< Yoshuwa 8 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Kada ka ji tsoro; kada ka karaya. Ka ɗauki dukan sojojin ku kai wa Ai hari, gama na ba ka nasara a kan sarkin Ai, mutanensa, birninsa da kuma ƙasarsa.
I řekl Hospodin k Jozue: Neboj se, ani se strachuj; pojmi s sebou všecken lid bojovný, a vstana, táhni k Hai. Aj, dal jsem v ruku tvou krále Hai a lid jeho, město i zemi jeho.
2 Za ku yi wa Ai yadda kuka yi wa Yeriko da sarkinta, sai dai za ku kwashe ganima da dabbobinta su zama naku. Ku yi kwanto a bayan birnin.”
A učiníš Hai a králi jeho, jako jsi učinil Jerichu a králi jeho, loupež však a dobytky jeho rozbitujete mezi sebe. Zdělejž sobě zálohy k městu po zadu.
3 Yoshuwa da dukan sojojin suka fita su kai wa Ai hari. Sai ya zaɓi sojojinsa waɗanda suka fi saura duka iya yaƙi guda dubu talatin, ya tura su da dad dare
Tedy vstal Jozue a všecken lid bojovný, aby táhli k Hai. I vybral Jozue třidcet tisíců mužů velmi silných, a předeslal je v noci.
4 ya ba su umarni ya ce, “Ku ji da kyau, za ku yi kwanto a bayan birnin, kada ku yi nisa da birnin. Kowannenku yă kasance a faɗake.
A přikázal jim, řka: Šetřtež vy, kteříž uděláte zálohy městu po zadní straně města, abyste nebyli příliš daleko od něho, ale buďte všickni pohotově.
5 Ni da waɗanda suke tare da ni za mu nufi birnin, a lokacin da mutanen suka taso mana yadda suka yi dā, sai mu guje musu.
Já pak i všecken lid, kterýž se mnou jest, přitáhneme k městu. A když oni nám vyjdou vstříc, jako prvé, utíkati budeme před nimi.
6 Za su bi mu har su yi nisa da birnin, gama za su ce, ‘Suna gudu kamar yadda suka yi dā.’ Saboda haka lokacin da muka guje musu,
Tedy honiti budou nás, až bychom poodvedli jich od města, (nebo řeknou: Utíkají před námi, jako prvé), utíkajíce před nimi.
7 sai ku tashi daga inda kuka yi kwanto, ku ci birnin da yaƙi, Ubangiji Allahnku zai ba da shi a hannunku.
Vy mezi tím vyskočíte z záloh, a vyženete ostatní obyvatele města, nebo dá je Hospodin Bůh váš v ruku vaši.
8 Lokacin da kuka ƙwace birnin, sai ku sa masa wuta. Ku yi abin da Ubangiji ya umarta. Ku tabbata kun yi abubuwan da na ce.”
A když vezmete město, zapálíte je ohněm, podlé slova Hospodinova učiníte; šetřtež toho, což jsem přikázal vám.
9 Sai Yoshuwa ya sallame su, suka kuma tafi wurin da za su yi kwanto, suka kwanta suna fako tsakanin Betel da Ai, yamma da Ai, amma Yoshuwa ya kwana tare da mutanen.
I poslal Jozue, a oni šli k zálohám, a zůstali mezi Bethel a Hai, od západní strany Hai; Jozue pak zůstal té noci u prostřed lidu.
10 Kashegari da sassafe Yoshuwa ya tattara mutanensa, sai shi da shugabannin Isra’ilawa suka sha gaba suka taka zuwa Ai.
Potom vstav Jozue velmi ráno, sečtl lid, i bral se napřed, on a starší Izraelští před lidem k Hai.
11 Dukan sojojin da suke tare da shi suka nufi birnin, da suka kai kuwa sai suka kafa sansaninsu a arewancin Ai. Tsakaninsu da Ai akwai kwari.
Všecken také lid bojovný, kterýž byl s ním, táhnouce, přiblížili se, až přišli naproti městu, a položili se po straně půlnoční Hai; údolí pak bylo mezi nimi a mezi Hai.
12 Yoshuwa ya sa mutum dubu biyar suka yi kwanto tsakanin Betel da Ai, a yammancin birnin.
Vzal pak byl okolo pěti tisíc mužů, kteréž postavil v zálohách mezi Bethel a Hai, od západní strany města.
13 Mutanen suka kafa sansaninsu arewa da birnin, sansani na’yan kwanto kuwa yana yamma da birnin, amma Yoshuwa ya kwana a kwarin.
