< Yoshuwa 9 >
1 To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
Quando todos os reis que estavam além do Jordão, na região montanhosa e na planície, e em toda a costa do grande mar em frente ao Líbano, o hitita, o amorreu, o cananeu, o perizeu, o hivita e o jebuseu, ouviram falar disso
2 suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
eles se reuniram para lutar com Josué e com Israel, com um só acordo.
3 Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
Mas quando os habitantes de Gibeon ouviram o que Josué tinha feito a Jericó e a Ai,
4 sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
eles também recorreram a um ardil, e foram e fizeram como se tivessem sido embaixadores, e levaram sacos velhos em seus burros, e peles de vinho velhas, rasgadas e amarradas,
5 Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
e sandálias velhas e remendadas em seus pés, e usaram roupas velhas. Todo o pão de sua alimentação era seco e mofado.
6 Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
Eles foram até Josué no acampamento em Gilgal, e disseram a ele e aos homens de Israel: “Nós viemos de um país distante. Agora, portanto, façam um pacto conosco”.
7 Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
Os homens de Israel disseram aos Hivitas: “E se você viver entre nós? Como poderíamos fazer um pacto com vocês”?
8 Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
Eles disseram a Joshua: “Nós somos seus servos”. Joshua disse-lhes: “Quem é você? De onde você vem?”
9 Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
Eles lhe disseram: “Seus servos vieram de um país muito distante por causa do nome de Yahweh seu Deus; pois ouvimos falar de sua fama, tudo o que ele fez no Egito,
10 da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
e tudo o que ele fez aos dois reis dos amorreus que estavam além do Jordão, a Sihon rei de Hesbon e a Og rei de Basã, que estava em Ashtaroth.
11 Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
Nossos anciãos e todos os habitantes de nosso país falaram conosco, dizendo: 'Pegue mantimentos em sua mão para a viagem e vá ao seu encontro'. Diga-lhes: “Nós somos seus servos”. Agora façam um pacto conosco”.
12 Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
Este nosso pão que tiramos quente de nossas casas no dia em que saímos para ir até você; mas agora, eis que está seco, e se tornou mofado.
13 Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
Estas peles de vinho, que enchemos, eram novas; e eis que estão rasgadas. Estas nossas vestes e nossas sandálias ficaram velhas por causa da longa jornada”.
14 Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
Os homens experimentaram suas provisões, e não pediram conselho da boca de Iavé.
15 Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
Josué fez as pazes com eles, e fez um pacto com eles, para deixá-los viver. Os príncipes da congregação juraram a eles.
16 Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
Ao final de três dias após terem feito um pacto com eles, eles ouviram que eram seus vizinhos e que viviam entre eles.
17 Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
As crianças de Israel viajaram e vieram para suas cidades no terceiro dia. Agora suas cidades eram Gibeon, Chephirah, Beeroth, e Kiriath Jearim.
18 Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
Os filhos de Israel não os atacaram, porque os príncipes da congregação haviam jurado por Javé, o Deus de Israel. Toda a congregação murmurou contra os príncipes.
19 Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
Mas todos os príncipes disseram a toda a congregação: “Nós juramos a eles por Javé, o Deus de Israel”. Agora, portanto, não podemos tocá-los”.
20 Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
Faremos isso com eles, e os deixaremos viver; para que não haja ira sobre nós, por causa do juramento que fizemos a eles”.
21 Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
Os príncipes disseram a eles: “Deixem-nos viver”. Assim, eles se tornaram cortadores de madeira e gavetas de água para toda a congregação, como os príncipes haviam falado com eles.
22 Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
Josué os chamou, e falou com eles, dizendo: “Por que vocês nos enganaram, dizendo: 'Estamos muito longe de vocês', quando vivem entre nós?
23 Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
Portanto, agora vocês estão amaldiçoados, e alguns de vocês nunca deixarão de ser escravos, tanto cortadores de madeira quanto gavetas de água para a casa de meu Deus”.
24 Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
Responderam a Josué, e disseram: “Porque a seus servos certamente foi dito como Javé seu Deus ordenou a seu servo Moisés que lhe desse toda a terra, e que destruísse todos os habitantes da terra de antes de você. Por isso tivemos muito medo de nossas vidas por causa de vocês, e fizemos isto.
25 Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
Agora, eis que estamos em suas mãos. Faça-nos o que lhe parece bom e certo fazer”.
26 Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
Ele fez isso com eles, e os entregou da mão das crianças de Israel, para que eles não os matassem.
27 A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.
Naquele dia Josué lhes fez cortadores de madeira e gavetas de água para a congregação e para o altar de Javé até hoje, no lugar que ele deveria escolher.