< Yoshuwa 8 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoro; kada ka karaya. Ka ɗauki dukan sojojin ku kai wa Ai hari, gama na ba ka nasara a kan sarkin Ai, mutanensa, birninsa da kuma ƙasarsa.
INkosi yasisithi kuJoshuwa: Ungesabi, ungatshaywa luvalo; thatha kanye lawe bonke abantu bempi, usukume wenyukele eAyi; bona, nginikele esandleni sakho inkosi yeAyi, labantu bayo, lomuzi wayo, lelizwe layo.
2 Za ku yi wa Ai yadda kuka yi wa Yeriko da sarkinta, sai dai za ku kwashe ganima da dabbobinta su zama naku. Ku yi kwanto a bayan birnin.”
Uzakwenza-ke eAyi lenkosini yayo njengokwenza kwakho eJeriko lenkosini yayo. Kuphela impango yayo lezifuyo zayo lizaziphangela. Uzibekele abacathameli ngasemzini emva kwawo.
3 Yoshuwa da dukan sojojin suka fita su kai wa Ai hari. Sai ya zaɓi sojojinsa waɗanda suka fi saura duka iya yaƙi guda dubu talatin, ya tura su da dad dare
UJoshuwa wasesukuma labo bonke abantu bempi ukwenyukela eAyi; uJoshuwa wasekhetha amaqhawe alamandla ayizinkulungwane ezingamatshumi amathathu, wawathuma ebusuku.
4 ya ba su umarni ya ce, “Ku ji da kyau, za ku yi kwanto a bayan birnin, kada ku yi nisa da birnin. Kowannenku yă kasance a faɗake.
Wawalaya esithi: Bonani, lizawucathamela umuzi ngemva komuzi. Lingabi khatshana kakhulu lomuzi, kodwa lungani lonke.
5 Ni da waɗanda suke tare da ni za mu nufi birnin, a lokacin da mutanen suka taso mana yadda suka yi dā, sai mu guje musu.
Mina-ke labo bonke abantu abalami sizasondela emzini. Kuzakuthi-ke lapho bephuma ukumelana lathi njengakuqala sibaleke phambi kwabo.
6 Za su bi mu har su yi nisa da birnin, gama za su ce, ‘Suna gudu kamar yadda suka yi dā.’ Saboda haka lokacin da muka guje musu,
Njalo bazaphuma emva kwethu size sibadonse basuke emzini. Ngoba bazakuthi: Bayabaleka phambi kwethu njengakuqala. Ngakho sizabaleka phambi kwabo.
7 sai ku tashi daga inda kuka yi kwanto, ku ci birnin da yaƙi, Ubangiji Allahnku zai ba da shi a hannunku.
Lina-ke lizasukuma ekucathameni, liwuthumbe umuzi; ngoba iNkosi uNkulunkulu wenu izawunikela esandleni senu.
8 Lokacin da kuka ƙwace birnin, sai ku sa masa wuta. Ku yi abin da Ubangiji ya umarta. Ku tabbata kun yi abubuwan da na ce.”
Kuzakuthi-ke seliwuthumbile umuzi, liwutshise umuzi ngomlilo, lizakwenza njengokwelizwi leNkosi. Bonani, ngililayile.
9 Sai Yoshuwa ya sallame su, suka kuma tafi wurin da za su yi kwanto, suka kwanta suna fako tsakanin Betel da Ai, yamma da Ai, amma Yoshuwa ya kwana tare da mutanen.
UJoshuwa wasebathuma, baya ekucathameni, bahlala phakathi kweBhetheli leAyi, entshonalanga kweAyi, kodwa uJoshuwa walala phakathi kwabantu ngalobobusuku.
10 Kashegari da sassafe Yoshuwa ya tattara mutanensa, sai shi da shugabannin Isra’ilawa suka sha gaba suka taka zuwa Ai.
UJoshuwa wasevuka ekuseni kakhulu, wabala abantu, wenyuka, yena labadala bakoIsrayeli, phambi kwabantu, waya eAyi.
11 Dukan sojojin da suke tare da shi suka nufi birnin, da suka kai kuwa sai suka kafa sansaninsu a arewancin Ai. Tsakaninsu da Ai akwai kwari.
Labo bonke abantu bempi ababelaye benyuka, basondela, beza maqondana lomuzi, bamisa inkamba enyakatho kweAyi. Njalo kwakulesihotsha phakathi kwabo leAyi.
12 Yoshuwa ya sa mutum dubu biyar suka yi kwanto tsakanin Betel da Ai, a yammancin birnin.
Wasethatha phose amadoda azinkulungwane ezinhlanu, wawacathamisa phakathi kweBhetheli leAyi entshonalanga komuzi.
13 Mutanen suka kafa sansaninsu arewa da birnin, sansani na’yan kwanto kuwa yana yamma da birnin, amma Yoshuwa ya kwana a kwarin.
