< Yoshuwa 8 >
1 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoro; kada ka karaya. Ka ɗauki dukan sojojin ku kai wa Ai hari, gama na ba ka nasara a kan sarkin Ai, mutanensa, birninsa da kuma ƙasarsa.
Gospod je rekel Józuetu: »Ne boj se niti ne bodi zaprepaden. S seboj vzemi vse bojno ljudstvo in se dvigni, pojdi gor do Aja. Glej, v tvojo roko sem izročil ajskega kralja, njegovo ljudstvo, njegovo mesto in njegovo deželo.
2 Za ku yi wa Ai yadda kuka yi wa Yeriko da sarkinta, sai dai za ku kwashe ganima da dabbobinta su zama naku. Ku yi kwanto a bayan birnin.”
Aju in njegovemu kralju boš storil, kakor si storil Jerihi in njenemu kralju. Samo njegov plen in njegovo živino si boste zaplenili. Zadaj za mestom si postavi zasedo.«
3 Yoshuwa da dukan sojojin suka fita su kai wa Ai hari. Sai ya zaɓi sojojinsa waɗanda suka fi saura duka iya yaƙi guda dubu talatin, ya tura su da dad dare
Tako je Józue vstal in vse bojno ljudstvo, da gredo gor zoper Aj. Józue je izbral trideset tisoč močnih junaških mož in jih ponoči odposlal.
4 ya ba su umarni ya ce, “Ku ji da kyau, za ku yi kwanto a bayan birnin, kada ku yi nisa da birnin. Kowannenku yă kasance a faɗake.
Zapovedal jim je, rekoč: »Glejte, prežali boste v zasedi zoper mesto, torej za mestom. Ne pojdite zelo daleč od mesta, temveč vsi bodite pripravljeni.
5 Ni da waɗanda suke tare da ni za mu nufi birnin, a lokacin da mutanen suka taso mana yadda suka yi dā, sai mu guje musu.
Jaz in vse ljudstvo, ki je z menoj, se bomo približali mestu in zgodilo se bo, ko bodo prišli ven zoper nas, kakor prvič, da bomo pobegnili pred njimi,
6 Za su bi mu har su yi nisa da birnin, gama za su ce, ‘Suna gudu kamar yadda suka yi dā.’ Saboda haka lokacin da muka guje musu,
(kajti prišli bodo ven za nami), dokler jih ne bomo pritegnili iz mesta, kajti rekli bodo: ›Pred nami bežijo, kakor prvič.‹ Zato bomo pobegnili pred njimi.
7 sai ku tashi daga inda kuka yi kwanto, ku ci birnin da yaƙi, Ubangiji Allahnku zai ba da shi a hannunku.
Potem boste vstali iz zasede in se polastili mesta, kajti Gospod, vaš Bog, ga bo izročil v vašo roko.
8 Lokacin da kuka ƙwace birnin, sai ku sa masa wuta. Ku yi abin da Ubangiji ya umarta. Ku tabbata kun yi abubuwan da na ce.”
Zgodilo se bo, ko boste zavzeli mesto, da boste požgali mesto. Glede na Gospodovo zapoved boste storili. Poglejte, zapovedal sem vam.«
9 Sai Yoshuwa ya sallame su, suka kuma tafi wurin da za su yi kwanto, suka kwanta suna fako tsakanin Betel da Ai, yamma da Ai, amma Yoshuwa ya kwana tare da mutanen.
Józue jih je torej poslal naprej in odšli so, da ležijo v zasedi in ostanejo med Betelom in Ajem, na zahodni strani Aja. Toda Józue je to noč prenočil med ljudstvom.
10 Kashegari da sassafe Yoshuwa ya tattara mutanensa, sai shi da shugabannin Isra’ilawa suka sha gaba suka taka zuwa Ai.
Józue je vstal zgodaj zjutraj, preštel ljudstvo in odšel gor, on in Izraelovi starešine, pred ljudstvo Aja.
11 Dukan sojojin da suke tare da shi suka nufi birnin, da suka kai kuwa sai suka kafa sansaninsu a arewancin Ai. Tsakaninsu da Ai akwai kwari.
Vse ljudstvo, celo bojno ljudstvo, ki je bilo z njim, je odšlo gor, se približalo, prišlo pred mesto in se utaborilo na severni strani Aja. Torej tam je bila dolina med njimi in Ajem.
12 Yoshuwa ya sa mutum dubu biyar suka yi kwanto tsakanin Betel da Ai, a yammancin birnin.
Vzel je okoli pet tisoč mož in jih postavil, da ležijo v zasedi med Betelom in Ajem, na zahodni strani mesta.
13 Mutanen suka kafa sansaninsu arewa da birnin, sansani na’yan kwanto kuwa yana yamma da birnin, amma Yoshuwa ya kwana a kwarin.