I přiblížil se lid, totiž všecko vojsko, kteréž bylo od půlnoční strany města, a kteříž byli v zálohách jeho od západní strany města; a tak vtáhl Jozue noci té do prostřed údolí.
14 Sa’ad da sarkin Ai ya ga haka, shi da duk mutanen birnin suka hanzarta da sassafe don su gamu da Isra’ilawa, su yi yaƙi da su a wani wurin da yake fuskantar Araba. Amma bai san cewa an yi masa kwanto a bayan birnin ba.
I stalo se, že když je uzřel král Hai, pospíšili, a ráno vstavše, vyšli lidé města vstříc Izraelovi k boji, on i všecken lid jeho toho času před rovinu; nevěděl pak, že zálohy udělány byly jemu po zadu města.
15 Yoshuwa da duk Isra’ilawa suka bari aka fafare su, sai suka gudu zuwa cikin jeji.
I postoupil Jozue a všecken Izrael před nimi, a utíkali cestou pouště.
16 Aka kira duk mazan Ai su fafare su, suka kuwa fafari Yoshuwa, aka yaudare su suka yi nisa da birnin.
I svolán jest všecken lid v městě, aby je honili. I honili Jozue, a vzdálili se od města svého,
17 Ba namijin da ya rage a Ai ko Betel da bai fita don yă fafari Isra’ilawa ba. Suka bar birnin a buɗe, suka tafi fafarar Isra’ilawa.
Tak že nezůstal žádný z obyvatelů Hai a Bethel, kdo by nevyšel, aby honil Izraele; a nechali města otevřeného, a honili Izraele.
18 Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka riƙe māshin da yake hannunka ka nuna wajen Ai, gama zan ba da birnin a hannunka.” Yoshuwa kuwa ya miƙa māshin ta wajen Ai.
Řekl pak Hospodin k Jozue: Zdvihni korouhev, kterouž máš v rukou svých, proti Hai, nebo v ruce tvé dám je. I zdvihl Jozue korouhev, kterouž měl v ruce své, proti městu.
19 Da yin haka kuwa sai mutanen da suka yi kwanto suka tashi nan da nan daga inda suke, suka nufi birnin a guje, suka shiga suka ci birnin da yaƙi, suka kuma cinna mata wuta da sauri.
Tedy, kteříž byli v zálohách, rychle vyskočili z místa svého, a běželi, když pozdvihl ruky své, a všedše do města, vzali je, a spěšně zapálili město ohněm.
20 Mutanen Ai suka juya suka ga hayaƙin birninsu yana tashi sama, amma ba yadda za su iya tsira ta ko’ina, gama Isra’ilawan da suke gudu zuwa cikin jeji suka juya suka fara fafarar waɗanda suke fafararsu.
Muži pak města Hai ohlédše se nazpět, uzřeli, a aj, vstupoval dým města k nebi, a neměli místa k utíkání sem ani tam; nebo lid, kterýž utíkati počal k poušti, obrátil se na ty, kteříž je honili.
21 Lokacin da Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka ga waɗanda suka yi kwanto sun ci birnin da yaƙi, hayaƙi kuwa ya cika birnin, sai suka juya suka kai wa mutanen Ai hari.
Jozue zajisté a všecken Izrael, když viděli, že z záloh vzali město, a že se vznáší dým města, obrátili se, a bili muže Hai.
22 Mutanen da suka yi kwanto su ma suka fito daga birnin suka tasar musu, ya zama an kama su a tsakiya, ga Isra’ilawa daga kowane gefe. Isra’ilawa kuwa suka karkashe su duka ba su bar wani da rai ba, ba kuma wanda ya tsere.
Onino také vyšli z města proti nim, a obklíčil Izrael nepřátely své, jedni odsud, druzí od onud; a zmordovali je, tak že žádný živ nezůstal ani neušel.
23 Amma suka tafi da sarkin Ai da rai suka kawo shi wurin Yoshuwa.
Ale krále Hai jali živého, a přivedli ho k Jozue.
24 Da Isra’ilawa suka gama kashe duk mutanen Ai a filaye da kuma a cikin jeji inda suka fafare su, kuma da aka karkashe kowane mutumin Ai da takobi sai dukan Isra’ilawa suka koma Ai suka karkashe duk waɗanda suke cikinsa.
Když pak pomordoval Izrael všecky obyvatele Hai v poli, totiž na poušti, kamž je honili, a padli ti všickni od ostrosti meče, až i zahlazeni jsou: navrátil se všecken Izrael do Hai, a zmordovali ostatky jeho mečem.
