< Yoshuwa 8 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoro; kada ka karaya. Ka ɗauki dukan sojojin ku kai wa Ai hari, gama na ba ka nasara a kan sarkin Ai, mutanensa, birninsa da kuma ƙasarsa.
Then Yahweh said to Joshua, “Do not be afraid or discouraged [because of what happened at] Ai. Lead all of your soldiers and go there again. I will help you to defeat the king of Ai, his people, and his city, and [enable you to take] his land.
2 Za ku yi wa Ai yadda kuka yi wa Yeriko da sarkinta, sai dai za ku kwashe ganima da dabbobinta su zama naku. Ku yi kwanto a bayan birnin.”
Your army will do to the people of Ai and their king like what you did to the people of Jericho and their king. But this time [I will permit you to] take all their possessions and keep them for yourselves. But first, tell some of your soldiers to [hide behind] the city [and] prepare to suddenly attack it.”
3 Yoshuwa da dukan sojojin suka fita su kai wa Ai hari. Sai ya zaɓi sojojinsa waɗanda suka fi saura duka iya yaƙi guda dubu talatin, ya tura su da dad dare
So Joshua led all his army toward Ai. He chose 30,000 of his best fighters/warriors and prepared to send them out during the night.
4 ya ba su umarni ya ce, “Ku ji da kyau, za ku yi kwanto a bayan birnin, kada ku yi nisa da birnin. Kowannenku yă kasance a faɗake.
He said to them, “Listen carefully. Some of you must hide on the other side of the city. Do not go far from the city. Just be ready [to attack].
5 Ni da waɗanda suke tare da ni za mu nufi birnin, a lokacin da mutanen suka taso mana yadda suka yi dā, sai mu guje musu.
I and the men who are with me will march toward the city [in the morning]. The men in the city will come out to fight us, like they did before. Then we will turn around and start to run away from them.
6 Za su bi mu har su yi nisa da birnin, gama za su ce, ‘Suna gudu kamar yadda suka yi dā.’ Saboda haka lokacin da muka guje musu,
They will think that we are running away from them like we did before. So they will chase us away from the city. While we are running away,
7 sai ku tashi daga inda kuka yi kwanto, ku ci birnin da yaƙi, Ubangiji Allahnku zai ba da shi a hannunku.
[those of you who are hiding come out and] rush into the city and capture it. Yahweh your God will enable you to conquer it.
8 Lokacin da kuka ƙwace birnin, sai ku sa masa wuta. Ku yi abin da Ubangiji ya umarta. Ku tabbata kun yi abubuwan da na ce.”
After you capture the city, burn it. Do what Yahweh has commanded us to do. Those are the orders I am giving to you.”
9 Sai Yoshuwa ya sallame su, suka kuma tafi wurin da za su yi kwanto, suka kwanta suna fako tsakanin Betel da Ai, yamma da Ai, amma Yoshuwa ya kwana tare da mutanen.
Then Joshua [prepared to] send some of them to [hide and] wait between Ai and Bethel, which was west of Ai. But Joshua stayed with his other soldiers that night.
10 Kashegari da sassafe Yoshuwa ya tattara mutanensa, sai shi da shugabannin Isra’ilawa suka sha gaba suka taka zuwa Ai.
Early the next morning, Joshua gathered his soldiers together. Then he and the other Israeli leaders led them up to Ai.
11 Dukan sojojin da suke tare da shi suka nufi birnin, da suka kai kuwa sai suka kafa sansaninsu a arewancin Ai. Tsakaninsu da Ai akwai kwari.
They all set up their tents close to Ai, just to the north of the city, where all the people of the city could see them. There was a valley between them and the city.
12 Yoshuwa ya sa mutum dubu biyar suka yi kwanto tsakanin Betel da Ai, a yammancin birnin.
Then Joshua chose about 5,000 men and told them to go and hide just west of the city, between Ai and Bethel.
13 Mutanen suka kafa sansaninsu arewa da birnin, sansani na’yan kwanto kuwa yana yamma da birnin, amma Yoshuwa ya kwana a kwarin.
So those men did that. The main group of soldiers was north of the city, and the others were hiding west of the city. That night Joshua went down into the valley.