Ko so postavili ljudstvo, torej vso vojsko, ki je bila na severu mesta in svoje prežavce v zasedi na zahodni strani mesta, je to noč Józue odšel v sredo doline.
14 Sa’ad da sarkin Ai ya ga haka, shi da duk mutanen birnin suka hanzarta da sassafe don su gamu da Isra’ilawa, su yi yaƙi da su a wani wurin da yake fuskantar Araba. Amma bai san cewa an yi masa kwanto a bayan birnin ba.
Ko je kralj Aja to videl, se je pripetilo, da so pohiteli in zgodaj vstali in možje iz mesta so odšli ven zoper Izraela, da se bojujejo, on in vse njegovo ljudstvo, ob določenem času pred ravnino. Toda ni vedel, da so bili za mestom zoper njega prežavci v zasedi.
15 Yoshuwa da duk Isra’ilawa suka bari aka fafare su, sai suka gudu zuwa cikin jeji.
Józue in ves Izrael so se pretvarjali kakor bi bili poraženi pred njimi in pobegnili po poti divjine.
16 Aka kira duk mazan Ai su fafare su, suka kuwa fafari Yoshuwa, aka yaudare su suka yi nisa da birnin.
Vse ljudstvo, ki je bilo v Aju, je bilo sklicano skupaj, da jih zasledujejo. Zasledovali so Józueta in bili so pritegnjeni proč iz mesta.
17 Ba namijin da ya rage a Ai ko Betel da bai fita don yă fafari Isra’ilawa ba. Suka bar birnin a buɗe, suka tafi fafarar Isra’ilawa.
V Aju ali v Betelu ni ostal niti mož, ki ne bi odšel ven za Izraelom in mesto so pustili odprto in sledili za Izraelom.
18 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka riƙe māshin da yake hannunka ka nuna wajen Ai, gama zan ba da birnin a hannunka.” Yoshuwa kuwa ya miƙa māshin ta wajen Ai.
Gospod je rekel Józuetu: »Iztegni sulico, ki je v tvoji roki, zoper Aj, kajti jaz ga bom dal v tvojo roko.« Józue je zoper mesto iztegnil sulico, ki jo je imel v svoji roki.
19 Da yin haka kuwa sai mutanen da suka yi kwanto suka tashi nan da nan daga inda suke, suka nufi birnin a guje, suka shiga suka ci birnin da yaƙi, suka kuma cinna mata wuta da sauri.
Zaseda je hitro vstala iz svojega kraja in stekli so takoj, ko je iztegnil svojo roko. Vstopili so v mesto, ga zavzeli, pohiteli in mesto zažgali.
20 Mutanen Ai suka juya suka ga hayaƙin birninsu yana tashi sama, amma ba yadda za su iya tsira ta ko’ina, gama Isra’ilawan da suke gudu zuwa cikin jeji suka juya suka fara fafarar waɗanda suke fafararsu.
Ko so možje iz Aja pogledali za seboj, so videli in glej, dim iz mesta se je dvigoval proti nebu in niso imeli moči, da pobegnejo to pot ali tisto pot. Ljudstvo, ki je bežalo k divjini, se je obrnilo nazaj proti zasledovalcem.
21 Lokacin da Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka ga waɗanda suka yi kwanto sun ci birnin da yaƙi, hayaƙi kuwa ya cika birnin, sai suka juya suka kai wa mutanen Ai hari.
Ko je Józue in ves Izrael videl, da je zaseda zavzela mesto in da se iz mesta dviguje dim, potem so se ponovno obrnili in usmrtili može iz Aja.
22 Mutanen da suka yi kwanto su ma suka fito daga birnin suka tasar musu, ya zama an kama su a tsakiya, ga Isra’ilawa daga kowane gefe. Isra’ilawa kuwa suka karkashe su duka ba su bar wani da rai ba, ba kuma wanda ya tsere.
In drugi so izšli iz mesta zoper njih. Tako so bili v sredi Izraela, nekateri na tej strani in nekateri na oni strani in udarili so jih tako, da nobenega izmed njih niso pustili ostati ali pobegniti.
23 Amma suka tafi da sarkin Ai da rai suka kawo shi wurin Yoshuwa.
Kralja Aja so prijeli živega in ga privedli pred Józueta.
24 Da Isra’ilawa suka gama kashe duk mutanen Ai a filaye da kuma a cikin jeji inda suka fafare su, kuma da aka karkashe kowane mutumin Ai da takobi sai dukan Isra’ilawa suka koma Ai suka karkashe duk waɗanda suke cikinsa.
