< Yoshuwa 9 >

1 To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
Og det skete, der alle Kongerne, som vare paa denne Side Jordanen, i Bjerglandet og i Lavlandet og paa hele Kysten af det store Hav tværs overfor Libanon, samt Hethiterne og Amoriterne, Kananiterne og Feresiterne, Heviterne og Jebusiterne, hørte det:
2 suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
Da samlede de sig til Hobe at stride imod Josva og imod Israel endrægteligen.
3 Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
Da Indbyggerne af Gibeon havde hørt, hvad Josva havde gjort ved Jeriko og Ai,
4 sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
da handlede ogsaa de med List og gik hen og gave sig ud for Sendebud; og de toge gamle Sække paa deres Asener og gamle sønderrevne og bødede Læderflasker til Vin
5 Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
og gamle og lappede Sko paa deres Fødder og gamle Klæder paa sig, og alt Brødet til deres Tæring var tørt og mullent.
6 Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
Og de gik til Josva i Lejren ved Gilgal, og de sagde til ham og til Israels Mænd: Vi ere komne fra et langt fra liggende Land, saa gører nu Pagt med os.
7 Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
Da sagde Israels Mænd til Heviten: Maaske du bor midt iblandt os, hvorledes kunne vi da gøre Pagt med dig.
8 Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
Og de sagde til Josva: Vi ere dine Tjenere; og Josva sagde til dem: Hvo ere I, og hvorfra komme I?
9 Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
Og de sagde til ham: Dine Tjenere ere komne fra et saa re langt fra liggende Land for Herren din Guds Navns Skyld; thi vi have hørt hans Rygte og alt det, som han gjorde i Ægypten.
10 da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
Og alt det, som han gjorde ved Amoriternes to Konger, som vare paa hin Side Jordanen, ved Sihon, Kongen i Hesbon, og ved Og, Kongen i Basan, som var i Astharoth.
11 Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
Derfor sagde vore Ældste og alle vort Lands Indbyggere til os saalunde: Tager Tæring med eder paa Vejen og gaar dem i Møde, og siger til dem: Vi ere eders Tjenere, saa gører nu Pagt med os.
12 Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
Dette er vort Brød, det toge vi varmt med os paa Rejsen fra vore Huse den Dag, vi gik ud for at vandre til eder; men se, nu er det tørt, og det er mullent.
13 Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
Og disse ere Læderflasker til Vin, som vi fyldte, der de vare nye, se, de ere og sønderrevne; og disse vore Klæder og vore Sko ere blevne gamle for denne saare lange Vejs Skyld.
14 Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
Saa toge Mændene af deres Rejsekost, og de spurgte ikke Herrens Mund ad.
15 Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
Og Josva gjorde Fred med dem og gjorde Pagt med dem, at han vilde lade dem leve; og Menighedens Fyrster tilsvore dem det.
16 Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
Men det skete, der tre Dage vare til Ende, efter at de havde gjort Pagt med dem, da hørte de, at de vare nær hos dem, og at de boede midt iblandt dem.
17 Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
Thi der Israels Børn rejste frem, da kom de paa den tredje Dag til deres Stæder; og deres Stæder vare Gibeon og Kefira og Beeroth og Kirjath-Jearim.
18 Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
Og Israels Børn ihjelsloge dem ikke; thi Menighedens Fyrster havde tilsvoret dem ved Herren, Israels Gud, og al Menigheden knurrede mod Fyrsterne.
19 Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
Da sagde alle Fyrsterne til hele Menigheden: Vi have tilsvoret dem ved Herren, Israels Gud; derfor kunne vi nu ikke røre dem.
20 Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
Dette ville vi gøre dem: Vi ville lade dem leve, at der ikke skal komme en Vrede over os for den Eds Skyld, som vi have tilsvoret dem.
21 Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
Fremdeles sagde Fyrsterne til dem: Lader dem leve, at de maa være Vedhuggere og Vanddragere for hele Menigheden, ligesom Fyrsterne have sagt til dem.
22 Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
Da kaldte Josva ad dem og talede til dem og sagde: Hvi bedroge I os og sagde: Vi bo saare langt fra eder, og I bo dog midt iblandt os?
23 Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
Derfor skulle I nu være forbandede, saa at der ikke skal være nogen iblandt eder, som jo er Træl, Vedhugger eller Vanddrager til min Guds Hus.
24 Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
Og de svarede Josva og sagde: Fordi det blev dine Tjenere sikkert tilkendegivet, hvad Herren din Gud bød Mose sin Tjener, at han vilde give eder alt Landet og ødelægge alle Landets Indbyggere for eders Ansigt, saa frygtede vi saare for vort Liv for eders Ansigt og have gjort denne Gerning.
25 Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
Men nu, se, vi ere i din Haand; som det er godt og som det er ret for dine Øjne at gøre os, det gør!
26 Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
Og han gjorde saaledes mod dem; og han reddede dem fra Israels Børns Haand, og de sloge dem ikke ihjel.
27 A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.
Og Josva satte dem paa den samme Dag til Vedhuggere og Vanddragere for Menigheden og for Herrens Alter indtil denne Dag, ved det Sted, som han vilde udvælge.

< Yoshuwa 9 >