< Yoshuwa 8 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoro; kada ka karaya. Ka ɗauki dukan sojojin ku kai wa Ai hari, gama na ba ka nasara a kan sarkin Ai, mutanensa, birninsa da kuma ƙasarsa.
And he said Yahweh to Joshua may not you fear and may not you be dismayed take with you all [the] people of war and arise go up Ai see - I have given in hand your [the] king of Ai and people his and city his and land his.
2 Za ku yi wa Ai yadda kuka yi wa Yeriko da sarkinta, sai dai za ku kwashe ganima da dabbobinta su zama naku. Ku yi kwanto a bayan birnin.”
And you will do to Ai and to king its just as you did to Jericho and to king its only booty its and livestock its you will plunder for yourselves set for yourself an ambush for the city behind it.
3 Yoshuwa da dukan sojojin suka fita su kai wa Ai hari. Sai ya zaɓi sojojinsa waɗanda suka fi saura duka iya yaƙi guda dubu talatin, ya tura su da dad dare
And he arose Joshua and all [the] people of war to go up Ai and he chose Joshua thirty thousand man [the] mighty [men] of strength and he sent out them night.
4 ya ba su umarni ya ce, “Ku ji da kyau, za ku yi kwanto a bayan birnin, kada ku yi nisa da birnin. Kowannenku yă kasance a faɗake.
And he commanded them saying see you [are] lying in wait for the city behind the city may not you go far away from the city very and you will be all of you prepared.
5 Ni da waɗanda suke tare da ni za mu nufi birnin, a lokacin da mutanen suka taso mana yadda suka yi dā, sai mu guje musu.
And I and all the people which [is] with me we will draw near to the city and it will be that they will come out to meet us just as at the first [time] and we will flee before them.
6 Za su bi mu har su yi nisa da birnin, gama za su ce, ‘Suna gudu kamar yadda suka yi dā.’ Saboda haka lokacin da muka guje musu,
And they will come out after us until have drawn out we them from the city for they will say [they are] fleeing before us just as at the first [time] and we will flee before them.
7 sai ku tashi daga inda kuka yi kwanto, ku ci birnin da yaƙi, Ubangiji Allahnku zai ba da shi a hannunku.
And you you will arise from the ambush and you will take possession of the city and he will give it Yahweh God your in hand your.
8 Lokacin da kuka ƙwace birnin, sai ku sa masa wuta. Ku yi abin da Ubangiji ya umarta. Ku tabbata kun yi abubuwan da na ce.”
And it will be when have captured you the city you will set on fire the city with fire according to [the] word of Yahweh you will do see I have commanded you.
9 Sai Yoshuwa ya sallame su, suka kuma tafi wurin da za su yi kwanto, suka kwanta suna fako tsakanin Betel da Ai, yamma da Ai, amma Yoshuwa ya kwana tare da mutanen.
And he sent out them Joshua and they went to the ambush and they remained between Beth-el and between Ai from [the] west of Ai and he stayed Joshua in the night that in among the people.
10 Kashegari da sassafe Yoshuwa ya tattara mutanensa, sai shi da shugabannin Isra’ilawa suka sha gaba suka taka zuwa Ai.
And he rose early Joshua in the morning and he mustered the people and he went up he and [the] elders of Israel before the people Ai.
11 Dukan sojojin da suke tare da shi suka nufi birnin, da suka kai kuwa sai suka kafa sansaninsu a arewancin Ai. Tsakaninsu da Ai akwai kwari.
And all the people of war which [was] with him they went up and they approached and they came before the city and they encamped from [the] north of Ai and the valley ([was] between it *Q(k)*) and between Ai.
12 Yoshuwa ya sa mutum dubu biyar suka yi kwanto tsakanin Betel da Ai, a yammancin birnin.
And he took about five thousand man and he set them an ambush between Beth-el and between Ai from [the] west of the city.
13 Mutanen suka kafa sansaninsu arewa da birnin, sansani na’yan kwanto kuwa yana yamma da birnin, amma Yoshuwa ya kwana a kwarin.
And they set the people all the camp which [was] from [the] north of the city and rearguard its from [the] west of the city and he went Joshua in the night that in [the] middle of the valley.
