙasar da ta kama daga hamada zuwa Lebanon, zuwa babban Kogin, wato, Kogin Yuferites, da dukan ƙasar Hittiyawa zuwa Bahar Rum, wajen yamma.
Ifrån öknene och denna Libanon, intill den stora älfvena Phrath, hela Hetheers land, intill det stora hafvet vesterut, skola edor landamäre vara.
5 Ba wanda zai yi tsayayya da kai dukan kwanakin ranka. Yadda na kasance tare da Musa, haka zan kasance tare da kai; ba zan taɓa rabuwa da kai ba; ba zan yashe ka ba.
Ingen skall stå emot dig i dina lifsdagar; såsom jag hafver varit med Mose, så skall jag ock vara med dig; jag skall icke öfvergifva eller förgäta dig.
6 “Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, gama kai za ka bi da mutanen nan har su karɓi ƙasar da na yi wa kakanninsu alkawari zan ba su.
Var tröst och frimodig; ty du skall utskifta desso folkena landet, som jag deras fäder svorit hafver, att jag dem det gifva skulle.
7 Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, ka yi lura fa, ka yi biyayya da dokokin da bawana Musa ya ba ka; kada ka kauce ga bin dokokin ko hagu ko dama, domin ka yi nasara a duk, inda za ka je.
Var nu tröst och ganska frimodig, att du håller och gör all ting efter lagen, som Mose min tjenare dig budit hafver; vik icke derifrån, antingen på högra sidon eller den venstra, på det att du må handla visliga i allt det du göra skall.
8 Kada ka bar Littafin Dokokin nan yă rabu da bakinka, sai dai ka yi ta tunani game da shi dare da rana, don ka lura, ka yi duk abin da aka rubuta a ciki, ta haka ne za ka yi nasara cikin duk abin da za ka yi.
Och låt denna lagbokena icke komma utu dinom mun; utan haf dina tankar deruti dag och natt, på det att du skall hålla och göra all ting derefter, som deruti skrifvet står; så skall dig lyckas i allt det du gör, och du skall kunna handla visliga.
9 Ba ni na umarce ka ba? Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro. Kada ka ji tsoro; kada ka karaya, gama Ubangiji Allahnka zai kasance tare da kai duk inda za ka je.”
Si, jag hafver budit dig, att du skall vara tröst, och vid godt mod; grufva dig för ingen ting, och frukta intet; ty Herren din Gud är med dig i allt det du företager.
10 Saboda haka sai Yoshuwa ya umarci shugabannin mutane,
Då böd Josua höfvitsmännerna öfver folket, och sade:
11 “Ku ratsa cikin sansani, ku gaya wa mutane, ‘Ku shirya guzurinku. Nan da kwana uku za ku ƙetare Urdun a nan, don ku je ka mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ta zama taku.’”
Går igenom lägret, och bjuder folkena, och säger: Bereder eder spisning; ty efter tre dagar skolen I gå öfver denna Jordanen, att I mågen inkomma till att intaga landet, som Herren edar Gud eder gifva skall.
12 Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Ruben, mutanen Gad da kuma rabin mutanen kabilar Manasse,
Och sade Josua till de Rubeniter, Gaditer, och till de halfva slägtena Manasse:
13 “Ku tuna da umarnin da Musa bawan Ubangiji ya yi muku. ‘Ubangiji Allahnku ya ba ku hutawa, ya kuma ba ku wannan ƙasa.’
Tänker uppå det ord, som Mose Herrans tjenare eder böd, och sade: Herren edar Gud hafver låtit eder komma till ro, och gifvit eder detta landet.
14 Matanku, da yaranku, da kuma dabbobinku za su kasance a ƙasar da Musa ya ba ku a gabashin Urdun, amma dole mayaƙanku, su yi shirin yaƙi su haye, su yi gaba tare da’yan’uwanku, za ku taimaki’yan’uwanku
Edra hustrur, barn och boskap låter blifva i landena, som Mose eder gifvit hafver, på denna sidone Jordan; men I skolen gå för edra bröder väpnade, alle de som väraktige män äro, och hjelpa dem;
15 har sai lokacin da Ubangiji ya ba su hutawa, kamar yadda ya yi muku, kuma har sai su ma sun ƙwace ƙasar da Ubangiji Allahnku ya yi alkawari zai ba su. Bayan haka ne za ku koma ku mallaki ƙasarku, wadda Musa bawan Ubangiji ya ba ku a gabashin Urdun.”
Intilldess Herren låter ock edra bröder komma till ro, så väl som eder, att de ock måga intaga det land, som Herren edar Gud dem gifva skall. Sedan skolen I vända om igen till edart land, att I det besitten, som Mose Herrans tjenare eder gifvit hafver, på denna sidone Jordan österut.
16 Sai suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “Duk abin da ka ce mu yi, za mu yi. Duk inda kuma ka aike mu, za mu je.
Och de svarade Josua, och sade: Allt det du oss budit hafver, det vilje vi göra, och hvart du sänder oss, dit vilje vi gå.
17 Kamar yadda muka yi wa Musa biyayya, haka za mu yi maka biyayya. Ubangiji Allahnka ya kasance tare da Musa.
Såsom vi hafve varit Mose lydige, så vilje vi ock vara dig lydige; allenast vare Herren din Gud med dig, såsom han var med Mose.
18 Duk wanda ya yi wa maganarka tawaye, ya ƙi yă yi biyayya da maganarka, ko da umarnin da ka ba shi, za a kashe shi. Ka dai ƙarfafa ka kuma yi ƙarfi hali!”
Hvilken som din mun emotstår, och icke lyder din ord i allt det du bjuder oss, han skall dö; allenast var du tröst, och vid godt mod.