< Yoshuwa 1 >
1 Bayan mutuwar Musa bawan Ubangiji, sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa ɗan Nun, mataimakin Musa,
Now it came to pass after the death of Moses the servant of the Lord, that the Lord spoke to Josue the son of Nun, the minister of Moses, and said to him:
2 “Bawana Musa ya mutu. Yanzu sai ka tashi tare da mutanen nan duka, ku yi shirin ƙetare kogin Urdun zuwa cikin ƙasar da zan ba su Isra’ilawa.
Moses my servant is dead: arise, and pass over this Jordan, thou and thy people with thee, into the land which I will give to the children of Israel.
3 Zan ba ku duk ƙasar da za ku taka, kamar yadda na yi wa Musa alkawari.
I will deliver to you every place that the sole of your foot shall tread upon, as I have said to Moses.
4 Ƙasar da ta kama daga hamada zuwa Lebanon, zuwa babban Kogin, wato, Kogin Yuferites, da dukan ƙasar Hittiyawa zuwa Bahar Rum, wajen yamma.
From the desert and from Libanus unto the great river Euphrates, all the land of the Hethites unto the great sea toward the going; down of the sun, shall be your border.
5 Ba wanda zai yi tsayayya da kai dukan kwanakin ranka. Yadda na kasance tare da Musa, haka zan kasance tare da kai; ba zan taɓa rabuwa da kai ba; ba zan yashe ka ba.
No man shall be able to resist you all the days of thy life: as I have been with Moses, so will I be with thee: I will not leave thee, nor forsake thee.
6 “Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, gama kai za ka bi da mutanen nan har su karɓi ƙasar da na yi wa kakanninsu alkawari zan ba su.
Take courage, and be strong: for thou shalt divide by lot to this people the land, for which I swore to their fathers, that I would deliver it to them.
7 Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, ka yi lura fa, ka yi biyayya da dokokin da bawana Musa ya ba ka; kada ka kauce ga bin dokokin ko hagu ko dama, domin ka yi nasara a duk, inda za ka je.
Take courage therefore, and be very valiant: that thou mayst observe and do all the law, which Moses my servant hath commanded thee: turn not from it to the right hand or to the left, that thou mayst understand all things which thou dost.
8 Kada ka bar Littafin Dokokin nan yă rabu da bakinka, sai dai ka yi ta tunani game da shi dare da rana, don ka lura, ka yi duk abin da aka rubuta a ciki, ta haka ne za ka yi nasara cikin duk abin da za ka yi.
Let not the book of this law depart from thy mouth: but thou shalt meditate on it day and night, that thou mayst observe and do all things that are written in it: then shalt thou direct thy way, and understand it.
9 Ba ni na umarce ka ba? Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro. Kada ka ji tsoro; kada ka karaya, gama Ubangiji Allahnka zai kasance tare da kai duk inda za ka je.”
Behold I command thee, take courage, and be strong. Fear not and be not dismayed: because the Lord thy God is with thee in all things whatsoever thou shalt go to.
10 Saboda haka sai Yoshuwa ya umarci shugabannin mutane,
And Josue commanded the princes of the people, saying: Pass through the midst of the camp, and command the people, and say:
11 “Ku ratsa cikin sansani, ku gaya wa mutane, ‘Ku shirya guzurinku. Nan da kwana uku za ku ƙetare Urdun a nan, don ku je ka mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ta zama taku.’”
Prepare you victuals: for after the third day you shall pass over the Jordan and shall go in to possess the land, which the Lord your God will give you.
12 Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Ruben, mutanen Gad da kuma rabin mutanen kabilar Manasse,
And he said to the Rubenites, and the Gadites, and the half tribe of Manasses:
13 “Ku tuna da umarnin da Musa bawan Ubangiji ya yi muku. ‘Ubangiji Allahnku ya ba ku hutawa, ya kuma ba ku wannan ƙasa.’
Remember the word, which Moses the servant of the Lord commanded you, saying: The Lord your God hath given you rest, and all this land.
14 Matanku, da yaranku, da kuma dabbobinku za su kasance a ƙasar da Musa ya ba ku a gabashin Urdun, amma dole mayaƙanku, su yi shirin yaƙi su haye, su yi gaba tare da’yan’uwanku, za ku taimaki’yan’uwanku
Your wives, and children, and cattle shall remain in the land which Moses gave you on this side of the Jordan: but pass you over armed before your brethren, all of you that are strong of hand, and fight for them,
15 har sai lokacin da Ubangiji ya ba su hutawa, kamar yadda ya yi muku, kuma har sai su ma sun ƙwace ƙasar da Ubangiji Allahnku ya yi alkawari zai ba su. Bayan haka ne za ku koma ku mallaki ƙasarku, wadda Musa bawan Ubangiji ya ba ku a gabashin Urdun.”
Until the Lord give rest to your brethren as he hath given you, and they also possess the land which the Lord your God will give them: and so you shall return into the land of your possession, and you shall dwell in it, which Moses the servant of the Lord gave you beyond the Jordan, toward the rising of the sun.
16 Sai suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “Duk abin da ka ce mu yi, za mu yi. Duk inda kuma ka aike mu, za mu je.
And they made answer to Josue, and said: All that thou hast commanded us we will do; and whithersoever thou shalt send us, we will go.
17 Kamar yadda muka yi wa Musa biyayya, haka za mu yi maka biyayya. Ubangiji Allahnka ya kasance tare da Musa.
As we obeyed Moses in all things, so will we obey thee also: only be the Lord thy God with thee, as he was with Moses.
18 Duk wanda ya yi wa maganarka tawaye, ya ƙi yă yi biyayya da maganarka, ko da umarnin da ka ba shi, za a kashe shi. Ka dai ƙarfafa ka kuma yi ƙarfi hali!”
He that shall gainsay thy mouth, and not obey all thy words, that thou shalt command him, let him die: only take thou courage, and do manfully.