14 Sa’ad da sarkin Ai ya ga haka, shi da duk mutanen birnin suka hanzarta da sassafe don su gamu da Isra’ilawa, su yi yaƙi da su a wani wurin da yake fuskantar Araba. Amma bai san cewa an yi masa kwanto a bayan birnin ba.
When the king of Ai saw the Israeli army, he and his soldiers got up early the next morning and quickly went out of the city to fight them. They went to a place east of the city, but they did not know that some Israeli soldiers were hiding behind the city.
15 Yoshuwa da duk Isra’ilawa suka bari aka fafare su, sai suka gudu zuwa cikin jeji.
Joshua and the Israeli soldiers [who were with him] allowed the army of Ai to push them back. They ran toward the desert.
16 Aka kira duk mazan Ai su fafare su, suka kuwa fafari Yoshuwa, aka yaudare su suka yi nisa da birnin.
The men in Ai were ordered to chase after Joshua and his men. So they left the city and started to pursue the Israelis.
17 Ba namijin da ya rage a Ai ko Betel da bai fita don yă fafari Isra’ilawa ba. Suka bar birnin a buɗe, suka tafi fafarar Isra’ilawa.
All the men of Ai and the men of Bethel pursued the Israeli army. They did not leave even one man in Ai to defend it. The [gates of the] city were left wide open.
18 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka riƙe māshin da yake hannunka ka nuna wajen Ai, gama zan ba da birnin a hannunka.” Yoshuwa kuwa ya miƙa māshin ta wajen Ai.
Then Yahweh said to Joshua, “[Lift up] your spear [and] point it toward Ai, because I am going to enable your soldiers to capture it!” So Joshua pointed [his spear] toward Ai.
19 Da yin haka kuwa sai mutanen da suka yi kwanto suka tashi nan da nan daga inda suke, suka nufi birnin a guje, suka shiga suka ci birnin da yaƙi, suka kuma cinna mata wuta da sauri.
When the Israeli men who were hiding saw that, they rushed out from the places where they were hiding and ran into the city. They quickly captured it and set it on fire.
20 Mutanen Ai suka juya suka ga hayaƙin birninsu yana tashi sama, amma ba yadda za su iya tsira ta ko’ina, gama Isra’ilawan da suke gudu zuwa cikin jeji suka juya suka fara fafarar waɗanda suke fafararsu.
When the men of Ai looked back, they saw smoke rising from their city. But they could not escape, because the Israeli troops stopped running away.
21 Lokacin da Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka ga waɗanda suka yi kwanto sun ci birnin da yaƙi, hayaƙi kuwa ya cika birnin, sai suka juya suka kai wa mutanen Ai hari.
Joshua and his men saw that the men who had been hiding had captured the city and were burning it, and they saw the smoke rising. So they turned around and started to attack the men of Ai.
22 Mutanen da suka yi kwanto su ma suka fito daga birnin suka tasar musu, ya zama an kama su a tsakiya, ga Isra’ilawa daga kowane gefe. Isra’ilawa kuwa suka karkashe su duka ba su bar wani da rai ba, ba kuma wanda ya tsere.
Meanwhile, the soldiers who had captured the city came out [and attacked them from the rear]. So the men of Ai were caught between the two groups of Israeli soldiers. None of the men of Ai escaped. The Israelis fought until they killed all of them. Only the king of Ai was still alive.
23 Amma suka tafi da sarkin Ai da rai suka kawo shi wurin Yoshuwa.
Then they seized the king of Ai and brought him to Joshua.
24 Da Isra’ilawa suka gama kashe duk mutanen Ai a filaye da kuma a cikin jeji inda suka fafare su, kuma da aka karkashe kowane mutumin Ai da takobi sai dukan Isra’ilawa suka koma Ai suka karkashe duk waɗanda suke cikinsa.
While they were fighting, the Israeli army pursued the men of Ai into the fields and into the desert, and killed all of them. Then they went to Ai and killed everyone who was there.
25 A ranan nan, dukan mutanen Ai da aka kashe, mutum dubu goma sha biyu ne maza da mata.
They killed 12,000 men and women.
