< Yoshuwa 7 >
1 Amma Isra’ilawa ba su yi aminci game da kayan da aka hallaka ba; Akan ɗan Karmi, ɗan Zabdi, ɗan Zera, na kabilan Yahuda ya kwashi waɗansu abubuwa, saboda haka fushin Ubangiji ya sauka a kan Isra’ilawa.
Ali se ogriješiše sinovi Izrailjevi o prokletinju, jer Ahan sin Harmije sina Zavdije sina Zarina od plemena Judina uze od prokletijeh stvari; zato se razgnjevi Gospod na sinove Izrailjeve.
2 Sai Yoshuwa ya aika mutane daga Yeriko zuwa Ai kusa da Bet-Awen gabas da Betel, ya ce musu, “Ku je ku leƙo ku ga yadda yankin yake.” Sai mutanen suka je suka leƙo asirin ƙasar Ai.
A Isus posla ljude iz Jerihona u Gaj, koji bijaše blizu Vet-Avena s istoka Vetilju, i reèe im govoreæi: idite i uhodite zemlju. I ljudi otidoše i uhodiše Gaj.
3 Da suka dawo wurin Yoshuwa suka ce, “Ba lalle dukan jama’a su je yaƙi da Ai ba, ka aika mutum dubu biyu ko dubu uku su je su ciwo ƙasar da yaƙi, ba sai ka dami mutane duka ba, gama mutanen wurin kaɗan ne.”
I vrativši se k Isusu rekoše mu: neka ne ide sav narod; do dvije tisuæe ljudi ili do tri tisuæe ljudi neka idu, i osvojiæe Gaj; nemoj truditi svega naroda, jer ih je malo.
4 Saboda haka sai kimanin mutum duba uku suka haura; amma mutanen Ai suka fatattake su,
I otide ih onamo iz naroda oko tri tisuæe ljudi; ali pobjegoše od Gajana.
5 suka kashe Isra’ilawa wajen mutum talatin da shida, suka fafari Isra’ilawa tun daga bakin ƙofar birnin har zuwa wurin da ake fasa duwatsu. Suka karkashe su a gangare. Wannan ya sa zuciyar Isra’ilawa ta narke suka zama kamar ruwa.
I Gajani posjekoše ih do trideset i šest ljudi; i goniše ih od vrata dori do Sivarima, i pobiše ih na strmeni; i rastopi se srce u narodu, i posta kao voda.
6 Sai Yoshuwa ya yaga tufafinsa ya fāɗi rubda ciki a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, yana can har yamma. Dattawan Isra’ila ma suka yi haka, suka zuba toka a kawunansu.
A Isus razdrije haljine svoje i pade licem na zemlju pred kovèegom Gospodnjim, i leža do veèera, on i starješine Izrailjeve, i posuše se prahom po glavi.
7 Yoshuwa kuma ya ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, me ya sa ka sa mutanen nan suka ƙetare Urdun don ka bari mu shiga hannun Amoriyawa su hallaka mu? Kila da mun haƙura mun zauna a ɗaya gefen Urdun da ya fi mana!
I reèe Isus: jaoh! Gospode Bože, zašto prevede ovaj narod preko Jordana da nas predaš u ruke Amorejcima da nas pobiju? o, da šæasmo ostati preko Jordana!
8 Ya Ubangiji me zan ce, yanzu da abokan gāban Isra’ilawa suka ci ƙarfinsu?
Jaoh! Gospode, šta da kažem, kad je Izrailj obratio pleæi pred neprijateljima svojim?
9 Yanzu Kan’aniyawa da sauran jama’a za su ji, za su zo su kewaye mu su share sunanmu daga duniya. To, yanzu me za ka yi don girman sunanka?”
Èuæe Hananeji i svi stanovnici te zemlje, i sleæi æe se oko nas, i istrijebiæe ime naše sa zemlje; i šta æeš uèiniti od velikoga imena svojega?
10 Ubangiji ya ce wa Yoshuwa, “Ka tashi! Me kake yi kwance rubda ciki?
A Gospod reèe Isusu: ustani; što si pao na lice svoje?
11 Isra’ilawa sun yi zunubi, sun karya sharaɗin da na yi musu. Sun ɗauki waɗansu abubuwan da aka keɓe; sun yi sata, sun yi ƙarya, sun ɓoye su cikin kayansu.
Zgriješio je Izrailj, i prestupio zavjet moj koji sam im zapovjedio: jer uzeše od prokletijeh stvari, i ukradoše, i zatajiše, i metnuše meðu svoje stvari.
12 Shi ne ya sa Isra’ilawa suka kāsa yin tsayayya da abokan gābansu; suka juya suka gudu domin za a hallaka su. Ba zan sāke kasancewa tare da ku ba sai in kun hallaka duk abin da aka keɓe don hallaka.
Zato neæe moæi sinovi Izrailjevi stajati pred neprijateljima svojim; pleæi æe obraæati pred neprijateljima svojim, jer su pod prokletstvom; neæu više biti s vama, ako ne istrijebite izmeðu sebe prokletinje.
13 “Tashi, ka je ka tsarkake mutane. Ka ce musu su tsarkake kansu, su yi shiri domin gobe; gama ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, a cikinku akwai abubuwan da aka keɓe, ya Isra’ilawa. Ba za ku iya yin tsayayya da abokan gābanku ba sai in kun rabu da abubuwan nan da aka haramta.
Ustani, osveštaj narod, i reci: osveštajte se za sjutra; jer ovako veli Gospod Bog Izrailjev: prokletstvo je usred tebe, Izrailju; neæeš moæi stajati pred neprijateljima svojim dokle ne uklonite prokletstva izmeðu sebe.
