< Yoshuwa 9 >

1 To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
Pripetilo se je, ko so vsi kralji, ki so bili na tej strani Jordana, na hribih, v dolinah in po vseh pokrajinah vélikega morja nasproti Libanonu, Hetejci, Amoréjci, Kánaanci, Perizéjci, Hivéjci in Jebusejci, slišali o tem,
2 suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
da so se zbrali skupaj, da se soglasno bojujejo z Józuetom in z Izraelom.
3 Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
Ko so prebivalci Gibeóna slišali, kaj je Józue storil Jerihi in Aju,
4 sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
so prebrisano storili in odšli ter se naredili kakor, da so bili predstavniki in na svoje osle dali stare vreče in vinske mehove, stare in raztrgane ter jih povezali
5 Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
in stare čevlje, zakrpane na njihovih stopalih in stare obleke na njih in ves kruh njihove popotnice je bil suh in drobljiv.
6 Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
Odšli so k Józuetu v tabor pri Gilgálu, in rekli njemu in Izraelovim možem: »Prišli smo iz daljne dežele, zdaj torej sklenite zavezo z nami.«
7 Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
Možje iz Izraela so rekli Hivéjcem: »Morda prebivate med nami in kako naj sklenemo zavezo z vami?«
8 Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
Ti so Józuetu rekli: »Mi smo tvoji služabniki.« Józue jim je rekel: »Kdo ste? In od kod ste prišli?«
9 Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
Rekli so mu: »Iz zelo oddaljene dežele so prišli tvoji služabniki zaradi imena Gospoda, tvojega Boga, kajti slišali smo sloves o njem in vse, kar je storil v Egiptu
10 da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
in vse, kar je storil dvema kraljema Amoréjcev, ki sta bila onkraj Jordana, hešbónskemu kralju Sihónu in bašánskemu kralju Ogu, ki je bil pri Aštarótu.
11 Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
Zato so nam naši starešine in vsi prebivalci dežele govorili, rekoč: ›S seboj vzemite živež za potovanje in pojdite, da jih srečate in jim recite: ›Mi smo vaši služabniki, zato zdaj sklenite zavezo z nami.‹‹
12 Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
Ta naš kruh smo vzeli še vročega za našo popotnico iz naših hiš na dan, ko smo šli, da gremo k vam, toda sedaj, glejte, je ta suh in drobljiv.
13 Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
Ti vinski mehovi, ki smo jih napolnili, so bili novi, in glejte, raztrgani so. Te naše obleke in naši čevlji so postali stari zaradi razloga zelo dolgega potovanja.«
14 Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
Možje so vzeli od njihovega živeža, niso pa vprašali za nasvet pri Gospodovih ustih.
15 Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
Józue je z njimi sklenil mir in z njimi sklenil zavezo, da jih pusti žive, in princi skupnosti so jim prisegli.
16 Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
Pripetilo pa se je ob koncu treh dni, potem ko so z njimi sklenili zavezo, da so slišali, da so bili njihovi sosedje in da so prebivali med njimi.
17 Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
Izraelovi otroci so odpotovali in na tretji dan prišli v njihova mesta. Torej njihova mesta so bila Gibeón, Kefíra, Beerót in Kirját Jearím.
18 Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
Izraelovi otroci jih niso udarili, ker so jim princi skupnosti prisegli pri Gospodu, Izraelovemu Bogu. In vsa skupnost je godrnjala zoper prince.
19 Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
Toda vsi princi so vsej skupnosti rekli: »Prisegli smo jim pri Gospodu, Izraelovem Bogu. Sedaj se jih torej ne smemo dotakniti.
20 Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
To jim bomo storili. Celo žive jih bomo pustili, da ne bi bil nad nami bes zaradi prisege, ki smo jim jo prisegli.«
21 Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
Princi so jim rekli: »Naj živijo, toda naj bodo drvarji in prinašalci vode vsej skupnosti, « kakor so jim princi obljubili.
22 Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
Józue jih je dal poklicati in jim spregovoril, rekoč: »Zakaj ste nas preslepili, rekoč: ›Mi smo zelo daleč od vas, ‹ ko prebivate med nami?
23 Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
Zdaj ste torej prekleti in nihče izmed vas naj ne bo prost pred tem, da bi bili sužnji, drvarji in prinašalci vode za hišo mojega Boga.«
24 Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
Józuetu so odgovorili in rekli: »Ker je bilo tvojim služabnikom zagotovo povedano to, kako je Gospod, tvoj Bog, zapovedal svojemu služabniku Mojzesu, da vam da vso deželo in da pred seboj uničite vse prebivalce dežele, zato smo bili zaradi vas boleče prestrašeni za svoja življenja in smo storili to stvar.
25 Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
In sedaj glej, mi smo v tvoji roki. Kakor se ti zdi dobro in pravilno, da nam storiš, stôri.«
26 Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
Tako jim je storil in jih osvobodil iz roke Izraelovih otrok, da jih niso pobili.
27 A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.
Józue jih je ta dan naredil za drvarje in prinašalce vode za skupnost in za Gospodov oltar, celo do tega dne, na kraju, ki bi ga izbral.

< Yoshuwa 9 >