26 Gama Yoshuwa bai janye hannunsa da yake riƙe da māshinsa ba har sai da ya hallaka dukan mazaunan Ai.
Joshua continued to point his spear [LIT] toward Ai, until all the people in Ai had been killed.
27 Amma Isra’ilawa suka kwashe ganima da dabbobin birnin nan yadda Ubangiji ya umarci Yoshuwa.
The Israeli soldiers took for themselves the animals and the other things that had belonged to the people of Ai, just like Yahweh had told Joshua that they should do.
28 Yoshuwa kuwa ya ƙone Ai, ya mai da ita tarin ƙasa, ta zama kufai har wa yau.
Joshua and his soldiers burned Ai city and caused it to become a pile of ruins. It is still like that today.
29 Ya rataye sarkin Ai a kan itace, ya bar shi a can har yamma. Da rana ta fāɗi, Yoshuwa ya umarta a ɗauke gawar sarkin a jefa a gaban ƙofar birnin. Suka kuma tara manyan duwatsu a kan gawar, tsibin na nan har wa yau.
Joshua hanged the king of Ai on a tree and left his corpse hanging there until the evening. At sunset Joshua told his men to take the king’s corpse down from the tree and to throw it on the ground at the city gate. [After they did that], they piled a lot of rocks on top of the corpse, and that pile of rocks is still there.
30 Yoshuwa kuwa ya yi wa Ubangiji, Allah na Isra’ila bagade a Dutsen Ebal,
Joshua [told his men to] build on Ebal Mountain an altar for Yahweh, the God [who is worshiped by] the Israeli people.
31 kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarci Isra’ilawa. Ya gina bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Littafin Dokoki na Musa, bagade na duwatsun da ba a sassaƙa su ba, waɗanda ba wani ƙarfen da ya taɓa su. Suka miƙa wa Ubangiji hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kai.
They built it just like Moses, the man who served God [well], had written previously in the laws [that God had given to him]. They made it from stones that had not been cut using iron tools. The Israelis then offered sacrifices to Yahweh that were burned completely on the altar. They also offered sacrifices to restore fellowship with Yahweh.
32 A can, a gaban Isra’ilawa, Yoshuwa ya rubuta dokokin Musa a kan duwatsun.
As the Israelis watched, Joshua wrote on stones the laws that [Yahweh had given] to Moses previously.
33 Sai Isra’ilawa duka, da baƙi, da haifaffun gida, da dattawansu, da shugabanninsu, da alƙalansu, suka tsaya a gefe-gefen akwatin alkawarin Ubangiji, suna fuskantar waɗanda suke ɗauke da shi, wato, firistoci waɗanda su ne Lawiyawa. Rabin mutanen suka tsaya a gaban Dutsen Gerizim, rabinsu kuma suka tsaya a gaban Dutsen Ebal, kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya riga ya umarta, cewa su sa wa mutanen Isra’ilawa albarka.
The Israeli leaders, the officials, the judges, and other Israelis were there, standing nearby. Many people who were not Israelis were also there. Half of the people stood [on one side of the valley] below Ebal Mountain, and the other half of the people stood [on the other side of the valley] below Gerizim Mountain. The sacred chest was [in the valley] between the two groups. That was what Moses had previously commanded that the people should do when [Yahweh was about to] bless them.
34 Bayan haka, Yoshuwa ya karanta duk abin da yake a cikin Dokoki, albarku da la’anoni, kamar yadda suke a rubuce a cikin Littafin Dokoki.
Then Joshua read [to the people] all that [Moses] had written previously. That included what Yahweh had taught them and the ways [that he promised] to bless them [if they obeyed his commands], or to curse them [if they disobeyed them].
35 Babu wata kalmar da Musa ya umarta da Yoshuwa bai karanta wa dukan taron Isra’ilawa ba, haɗe da mata, da yara, da baƙin da suke zama tare da su.
All the Israelis gathered together [to listen]—the men, the women, and the children. The (foreigners/people who were not Israelis) who were living among them also listened, while Joshua read all the commands that Moses had written.

< Yoshuwa 8 >