Ko je Izrael naredil konec pobijanju vseh prebivalcev Aja na polju, v divjini, kjer so jih zasledovali in ko so vsi padli pod ostrino meča, dokler niso bili použiti, se je pripetilo, da so se vsi Izraelci vrnili v Aj in ga udarili z ostrino meča.
25 A ranan nan, dukan mutanen Ai da aka kashe, mutum dubu goma sha biyu ne maza da mata.
Bilo je tako, da je bilo vseh, ki so ta dan padli, tako mož in žensk, dvanajst tisoč, torej vsi možje iz Aja.
26 Gama Yoshuwa bai janye hannunsa da yake riƙe da māshinsa ba har sai da ya hallaka dukan mazaunan Ai.
Kajti Józue svoje roke, s katero je iztegnil sulico, ni potegnil nazaj, dokler ni popolnoma uničil vseh prebivalcev Aja.
27 Amma Isra’ilawa suka kwashe ganima da dabbobin birnin nan yadda Ubangiji ya umarci Yoshuwa.
Samo živino in ukradeno blago iz mesta si je Izrael vzel za plen, glede na Gospodovo besedo, ki jo je zapovedal Józuetu.
28 Yoshuwa kuwa ya ƙone Ai, ya mai da ita tarin ƙasa, ta zama kufai har wa yau.
Józue je požgal Aj in ga naredil kup na veke, opustošenje do današnjega dne.
29 Ya rataye sarkin Ai a kan itace, ya bar shi a can har yamma. Da rana ta fāɗi, Yoshuwa ya umarta a ɗauke gawar sarkin a jefa a gaban ƙofar birnin. Suka kuma tara manyan duwatsu a kan gawar, tsibin na nan har wa yau.
Ajskega kralja je obesil na drevo do večera in takoj, ko je sonce zašlo, je Józue zapovedal, da njegovo truplo vzamejo dol iz drevesa in ga odvržejo pri vhodu velikih vrat mesta in nad njim naložijo velik kup kamenja, ki ostaja do tega dne.
30 Yoshuwa kuwa ya yi wa Ubangiji, Allah na Isra’ila bagade a Dutsen Ebal,
Potem je Józue zgradil oltar Gospodu, Izraelovemu Bogu, na gori Ebál,
31 kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarci Isra’ilawa. Ya gina bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Littafin Dokoki na Musa, bagade na duwatsun da ba a sassaƙa su ba, waɗanda ba wani ƙarfen da ya taɓa su. Suka miƙa wa Ubangiji hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kai.
kakor je Gospodov služabnik Mojzes zapovedal Izraelovim otrokom, kakor je to zapisano v knjigi Mojzesove postave, oltar iz celih kamnov, nad katere noben človek ni dvignil nobenega železa in na njem so darovali žgalne daritve Gospodu in žrtvovali mirovne daritve.
32 A can, a gaban Isra’ilawa, Yoshuwa ya rubuta dokokin Musa a kan duwatsun.
Na kamne je napisal prepis iz Mojzesove postave, ki jo je napisal v prisotnosti Izraelovih otrok.
33 Sai Isra’ilawa duka, da baƙi, da haifaffun gida, da dattawansu, da shugabanninsu, da alƙalansu, suka tsaya a gefe-gefen akwatin alkawarin Ubangiji, suna fuskantar waɗanda suke ɗauke da shi, wato, firistoci waɗanda su ne Lawiyawa. Rabin mutanen suka tsaya a gaban Dutsen Gerizim, rabinsu kuma suka tsaya a gaban Dutsen Ebal, kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya riga ya umarta, cewa su sa wa mutanen Isra’ilawa albarka.
Ves Izrael, njihove starešine, častniki in njihovi sodniki, so stali na tej strani skrinje in na oni strani, pred duhovniki Lévijevci, ki so nosili skrinjo Gospodove zaveze, kakor tudi tujec, kakor ta, ki je bil rojen med njimi. Polovica izmed njih nasproti gore Garizím in polovica izmed njih nasproti gore Ebál, kakor je Gospodov služabnik Mojzes prej zapovedal, da bodo blagoslovili izraelsko ljudstvo.
34 Bayan haka, Yoshuwa ya karanta duk abin da yake a cikin Dokoki, albarku da la’anoni, kamar yadda suke a rubuce a cikin Littafin Dokoki.
Potem je bral vse besede iz postave, blagoslove in prekletstva, glede na vse, kar je zapisano v knjigi postave.
35 Babu wata kalmar da Musa ya umarta da Yoshuwa bai karanta wa dukan taron Isra’ilawa ba, haɗe da mata, da yara, da baƙin da suke zama tare da su.
Ni bilo besede od vsega, kar je Mojzes zapovedal, česar Józue ni prebral pred vso Izraelovo skupnostjo, z ženskami, malčki in tujci, ki so bili seznanjeni med njimi.