Lapho sebemisa abantu, lonke ibutho elalisenyakatho komuzi, labacathami ngasentshonalanga komuzi, uJoshuwa waya phakathi kwesihotsha ngalobobusuku.
14 Sa’ad da sarkin Ai ya ga haka, shi da duk mutanen birnin suka hanzarta da sassafe don su gamu da Isra’ilawa, su yi yaƙi da su a wani wurin da yake fuskantar Araba. Amma bai san cewa an yi masa kwanto a bayan birnin ba.
Kwasekusithi inkosi yeAyi ikubona, aphangisa avuka ngovivi; lamadoda omuzi aphuma impi emelane loIsrayeli, yona labantu bayo bonke, ngesikhathi esimisiweyo, phambi kwamagceke; kodwa yona yayingazi ukuthi kukhona abayicathameleyo emva komuzi.
15 Yoshuwa da duk Isra’ilawa suka bari aka fafare su, sai suka gudu zuwa cikin jeji.
UJoshuwa loIsrayeli basebetshaywa phambi kwawo, babaleka ngendlela yenkangala.
16 Aka kira duk mazan Ai su fafare su, suka kuwa fafari Yoshuwa, aka yaudare su suka yi nisa da birnin.
Kwasekubizwa bonke abantu ababesemzini ukuxotshana labo. Nxa bexotshana loJoshuwa badonswa basuka emzini.
17 Ba namijin da ya rage a Ai ko Betel da bai fita don yă fafari Isra’ilawa ba. Suka bar birnin a buɗe, suka tafi fafarar Isra’ilawa.
Njalo kakusalanga muntu eAyi kumbe eBhetheli, abangaphumanga ukulandela uIsrayeli; bawutshiya umuzi ukhamisile, baxotshana loIsrayeli.
18 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka riƙe māshin da yake hannunka ka nuna wajen Ai, gama zan ba da birnin a hannunka.” Yoshuwa kuwa ya miƙa māshin ta wajen Ai.
INkosi yasisithi kuJoshuwa: Yelulela umkhonto osesandleni sakho eAyi, ngoba ngizayinikela esandleni sakho. UJoshuwa waseselulela umkhonto osesandleni sakhe emzini.
19 Da yin haka kuwa sai mutanen da suka yi kwanto suka tashi nan da nan daga inda suke, suka nufi birnin a guje, suka shiga suka ci birnin da yaƙi, suka kuma cinna mata wuta da sauri.
Abacathemeyo basebesukuma masinyane endaweni yabo; bagijima esanda ukwelula isandla sakhe, bangena emzini, bawuthumba, baphangisa, bawutshisa umuzi ngomlilo.
20 Mutanen Ai suka juya suka ga hayaƙin birninsu yana tashi sama, amma ba yadda za su iya tsira ta ko’ina, gama Isra’ilawan da suke gudu zuwa cikin jeji suka juya suka fara fafarar waɗanda suke fafararsu.
Kwathi lapho amadoda eAyi enyemukula abona, khangela-ke, intuthu yomuzi yenyukela emazulwini, njalo ayengelandawo yokubalekela ngapha langapha, ngoba abantu ababebalekele enkangala baphendukela ababaxotshayo.
21 Lokacin da Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka ga waɗanda suka yi kwanto sun ci birnin da yaƙi, hayaƙi kuwa ya cika birnin, sai suka juya suka kai wa mutanen Ai hari.
Kwathi uJoshuwa loIsrayeli wonke bebona ukuthi abacathemeyo sebewuthumbile umuzi lokuthi intuthu yomuzi yenyuka, baphenduka batshaya amadoda eAyi.
22 Mutanen da suka yi kwanto su ma suka fito daga birnin suka tasar musu, ya zama an kama su a tsakiya, ga Isra’ilawa daga kowane gefe. Isra’ilawa kuwa suka karkashe su duka ba su bar wani da rai ba, ba kuma wanda ya tsere.
Lalaba baphuma emzini ukumelana lawo, aze aba phakathi kukaIsrayeli, abanye ngapha labanye ngale; basebewatshaya, kakwaze kwasala muntu kuwo, owasilayo kumbe owaphunyukayo.
23 Amma suka tafi da sarkin Ai da rai suka kawo shi wurin Yoshuwa.
Kodwa inkosi yeAyi bayibamba iphila, bayisondeza kuJoshuwa.
24 Da Isra’ilawa suka gama kashe duk mutanen Ai a filaye da kuma a cikin jeji inda suka fafare su, kuma da aka karkashe kowane mutumin Ai da takobi sai dukan Isra’ilawa suka koma Ai suka karkashe duk waɗanda suke cikinsa.
Kwasekusithi lapho uIsrayeli eseqedile ukubulala bonke abahlali beAyi egangeni, enkangala lapho ababebaxotshele khona, babewile bonke ngobukhali benkemba, baze baqedwa, uIsrayeli wonke wabuyela eAyi, bayitshaya ngobukhali benkemba.
