< Yoshuwa 8 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoro; kada ka karaya. Ka ɗauki dukan sojojin ku kai wa Ai hari, gama na ba ka nasara a kan sarkin Ai, mutanensa, birninsa da kuma ƙasarsa.
Yahweh disse a Joshua: “Não tenha medo, e não fique consternado. Leve todos os guerreiros com você, e levante-se, vá até Ai. Eis que eu entreguei em suas mãos o rei de Ai, com seu povo, sua cidade e sua terra.
2 Za ku yi wa Ai yadda kuka yi wa Yeriko da sarkinta, sai dai za ku kwashe ganima da dabbobinta su zama naku. Ku yi kwanto a bayan birnin.”
Fareis com Ai e seu rei como fizestes com Jericó e seu rei, exceto que tomareis seus bens e seu gado para vós. Preparai uma emboscada para a cidade por trás dela”.
3 Yoshuwa da dukan sojojin suka fita su kai wa Ai hari. Sai ya zaɓi sojojinsa waɗanda suka fi saura duka iya yaƙi guda dubu talatin, ya tura su da dad dare
Então Joshua levantou-se, com todos os guerreiros, para ir até Ai. Joshua escolheu trinta mil homens, os poderosos homens de valor, e os enviou à noite.
4 ya ba su umarni ya ce, “Ku ji da kyau, za ku yi kwanto a bayan birnin, kada ku yi nisa da birnin. Kowannenku yă kasance a faɗake.
Ele os ordenou, dizendo: “Eis que jazereis numa emboscada contra a cidade, atrás da cidade”. Não se afastem muito da cidade, mas estejam todos prontos.
5 Ni da waɗanda suke tare da ni za mu nufi birnin, a lokacin da mutanen suka taso mana yadda suka yi dā, sai mu guje musu.
Eu e todas as pessoas que estão comigo nos aproximaremos da cidade. Acontecerá, quando eles saírem contra nós, como no início, que fugiremos diante deles.
6 Za su bi mu har su yi nisa da birnin, gama za su ce, ‘Suna gudu kamar yadda suka yi dā.’ Saboda haka lokacin da muka guje musu,
Eles sairão atrás de nós até que os tenhamos afastado da cidade; pois dirão: 'Eles fogem diante de nós, como na primeira vez'. Assim, fugiremos diante deles,
7 sai ku tashi daga inda kuka yi kwanto, ku ci birnin da yaƙi, Ubangiji Allahnku zai ba da shi a hannunku.
e vocês se levantarão da emboscada e tomarão posse da cidade; pois Yahweh, seu Deus, a entregará em suas mãos.
8 Lokacin da kuka ƙwace birnin, sai ku sa masa wuta. Ku yi abin da Ubangiji ya umarta. Ku tabbata kun yi abubuwan da na ce.”
Será, quando tiverdes tomado a cidade, que poreis fogo à cidade. Você fará isso de acordo com a palavra de Iavé. Eis que eu te ordenei”.
9 Sai Yoshuwa ya sallame su, suka kuma tafi wurin da za su yi kwanto, suka kwanta suna fako tsakanin Betel da Ai, yamma da Ai, amma Yoshuwa ya kwana tare da mutanen.
Joshua os enviou; e eles foram montar a emboscada, e ficaram entre Betel e Ai, no lado oeste de Ai; mas Joshua ficou entre o povo naquela noite.
10 Kashegari da sassafe Yoshuwa ya tattara mutanensa, sai shi da shugabannin Isra’ilawa suka sha gaba suka taka zuwa Ai.
Josué levantou-se cedo pela manhã, reuniu o povo e subiu, ele e os anciãos de Israel, diante do povo para Ai.
11 Dukan sojojin da suke tare da shi suka nufi birnin, da suka kai kuwa sai suka kafa sansaninsu a arewancin Ai. Tsakaninsu da Ai akwai kwari.
Todo o povo, mesmo os homens de guerra que estavam com ele, subiram e se aproximaram, e vieram diante da cidade e acamparam no lado norte de Ai. Agora havia um vale entre ele e Ai.
12 Yoshuwa ya sa mutum dubu biyar suka yi kwanto tsakanin Betel da Ai, a yammancin birnin.
Ele levou cerca de cinco mil homens, e os colocou numa emboscada entre Betel e Ai, no lado oeste da cidade.
13 Mutanen suka kafa sansaninsu arewa da birnin, sansani na’yan kwanto kuwa yana yamma da birnin, amma Yoshuwa ya kwana a kwarin.