14 Sa’ad da sarkin Ai ya ga haka, shi da duk mutanen birnin suka hanzarta da sassafe don su gamu da Isra’ilawa, su yi yaƙi da su a wani wurin da yake fuskantar Araba. Amma bai san cewa an yi masa kwanto a bayan birnin ba.
And it was when saw [the] king of Ai and they hurried and they rose early and they went out [the] men of the city to meet Israel for battle he and all people his to the appointed place before the Arabah and he not he knew that an ambush for him [was] behind the city.
15 Yoshuwa da duk Isra’ilawa suka bari aka fafare su, sai suka gudu zuwa cikin jeji.
And they were struck Joshua and all Israel before them and they fled [the] direction of the wilderness.
16 Aka kira duk mazan Ai su fafare su, suka kuwa fafari Yoshuwa, aka yaudare su suka yi nisa da birnin.
And they were called together all the people which ([was] in Ai *Q(K)*) to pursue after them and they pursued after Joshua and they were drawn out from the city.
17 Ba namijin da ya rage a Ai ko Betel da bai fita don yă fafari Isra’ilawa ba. Suka bar birnin a buɗe, suka tafi fafarar Isra’ilawa.
And not he remained anyone in Ai and Beth-el who not they went out after Israel and they left the city open and they pursued after Israel.
18 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka riƙe māshin da yake hannunka ka nuna wajen Ai, gama zan ba da birnin a hannunka.” Yoshuwa kuwa ya miƙa māshin ta wajen Ai.
And he said Yahweh to Joshua stretch out with the javelin which [is] in hand your to Ai for in hand your I will give it and he stretched out Joshua with the javelin which [was] in hand his to the city.
19 Da yin haka kuwa sai mutanen da suka yi kwanto suka tashi nan da nan daga inda suke, suka nufi birnin a guje, suka shiga suka ci birnin da yaƙi, suka kuma cinna mata wuta da sauri.
And the ambush it arose quickly from place its and they ran when stretched out hand his and they went the city and they captured it and they hurried and they set on fire the city with fire.
20 Mutanen Ai suka juya suka ga hayaƙin birninsu yana tashi sama, amma ba yadda za su iya tsira ta ko’ina, gama Isra’ilawan da suke gudu zuwa cikin jeji suka juya suka fara fafarar waɗanda suke fafararsu.
And they turned [the] men of Ai behind them and they saw and there! it went up [the] smoke of the city the heavens towards and not it was in them hands to flee hither and hither and the people which was fleeing the wilderness it turned back against the pursuer.
21 Lokacin da Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka ga waɗanda suka yi kwanto sun ci birnin da yaƙi, hayaƙi kuwa ya cika birnin, sai suka juya suka kai wa mutanen Ai hari.
And Joshua and all Israel they saw that it had captured the ambush the city and that it went up [the] smoke of the city and they turned back and they attacked [the] men of Ai.
22 Mutanen da suka yi kwanto su ma suka fito daga birnin suka tasar musu, ya zama an kama su a tsakiya, ga Isra’ilawa daga kowane gefe. Isra’ilawa kuwa suka karkashe su duka ba su bar wani da rai ba, ba kuma wanda ya tsere.
And these [men] they came out from the city to meet them and they were to Israel in the middle these from this and these from this and they struck down them until not he had left to him a survivor and a fugitive.
23 Amma suka tafi da sarkin Ai da rai suka kawo shi wurin Yoshuwa.
And [the] king of Ai they captured alive and they brought near him to Joshua.
24 Da Isra’ilawa suka gama kashe duk mutanen Ai a filaye da kuma a cikin jeji inda suka fafare su, kuma da aka karkashe kowane mutumin Ai da takobi sai dukan Isra’ilawa suka koma Ai suka karkashe duk waɗanda suke cikinsa.
And it was when had finished Israel to kill all [the] inhabitants of Ai in the open country in the wilderness which they had pursued them in it and they had fallen all of them to [the] mouth of [the] sword until were finished they and they returned all Israel Ai and they attacked it to [the] mouth of [the] sword.
