< Yoshuwa 9 >

1 To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
Då nu detta hördes intill alla de Konungar, som voro på den sidon Jordan, på bergom och i dalom, och i alla stora hafsens hamner, och när dem som voro invid Libanons berg, nämliga de Hetheer, Amoreer, Cananeer, Phereseer, Heveer och Jebuseer;
2 suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
Samkade de sig tillhopa endrägteliga, att de skulle strida emot Josua, och emot Israel.
3 Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
Men Gibeons inbyggare, då de hörde hvad Josua gjort hade med Jericho och Aj,
4 sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
Upptänkte de en list, gingo till och sände bådskap åstad, och togo gamla säcker på sina åsnar, och gamla slitna vinläglar,
5 Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
Och gamla lappade skor på sina fötter, och drogo gamla och rifna kläder uppå; och allt det bröd, som de togo med sig, var hårdt och mögladt;
6 Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
Och gingo till Josua i lägret vid Gilgal, och sade till honom, och till hela Israel: Vi äre komne fjerran af annor land; så görer nu ett förbund med oss.
7 Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
Då sade hela Israel till de Heveer: Kan hända, att du bor här ibland oss, huru kunne vi då göra förbund med dig?
8 Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
De sade till Josua: Vi äre dine tjenare. Josua sade till dem: Ho ären I; eller hvadan kommen I?
9 Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
De sade: Dine tjenare äro ganska fjerran komne af annor land, för Herrans dins Guds Namns skull; ty vi hafve hört hans rykte, och allt det han i Egypten gjort hafver;
10 da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
Och allt det han de två Amoreers Konungar på hinsidon Jordan gjort hafver, Sihon, Konungenom i Hesbon, och Og, Konungenom i Basan, som bodde i Astaroth.
11 Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
Derföre sade våre äldste; och alle vårt lands inbyggare: Tager spisning med eder på resona, och går åstad emot dem, och säger till dem: Vi äre edre tjenare; så görer nu ett förbund med oss.
12 Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
Detta vårt bröd, som vi togo med oss till spisning utu vår hus, var ännu färskt, då vi åstad forom till eder; men nu, si, det är hårdt och mögladt.
13 Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
Och dessa vinläglarna fyllde vi nya; och si, de äro slitne; och denna vår kläder och skor äro gamla vordna för denna ganska långa resonas skull.
14 Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
Då togo höfvitsmännerna af deras spisning, och frågade intet Herrans mun.
15 Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
Och Josua gjorde frid med dem, och ingick ett förbund med dem, att de skulle blifva lefvande; och de öfverste för menighetene svoro dem.
16 Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
Men efter tre dagar, sedan de hade gjort förbundet med dem, kom för dem, att de voro hardt när dem, och skulle bo ibland dem.
17 Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
Ty då Israels barn drogo framåt, kommo de tredje dagen till deras städer, hvilke så voro nämnde: Gibeon, Cephira, Beeroth och KiriathJearim.
18 Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
Och de slogo dem intet, ty de öfverste för menighetene hade svorit vid Herran Israels Gud; och hela menigheten knorrade emot de öfversta.
19 Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
Då sade alle de öfverste för hela menighetene: Vi hafve svorit dem vid Herran Israels Gud; derföre kunne vi intet komma vid dem.
20 Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
Men det vilje vi göra dem; låtom dem lefva, att en vrede icke kommer öfver oss för edens skull, den vi dem gjort hafvom.
21 Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
Och de öfverste sade till dem: Låtom dem lefva, att de måga vara vedahuggare och vattudragare för hela menighetene, såsom öfverstarna dem sagt hafva.
22 Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
Då kallade dem Josua, och talade med dem, och sade: Hvi hafven I bedragit oss, och sagt: I ären ganska långt ifrån oss; ändock I bon ibland oss?
23 Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
Derföre skolen I vara förbannade, så att af eder icke skall återvända trälar, som ved hugga, och vatten draga, till mins Guds hus.
24 Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
De svarade Josua, och sade: Det hafver varit sagdt dina tjenare, att Herren din Gud hafver budit sinom tjenare Mose, att han skall gifva eder detta hela landet, och förgöra för eder alla landsens inbyggare; då fruktade vi om våra själar för eder storliga, och gjorde detta.
25 Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
Men nu, si, vi äre i dina händer; hvad dig tycker godt och rätt vara att göra med oss, det gör.
26 Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
Och han gjorde dem så, och friade dem ifrån Israels barnas hand, att de icke slogo dem ihjäl.
27 A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.
Så gjorde Josua dem på samma dagen till vedahuggare och vattudragare för menighetene, och till Herrans altare, allt intill denna dag, på det rum som han utväljandes vorde.

< Yoshuwa 9 >