Então eles colocaram o povo, mesmo todo o exército que estava no norte da cidade, e sua emboscada no oeste da cidade; e Josué foi naquela noite para o meio do vale.
14 Sa’ad da sarkin Ai ya ga haka, shi da duk mutanen birnin suka hanzarta da sassafe don su gamu da Isra’ilawa, su yi yaƙi da su a wani wurin da yake fuskantar Araba. Amma bai san cewa an yi masa kwanto a bayan birnin ba.
Quando o rei de Ai o viu, eles apressaram-se e se levantaram cedo, e os homens da cidade saíram contra Israel para lutar, ele e todo seu povo, no momento designado, diante do Arabah; mas ele não sabia que havia uma emboscada contra ele atrás da cidade.
15 Yoshuwa da duk Isra’ilawa suka bari aka fafare su, sai suka gudu zuwa cikin jeji.
Josué e todo Israel fizeram como se tivessem sido espancados antes deles, e fugiram pelo caminho do deserto.
16 Aka kira duk mazan Ai su fafare su, suka kuwa fafari Yoshuwa, aka yaudare su suka yi nisa da birnin.
Todas as pessoas que estavam na cidade foram convocadas para persegui-los. Eles perseguiram Josué, e foram afastados da cidade.
17 Ba namijin da ya rage a Ai ko Betel da bai fita don yă fafari Isra’ilawa ba. Suka bar birnin a buɗe, suka tafi fafarar Isra’ilawa.
Não havia um homem em Ai ou Betel que não tivesse saído depois de Israel. Eles deixaram a cidade aberta, e perseguiram Israel.
18 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka riƙe māshin da yake hannunka ka nuna wajen Ai, gama zan ba da birnin a hannunka.” Yoshuwa kuwa ya miƙa māshin ta wajen Ai.
Yahweh disse a Joshua: “Estenda o dardo que está em sua mão em direção a Ai, pois eu o darei em sua mão”. Josué estendeu o martelo que estava em sua mão em direção à cidade.
19 Da yin haka kuwa sai mutanen da suka yi kwanto suka tashi nan da nan daga inda suke, suka nufi birnin a guje, suka shiga suka ci birnin da yaƙi, suka kuma cinna mata wuta da sauri.
A emboscada saiu rapidamente de seu lugar, e eles correram assim que ele estendeu sua mão e entrou na cidade e a pegou. Eles apressaram-se e incendiaram a cidade.
20 Mutanen Ai suka juya suka ga hayaƙin birninsu yana tashi sama, amma ba yadda za su iya tsira ta ko’ina, gama Isra’ilawan da suke gudu zuwa cikin jeji suka juya suka fara fafarar waɗanda suke fafararsu.
Quando os homens de Ai olharam atrás deles, viram, e eis que a fumaça da cidade subiu ao céu, e não tinham poder para fugir por este ou aquele caminho. As pessoas que fugiram para o deserto voltaram-se contra os perseguidores.
21 Lokacin da Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka ga waɗanda suka yi kwanto sun ci birnin da yaƙi, hayaƙi kuwa ya cika birnin, sai suka juya suka kai wa mutanen Ai hari.
Quando Josué e todo Israel viram que a emboscada havia tomado a cidade, e que a fumaça da cidade subia, então voltaram para trás e mataram os homens de Ai.
22 Mutanen da suka yi kwanto su ma suka fito daga birnin suka tasar musu, ya zama an kama su a tsakiya, ga Isra’ilawa daga kowane gefe. Isra’ilawa kuwa suka karkashe su duka ba su bar wani da rai ba, ba kuma wanda ya tsere.
Os outros saíram da cidade contra eles, então eles estavam no meio de Israel, alguns deste lado, e outros daquele lado. Eles os atingiram, de modo que não deixaram nenhum deles permanecer ou escapar.
23 Amma suka tafi da sarkin Ai da rai suka kawo shi wurin Yoshuwa.
Eles capturaram o rei de Ai vivo, e o trouxeram a Josué.
24 Da Isra’ilawa suka gama kashe duk mutanen Ai a filaye da kuma a cikin jeji inda suka fafare su, kuma da aka karkashe kowane mutumin Ai da takobi sai dukan Isra’ilawa suka koma Ai suka karkashe duk waɗanda suke cikinsa.
Quando Israel terminou de matar todos os habitantes de Ai no campo, no deserto em que os perseguiam, e todos eles haviam caído pelo fio da espada até serem consumidos, todo Israel voltou a Ai e a atingiu com o fio da espada.