25 A ranan nan, dukan mutanen Ai da aka kashe, mutum dubu goma sha biyu ne maza da mata.
And it was all those [who] fell on the day that from man and unto woman two [plus] ten thousand all [the] people of Ai.
26 Gama Yoshuwa bai janye hannunsa da yake riƙe da māshinsa ba har sai da ya hallaka dukan mazaunan Ai.
And Joshua not he drew back hand his which he had stretched out with the javelin until that he had totally destroyed all [the] inhabitants of Ai.
27 Amma Isra’ilawa suka kwashe ganima da dabbobin birnin nan yadda Ubangiji ya umarci Yoshuwa.
Only the livestock and [the] booty of the city that they plundered for themselves Israel according to [the] word of Yahweh which he had commanded Joshua.
28 Yoshuwa kuwa ya ƙone Ai, ya mai da ita tarin ƙasa, ta zama kufai har wa yau.
And he burned Joshua Ai and he made it a mound of perpetuity a desolation until the day this.
29 Ya rataye sarkin Ai a kan itace, ya bar shi a can har yamma. Da rana ta fāɗi, Yoshuwa ya umarta a ɗauke gawar sarkin a jefa a gaban ƙofar birnin. Suka kuma tara manyan duwatsu a kan gawar, tsibin na nan har wa yau.
And [the] king of Ai he hanged on the tree until [the] time of the evening and just as went the sun he commanded Joshua and they took down corpse his from the tree and they threw it to [the] entrance of [the] gate of the city and they set up over him a heap of stones great until the day this.
30 Yoshuwa kuwa ya yi wa Ubangiji, Allah na Isra’ila bagade a Dutsen Ebal,
Then he built Joshua an altar to Yahweh [the] God of Israel on [the] mountain of Ebal.
31 kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarci Isra’ilawa. Ya gina bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Littafin Dokoki na Musa, bagade na duwatsun da ba a sassaƙa su ba, waɗanda ba wani ƙarfen da ya taɓa su. Suka miƙa wa Ubangiji hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kai.
Just as he had commanded Moses [the] servant of Yahweh [the] people of Israel according to [what] is written in [the] book of [the] law of Moses an altar of stones complete which not anyone has wielded on them iron and they offered up on it burnt offerings to Yahweh and they sacrificed peace offerings.
32 A can, a gaban Isra’ilawa, Yoshuwa ya rubuta dokokin Musa a kan duwatsun.
And he wrote there on the stones copy of [the] law of Moses which he had written before [the] people of Israel.
33 Sai Isra’ilawa duka, da baƙi, da haifaffun gida, da dattawansu, da shugabanninsu, da alƙalansu, suka tsaya a gefe-gefen akwatin alkawarin Ubangiji, suna fuskantar waɗanda suke ɗauke da shi, wato, firistoci waɗanda su ne Lawiyawa. Rabin mutanen suka tsaya a gaban Dutsen Gerizim, rabinsu kuma suka tsaya a gaban Dutsen Ebal, kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya riga ya umarta, cewa su sa wa mutanen Isra’ilawa albarka.
And all Israel and elders its and officials - and judges its [were] standing from this - and from this - of the ark before the priests the Levites [the] bearers of - [the] ark of [the] covenant of Yahweh as the sojourner as the native half of it to [the] front of [the] mountain of Gerizim and half of it to [the] front of [the] mountain of Ebal just as he had commanded Moses [the] servant of Yahweh to bless the people Israel at the former [time].
34 Bayan haka, Yoshuwa ya karanta duk abin da yake a cikin Dokoki, albarku da la’anoni, kamar yadda suke a rubuce a cikin Littafin Dokoki.
And after thus he read aloud all [the] words of the law the blessing and the curse according to every [thing] written in [the] book of the law.
35 Babu wata kalmar da Musa ya umarta da Yoshuwa bai karanta wa dukan taron Isra’ilawa ba, haɗe da mata, da yara, da baƙin da suke zama tare da su.
Not it was anything from all that he had commanded Moses which not he read aloud Joshua before all [the] assembly of Israel and the women and the little one[s] and the sojourner[s] who went in midst their.

< Yoshuwa 8 >