25 A ranan nan, dukan mutanen Ai da aka kashe, mutum dubu goma sha biyu ne maza da mata.
A bylo všech, kteříž padli v ten den, od muže až do ženy, dvanácte tisíců; všickni ti byli z Hai.
26 Gama Yoshuwa bai janye hannunsa da yake riƙe da māshinsa ba har sai da ya hallaka dukan mazaunan Ai.
Ale Jozue nespustil ruky své, kterouž vyzdvihl korouhev, dokudž nebyli zmordováni všickni obyvatelé Hai.
27 Amma Isra’ilawa suka kwashe ganima da dabbobin birnin nan yadda Ubangiji ya umarci Yoshuwa.
Toliko hovada a loupež města toho rozbitovali mezi sebou synové Izraelští podlé slova Hospodinova, kteréž on přikázal Jozue.
28 Yoshuwa kuwa ya ƙone Ai, ya mai da ita tarin ƙasa, ta zama kufai har wa yau.
Tedy vypálil Jozue Hai, a položil je v hromadu věčnou a pustinu, až do tohoto dne.
29 Ya rataye sarkin Ai a kan itace, ya bar shi a can har yamma. Da rana ta fāɗi, Yoshuwa ya umarta a ɗauke gawar sarkin a jefa a gaban ƙofar birnin. Suka kuma tara manyan duwatsu a kan gawar, tsibin na nan har wa yau.
Krále pak Hai oběsil na dřevě, a nechal ho tam až do večera. A když zapadlo slunce, rozkázal Jozue, aby složili tělo jeho s dřeva, a povrhli je u brány města, a nametali na ně hromadu kamení velikou, kteráž trvá až do dnešního dne.
30 Yoshuwa kuwa ya yi wa Ubangiji, Allah na Isra’ila bagade a Dutsen Ebal,
Tedy vzdělal Jozue oltář Hospodinu Bohu Izraelskému na hoře Hébal,
31 kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarci Isra’ilawa. Ya gina bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Littafin Dokoki na Musa, bagade na duwatsun da ba a sassaƙa su ba, waɗanda ba wani ƙarfen da ya taɓa su. Suka miƙa wa Ubangiji hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kai.
(Jakož přikázal Mojžíš, služebník Hospodinův, synům Izraelským, jakož psáno jest v knize zákona Mojžíšova, ) oltář z kamení celého, nad nímž nebylo zdviženo železo, a obětovali na něm oběti zápalné Hospodinu, obětovali i oběti pokojné.
32 A can, a gaban Isra’ilawa, Yoshuwa ya rubuta dokokin Musa a kan duwatsun.
Napsal také tam na kameních výpis zákona Mojžíšova, kterýž psal před syny Izraelskými.
33 Sai Isra’ilawa duka, da baƙi, da haifaffun gida, da dattawansu, da shugabanninsu, da alƙalansu, suka tsaya a gefe-gefen akwatin alkawarin Ubangiji, suna fuskantar waɗanda suke ɗauke da shi, wato, firistoci waɗanda su ne Lawiyawa. Rabin mutanen suka tsaya a gaban Dutsen Gerizim, rabinsu kuma suka tsaya a gaban Dutsen Ebal, kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya riga ya umarta, cewa su sa wa mutanen Isra’ilawa albarka.
Všecken pak Izrael a starší jeho, i správcové i soudcové jeho stáli po obou stranách truhly před kněžími Levítskými, kteříž nosili truhlu smlouvy Hospodinovy, tak cizí jako doma zrozený, polovice jich proti hoře Garizim, a polovice proti hoře Hébal, jakož byl prvé přikázal Mojžíš, služebník Hospodinův, aby dobrořečil lidu Izraelskému nejprvé.
34 Bayan haka, Yoshuwa ya karanta duk abin da yake a cikin Dokoki, albarku da la’anoni, kamar yadda suke a rubuce a cikin Littafin Dokoki.
A potom četl všecka slova zákona, požehnání i zlořečení, tak jakž psáno jest v knize zákona.
35 Babu wata kalmar da Musa ya umarta da Yoshuwa bai karanta wa dukan taron Isra’ilawa ba, haɗe da mata, da yara, da baƙin da suke zama tare da su.
Nebylo ani slova ze všeho, což přikázal Mojžíš, jehož by nečetl Jozue přede vším shromážděním Izraelským, i ženami i dětmi i příchozími, kteříž šli u prostřed nich.

< Yoshuwa 8 >