25 A ranan nan, dukan mutanen Ai da aka kashe, mutum dubu goma sha biyu ne maza da mata.
Todos os que caíram naquele dia, tanto de homens como de mulheres, eram doze mil, até mesmo todo o povo de Ai.
26 Gama Yoshuwa bai janye hannunsa da yake riƙe da māshinsa ba har sai da ya hallaka dukan mazaunan Ai.
Pois Josué não retirou sua mão, com a qual estendeu o martelo, até ter destruído completamente todos os habitantes de Ai.
27 Amma Isra’ilawa suka kwashe ganima da dabbobin birnin nan yadda Ubangiji ya umarci Yoshuwa.
Israel tomou para si somente o gado e os bens daquela cidade, de acordo com a palavra de Javé que ele ordenou a Josué.
28 Yoshuwa kuwa ya ƙone Ai, ya mai da ita tarin ƙasa, ta zama kufai har wa yau.
Então Josué queimou Ai e fez dela um monte para sempre, até os dias de hoje, até mesmo uma desolação.
29 Ya rataye sarkin Ai a kan itace, ya bar shi a can har yamma. Da rana ta fāɗi, Yoshuwa ya umarta a ɗauke gawar sarkin a jefa a gaban ƙofar birnin. Suka kuma tara manyan duwatsu a kan gawar, tsibin na nan har wa yau.
Ele enforcou o rei de Ai em uma árvore até a noite. Ao entardecer, Josué ordenou, e eles tiraram seu corpo da árvore e o jogaram na entrada do portão da cidade, e levantaram sobre ela um grande monte de pedras que permanece até hoje.
30 Yoshuwa kuwa ya yi wa Ubangiji, Allah na Isra’ila bagade a Dutsen Ebal,
Então Josué construiu um altar a Javé, o Deus de Israel, no Monte Ebal,
31 kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarci Isra’ilawa. Ya gina bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Littafin Dokoki na Musa, bagade na duwatsun da ba a sassaƙa su ba, waɗanda ba wani ƙarfen da ya taɓa su. Suka miƙa wa Ubangiji hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kai.
como Moisés, servo de Javé, ordenou aos filhos de Israel, como está escrito no livro da lei de Moisés: um altar de pedras não cortadas, sobre o qual ninguém tinha levantado ferro algum. Eles ofereceram holocaustos sobre ele a Iavé e sacrificaram ofertas de paz.
32 A can, a gaban Isra’ilawa, Yoshuwa ya rubuta dokokin Musa a kan duwatsun.
Ele escreveu lá nas pedras uma cópia da lei de Moisés, que ele escreveu na presença dos filhos de Israel.
33 Sai Isra’ilawa duka, da baƙi, da haifaffun gida, da dattawansu, da shugabanninsu, da alƙalansu, suka tsaya a gefe-gefen akwatin alkawarin Ubangiji, suna fuskantar waɗanda suke ɗauke da shi, wato, firistoci waɗanda su ne Lawiyawa. Rabin mutanen suka tsaya a gaban Dutsen Gerizim, rabinsu kuma suka tsaya a gaban Dutsen Ebal, kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya riga ya umarta, cewa su sa wa mutanen Isra’ilawa albarka.
Todo Israel, com seus anciãos, oficiais e juízes, estava em ambos os lados da arca diante dos sacerdotes levíticos, que levavam a arca do pacto de Iavé, tanto o estrangeiro quanto o nativo; metade deles em frente ao Monte Gerizim, e a outra metade em frente ao Monte Ebal, como Moisés, o servo de Iavé, havia ordenado no início, que abençoassem o povo de Israel.
34 Bayan haka, Yoshuwa ya karanta duk abin da yake a cikin Dokoki, albarku da la’anoni, kamar yadda suke a rubuce a cikin Littafin Dokoki.
Depois ele leu todas as palavras da lei, a bênção e a maldição, de acordo com tudo o que está escrito no livro da lei.
35 Babu wata kalmar da Musa ya umarta da Yoshuwa bai karanta wa dukan taron Isra’ilawa ba, haɗe da mata, da yara, da baƙin da suke zama tare da su.
Não havia uma palavra de tudo o que Moisés ordenou que Josué não lesse antes de toda a assembléia de Israel, com as mulheres, os pequenos, e os estrangeiros que estavam entre eles.

< Yoshuwa 8 >