< Yoshuwa 9 >

1 To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
وقتی پادشاهان سرزمینهای همسایه از فتوحات بنی‌اسرائیل باخبر شدند، به خاطر حفظ جان و مال خود با هم متحد گشتند تا با یوشع و بنی‌اسرائیل بجنگند. اینها پادشاهان قبایل حیتی، اموری، کنعانی، فرزی، حوی و یبوسی بودند که در غرب رود اردن و سواحل دریای مدیترانه تا کوههای لبنان در شمال، زندگی می‌کردند.
2 suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
3 Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
اما مردم جبعون وقتی خبر پیروزی یوشع بر شهرهای اریحا و عای را شنیدند، برای نجات جان خود، عوض جنگ به حیله متوسل شدند. آنها گروهی را با لباسهای ژنده و کفشهای کهنه و پینه زده، الاغهایی با پالانهای مندرس و مقداری نان کپک زده خشک و چند مشک شراب که کهنه و وصله‌دار بودند نزد یوشع فرستادند.
4 sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
5 Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
6 Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
وقتی این گروه به اردوگاه اسرائیل در جلجال رسیدند، نزد یوشع و سایر مردان اسرائیلی رفته، گفتند: «ما از سرزمین دوری به اینجا آمده‌ایم تا از شما بخواهیم با ما پیمان صلح ببندید.»
7 Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
اما اسرائیلی‌ها گفتند: «ما چطور بدانیم که شما ساکن این سرزمین نیستید؟ چون اگر در این سرزمین ساکن باشید نمی‌توانیم با شما پیمان صلح ببندیم.»
8 Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
آنها به یوشع گفتند: «ما بندگان تو هستیم.» ولی یوشع از آنها پرسید: «شما چه کسانی هستید و از کجا آمده‌اید؟»
9 Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
گفتند: «ما بندگانت از یک سرزمین دور به اینجا آمده‌ایم؛ زیرا شهرت خداوند، خدایتان به گوش ما رسیده است و شنیده‌ایم که او چه کارهای بزرگی در مصر کرد
10 da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
و چه بلایی بر سر دو پادشاه اموری که در طرف شرق اردن بودند یعنی سیحون، پادشاه حشبون و عوج، پادشاه باشان که در عشتاروت حکومت می‌کرد، آورد.
11 Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
پس بزرگان و مردم ما از ما خواستند که توشه‌ای برای سفر طولانی بگیریم و به حضور شما بیاییم و بگوییم که ما بندگان شما هستیم و از شما می‌خواهیم با ما پیمان صلح ببندید.
12 Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
وقتی عازم سفر شدیم این نانها تازه از تنور درآمده بودند، اما حالا چنانکه می‌بینید خشک شده و کپک زده‌اند!
13 Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
این مشکهای شراب در آغاز سفر، نو بودند، اما حالا کهنه شده و ترکیده‌اند! لباسها و کفشهای ما به سبب طولانی بودن راه، مندرس شده‌اند.»
14 Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
یوشع و بزرگان اسرائیل با دیدن توشهٔ آنها، حرفهایشان را باور کردند و بدون آنکه با خداوند مشورت نمایند، یوشع با آنها پیمان صلح بست و قول داد که ایشان را از بین نبرد و بزرگان اسرائیل نیز قسم خوردند که این پیمان را نشکنند.
15 Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
16 Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
هنوز سه روز از این موضوع نگذشته بود که معلوم شد این گروه مسافر از همسایگانشان در آن سرزمین هستند و در همان نزدیکی زندگی می‌کنند!
17 Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
بنی‌اسرائیل در مسیر پیشروی خود، سه روز بعد به شهرهای ایشان رسیدند. (نام این شهرها جبعون، کفیره، بئیروت و قریه یعاریم بود.)
18 Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
اما به خاطر سوگندی که بزرگان اسرائیل به نام خداوند، خدای اسرائیل یاد کرده بودند نتوانستند آنها را از بین ببرند. اسرائیلی‌ها به بزرگان قوم اعتراض کردند،
19 Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
اما آنها در جواب گفتند: «ما به نام یهوه، خدای اسرائیل سوگند خورده‌ایم که به آنها صدمه‌ای نزنیم.
20 Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
پس باید به سوگند خود وفا نموده، بگذاریم که زنده بمانند؛ چون اگر پیمانی را که با آنان بسته‌ایم بشکنیم، خشم خداوند بر ما افروخته خواهد شد.»
21 Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
سپس اضافه کردند: «بگذارید ایشان زنده بمانند و برای ما هیزم بشکنند و آب بیاورند.»
22 Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
یوشع جبعونی‌ها را احضار کرده، گفت: «چرا ما را فریب داده، گفتید که از سرزمین بسیار دور آمده‌اید و حال آنکه همسایهٔ نزدیک ما هستید؟
23 Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
پس شما زیر لعنت خواهید بود و بعد از این باید همیشه به عنوان غلام برای خانهٔ خدای ما هیزم بشکنید و آب مورد نیاز را تهیه کنید.»
24 Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
آنها گفتند: «چون شنیده بودیم که خداوند، خدای شما به خدمتگزار خود موسی دستور داده بود تمام این سرزمین را تصرف نماید و ساکنانش را نابود کند، پس بسیار ترسیدیم و به خاطر نجات جان خود این کار را کردیم.
25 Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
ولی حالا در اختیار شما هستیم، هر طور که صلاح می‌دانید با ما رفتار کنید.»
26 Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
یوشع به مردم اسرائیل اجازه نداد آنها را بکشند،
27 A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.
و ایشان را برای شکستن هیزم و کشیدن آب برای مردم اسرائیل و مذبح خداوند تعیین نمود. ایشان تا امروز به کار خود در جایی که خداوند برای عبادت تعیین کرده است ادامه می‌دهند.

< Yoshuwa 9 >