14 “‘Da safe ku zo kabila-kabila. Kabilar da Ubangiji ya ware, za tă zo gaba gida-gida; gidan da Ubangiji ya ware, za su zo gaba iyali-iyali. Iyalin kuma da Ubangiji ya ware, za su zo gaba mutum bayan mutum.
Pristupiæete ujutru po plemenima svojim; i koje pleme oblièi Gospod ono æe pristupiti po porodicama svojim, i koju porodicu oblièi Gospod ona æe pristupiti po domovima svojim; i koji dom oblièi Gospod, pristupiæe ljudi iz njega jedan po jedan.
15 Mutumin da aka same shi da haramtattun abubuwan kuwa za a ƙone shi, duk da mallakarsa domin ya karya sharaɗin da Ubangiji ya yi muku, ya yi abin kunya a Isra’ila!’”
Pa ko se naðe u prokletstvu, neka se spali ognjem i on i sve njegovo, jer prestupi zavjet Gospodnji i uèini bezakonje u Izrailju.
16 Kashegari da sassafe Yoshuwa ya sa Isra’ilawa suka fito kabila-kabila, aka ware kabilar Yahuda.
I ustavši Isus ujutru rano reèe te pristupi Izrailj po plemenima svojim; i oblièi se pleme Judino.
17 Gidan Yahuda suka zo gaba, sai aka ware gidan Zera, aka sa suka fito iyali-iyali, sai aka ware Zabdi.
Potom reèe te pristupiše porodice Judine; i oblièi se porodica Zarina; potom reèe te pristupi porodica Zarina, domaæin jedan po jedan, i oblièi se Zavdija.
18 Yoshuwa kuwa ya sa iyalin Zabdi suka fito mutum-mutum, sai kuwa aka ware Akan ɗan Karmi, ɗan Zimri, ɗan Zera na kabilar Yahuda.
I reèe, te pristupi njegov dom, ljudi jedan po jedan, i oblièi se Ahan sin Harmije sina Zavdije sina Zarina od plemena Judina.
19 Sai Yoshuwa ya ce wa Akan, “Ɗana, sai ka ba Ubangiji, Allah na Isra’ila ɗaukaka, ka yi masa yabo. Ka gaya mini abin da ka yi; kada ka ɓoye mini.”
I reèe Isus Ahanu: sine, hajde daj hvalu Gospodu Bogu Izrailjevu, i priznaj pred njim, i kaži mi šta si uèinio, nemoj tajiti od mene.
20 Akan kuwa ya amsa ya ce, “Gaskiya ne! Na yi wa Ubangiji, Allah na Isra’ila zunubi. Ga abin da na yi.
A Ahan odgovori Isusu i reèe: istina je, ja zgriješih Gospodu Bogu Izrailjevu, i uèinih tako i tako:
21 A cikin ganimar, na ga doguwar riga mai kyau irin ta Babilon, da shekel ɗari biyu na azurfa, da kuma sandan zinariya mai nauyin shekel hamsin, sai raina ya so su, na kuwa kwashe su. Na tona rami a cikin ƙasa a tentina; na ɓoye.”
Vidjeh u plijenu jedan lijep plašt Vavilonski, i dvjesta sikala srebra, i jednu šipku zlata od pedeset sikala, pa se polakomih i uzeh; i eno je zakopano u zemlju usred mojega šatora, i srebro ozdo.
22 Sai Yoshuwa ya aiki’yan aika suka tafi da gudu zuwa tenti ɗin, haka kuwa suka same su a ɓoye a tentinsa, da azurfa a ƙarƙashi.
Tada Isus posla poslanike, koji otrèaše u šator, i gle, bješe zakopano u šatoru njegovu, i ozdo srebro.
23 Suka kwashe kayan daga tenti ɗin suka kawo wa Yoshuwa da sauran Isra’ilawa, suka baza su a gaban Ubangiji.
I uzeše iz šatora i donesoše k Isusu i svijem sinovima Izrailjevijem, i metnuše pred Gospoda.
24 Sai Yoshuwa da dukan Isra’ilawa suka ɗauki Akan ɗan Zera, da azurfar, doguwar rigar, sandan zinariya,’ya’yansa maza da mata, shanunsa, jakuna da tumaki, tentinsa da duk abin da yake da shi, suka kai su Kwarin Akor.
Tada Isus i s njim sav Izrailj uzeše Ahana sina Zarina, i srebro i plašt i šipku zlata, i sinove njegove i kæeri njegove, i volove njegove i magarce njegove, i ovce njegove, i šator i sve što bješe njegovo, i izvedoše u dolinu Ahor.
25 Yoshuwa ya ce, “Me ya sa ka jawo mana wahala haka? Ubangiji zai kawo maka wahala kai ma a yau.” Sai dukan Isra’ilawa suka jajjefe shi, bayan da suka gama jifarsa sai suka ƙone sauran.
I reèe Isus: što si nas smeo? Gospod da te smete danas! I zasu ga kamenjem sav Izrailj, i spališe sve ognjem zasuvši kamenjem.
26 Suka tara manyan duwatsu a kan Akan, tarin duwatsun na nan a can har wa yau. Sa’an nan Ubangiji ya huce daga fushinsa mai zafi. Saboda haka ake kiran wurin Kwarin Akor.
Potom nabacaše na nj veliku gomilu kamenja, koja stoji i danas. I Gospod se povrati od žestine gnjeva svojega. Otuda se prozva ono mjesto dolina Ahor do danas.