25 A ranan nan, dukan mutanen Ai da aka kashe, mutum dubu goma sha biyu ne maza da mata.
Kwasekusithi, bonke abawayo mhlalokho, kusukela kwabesilisa kusiya kwabesifazana, babeyizinkulungwane ezilitshumi lambili, bonke abantu beAyi.
26 Gama Yoshuwa bai janye hannunsa da yake riƙe da māshinsa ba har sai da ya hallaka dukan mazaunan Ai.
Njalo uJoshuwa kasifinyezanga isandla sakhe ayelule umkhonto ngaso baze batshabalalisa bonke abahlali beAyi.
27 Amma Isra’ilawa suka kwashe ganima da dabbobin birnin nan yadda Ubangiji ya umarci Yoshuwa.
Kuphela izifuyo lempango yalowomuzi uIsrayeli waziphangela, njengelizwi leNkosi eyalilaya uJoshuwa.
28 Yoshuwa kuwa ya ƙone Ai, ya mai da ita tarin ƙasa, ta zama kufai har wa yau.
UJoshuwa waseyitshisa iAyi, wayimisa yaba yinqwaba phakade, unxiwa, kuze kube lamuhla.
29 Ya rataye sarkin Ai a kan itace, ya bar shi a can har yamma. Da rana ta fāɗi, Yoshuwa ya umarta a ɗauke gawar sarkin a jefa a gaban ƙofar birnin. Suka kuma tara manyan duwatsu a kan gawar, tsibin na nan har wa yau.
Lenkosi yeAyi wayiphanyeka esihlahleni kwaze kwaba yisikhathi santambama. Lekutshoneni kwelanga uJoshuwa walaya ukuthi bethule isidumbu sayo esihlahleni, basiphosele emnyango wesango lomuzi, bamisa phezu kwaso inqwaba enkulu yamatshe, ekhona kuze kube lamuhla.
30 Yoshuwa kuwa ya yi wa Ubangiji, Allah na Isra’ila bagade a Dutsen Ebal,
Khona uJoshuwa wayakhela iNkosi uNkulunkulu kaIsrayeli ilathi entabeni yeEbhali.
31 kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarci Isra’ilawa. Ya gina bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Littafin Dokoki na Musa, bagade na duwatsun da ba a sassaƙa su ba, waɗanda ba wani ƙarfen da ya taɓa su. Suka miƙa wa Ubangiji hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kai.
Njengokulaya kukaMozisi inceku yeNkosi kubantwana bakoIsrayeli, njengalokhu kubhalwe egwalweni lomlayo kaMozisi, ilathi lamatshe apheleleyo, okungazange kusetshenziswe nsimbi phezu kwalo. Basebenikela phezu kwalo eNkosini iminikelo yokutshiswa, bahlaba iminikelo yokuthula.
32 A can, a gaban Isra’ilawa, Yoshuwa ya rubuta dokokin Musa a kan duwatsun.
Wasebhala lapho ematsheni impinda yomlayo kaMozisi, ayibhala phambi kwabantwana bakoIsrayeli.
33 Sai Isra’ilawa duka, da baƙi, da haifaffun gida, da dattawansu, da shugabanninsu, da alƙalansu, suka tsaya a gefe-gefen akwatin alkawarin Ubangiji, suna fuskantar waɗanda suke ɗauke da shi, wato, firistoci waɗanda su ne Lawiyawa. Rabin mutanen suka tsaya a gaban Dutsen Gerizim, rabinsu kuma suka tsaya a gaban Dutsen Ebal, kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya riga ya umarta, cewa su sa wa mutanen Isra’ilawa albarka.
UIsrayeli wonke-ke, labadala babo, lezinduna, labahluleli babo, bema ngapha langapha komtshokotsho, beqondene labapristi, amaLevi, abathwala umtshokotsho wesivumelwano seNkosi, owezizwe njengowokuzalwa. Ingxenye yabo imaqondana lentaba yeGerizimi, lengxenye yabo maqondana lentaba yeEbhali, njengokulaya kukaMozisi inceku yeNkosi, ukubusisa abantu bakoIsrayeli kuqala.
34 Bayan haka, Yoshuwa ya karanta duk abin da yake a cikin Dokoki, albarku da la’anoni, kamar yadda suke a rubuce a cikin Littafin Dokoki.
Langemva kwalokho wamemezela wonke amazwi omlayo, isibusiso lesiqalekiso, njengakho konke okubhaliweyo egwalweni lomlayo.
35 Babu wata kalmar da Musa ya umarta da Yoshuwa bai karanta wa dukan taron Isra’ilawa ba, haɗe da mata, da yara, da baƙin da suke zama tare da su.
Akwabakho ilizwi kukho konke uMozisi akulayayo uJoshuwa angalimemezelanga phambi kwebandla lonke lakoIsrayeli labesifazana labantwanyana labezizweni ababehamba phakathi kwabo.

< Yoshuwa 8 >